Sashe 50
Ƙaramar Bazawara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da yammacin ranan dady ya tattari kan iyalanshi gaba ɗaya suka tafi asibiti duba jikin inna harda wa'inda basu so zuwa ba because he consider me as part of his family, saida suka je ne yayi nadaman zuwa da Nana don Sulthana ta fita wayo ita ta kama kanta kaɗan, haka ta zauna ta dinga yaɓa ma iyayena magana a fakaice abin saida ya kusan zama faɗa tsakanin mu domin kalaman da take jifan su dashi yayi tsauri,
Dukda nasha rarrashi a wurin su aunty da su hajiya amman saida nayi kukan takaici bayan sun tafi, nidai Allah yamin katangar ƙarfe tsakanina da yarinyar nan banma san yaya zamu ƙare ba idan na shiga gidansu a matsayin matar Zayyad,
******
Ba zato ba tsammani ya jawota baya ya dungurata a tsakiyar ɗaki sannan ya rufe ƙofar ɗakin, yaushe ya shigo ciki bata sani ba? Tunaninta ne ya katse lokacin da sulaiman ya ɗaga bulala ya shargwaɗa mata a gadon baya ta wani boƙare tare da saka ihu, da gudu ta miƙe ta nufi ƙofa amman a rufe ya garƙame da key,
Ihu nana take kaman wanda ake zare ma rai tana buga ƙofar ɗakin wanda yasa mutane fitowa don ganin abinda ke faruwa, taku ɗaya sulaiman yayi ya sake jawota ya shauɗa mata wani a kan cinya,
bata san laifin me tayi mishi ba, ita dai tasan bayi duka amman bata san me ta masa yake son kasheta a halin yanzu ba,
Taƙarƙarewa yayi ya sake zuba mata wani a take numfashinta ya tsaya cakk sautin kukanta ya daina tashi sai gurnani,
Shi da yayi dukan ma sai haki yake yi ya gwada ta da bulalan hannun shi yana jifanta da mugun kallo yace,
"Na daɗe ina taraki Nana Hafsah yanzu kin fara ƙure ni, wallahi kinji na rantse miki indai ba zaki nutsu kiyi hankali ba zaki sha baƙar wahala a hannu na shashasha mai banzan ɗabi'a, ziciyar ki baƙiƙƙirin kamar fuskar ki shiyasa har yanzu kika rasa mashinshini baki nufin kowa da alkhairi, Allah idan baki gyara ba haɗuwar mu na gaba ba zata kai wannan kyau ba"
Ita dai ta saurare shi sama_sama amman bata iya fassara kalamansa ga numfashinta dake barazanar barin jikinta tana kuka mai haɗe da gurnani, sai yanzu ya kula buga ƙofar da hajiya takeyi tana kiran sunan sa, hankalin sa kwance ya ƙarasa ya buɗe ƙofar ya fita,
"Me yake damunka ne sulaiman wannan wani irin zalunci ne?"
Kallon yanda su Ruma sukayi kanta suna kuka yayi yaja tsaki saikace wanda ya kasheta, Junior kuwa abin yayi mishi sugar don a gaban idanunshi taci mutuncin iyayen girlfriend É—inshi,
"Hajiya she is just putting a drama ni babu abinda nayi mata bayan barazana, razana ta kaɗan kawai nayi" daga faɗan haka yayi gaba ya bar hajiya da baki sake cike da al'ajabi da kunnuwanta taji sauƙan bulalu amman yace mata wai _barazana_
Bayan ya koma gida bai samu nutsuwa ba saida ya kirani a waya ya ƙara bani hakuri gashi sadiya ta shiga partial yaji don ta zama kaman babu itane cikin gidan harta yaranta ta daina kula su ta daina musu komai wai tana so sulaiman ya gano amfaninta ne yasan tana da muhimmanci a rayuwan dukkan su shi kuma hakan dq takeyi yana kara saka mishi matsuwa na ganin ya auro Saudat tazo ta ɗauki ragamar gidan baki ɗaya sai yaga ta allon ta,
Munsha hira na kusan rabin hour dukda taɗinmun ya ta'allaƙa ne akan shirin tafiyan mu wuroɓokki amman hakan ya sama mishi nutsuwa sosai, while a nawa fannin i can tell that sulaiman is becoming soft...so tender indeed da har yasa tsoro da kuma fargaban shi da nakeji a raina ya ragu sosai,
8 days later
7:30am
Annashuwa, nutsuwa, farinciki, ga kuma iska mai daÉ—i dake kaÉ—awa a hankali cikin albakataccen daji mai kawace da bishiyoyi daban_daban da tsuntsaye masu shawagi suna daÉ—aÉ—a kunnuwan bil adama da sautin muryoyin su masu daÉ—i,
Zaune nake a passenger seat na rungume kanwata indo a ƙirjina idanu na a lumshe babban yaya zaune a gefe na hankalin shi a kan titi yana driving, mahaifiyata da mahaifina kuma suna back seat, ya aminu, jaɗe, khamis, da zayyad suna motar dake gabanmu da motar police suma guda daya a gaban su motar bayanmu kuma ya Nafi'u ne ke driving da matan jaɗe da na ya aminu sai kuma ƴaƴansu, suma da na police guda ɗaya a bayan su making 5 cars in total,
Na daɗe ina burin irin wannan dawowar, na daɗe ina mafarkin ɗaukar fansa gashi tun kafin muzo babban yaya ya bani wuƙa da nama ni kuma nayi alƙawarin ba zan bar wuroɓokki ba sai na tabbar an kama mai gari wanda ya kasace ƙanin tsohon mijina yarima tacaccen ɗan shaye_shaye aje ayi ta gana mishi azaba a rehabilitation center shima mahaifinshi yaji yanda uba yake ji idan an raba shi da jininshi, kaiii harda ƴan uwan shi da abokan shi dan saka a kama don na rama sharrin da furere tayi wa ya aminu saboda su,
A hankali motocin suka tsaya bakunan mu suna godiya ma Allah sannan baba ya fito, da mamakinsa babu gidanmu a wurin.....tabbas nan ne inda yake amman babu shi a wurin sai wani....wani mai ginin zamani wanda ƙauyen karankaf babu kamarsa,
Juyowa malam ardo yayi kaman zaiyi kuka abin nasu ya fara kaishi bango, koda ace fili ba nashi bane amman ai gida nasi ne shi ya gina da guminsa bai kamata a rushe ba tare da izinin shi ba,
"Mu shiga ciki mana baba! Mai muke jira?" Sulaiman ya tambaya,
A raunane ya juyo yana kallon mu murya can ƙasa yace
"Bamu da wurin da zamu shiga, sun riga sun fitar dani daga garin bani da matsuguni a cikinta a halin yanzu"
"Kaman yaya baka da matsuguni bayan ga gidanka nan? Duk duniya akwai wanda ya isa ya fitar da kai daga cikinta ne bayan ikon Allah?"
Da mamaki malam arɗo ya tsaya yana kallon Sulaiman kanshi ya kasa fassara mishi abinda yake nufi, ganin mutane sun fara cika a ƙofar gidan ciki harda matan aure suna yafo mayafinsu suzo ganin kalan motoci da mutanen da akace saudat tazo dasu,
Muna zuwa shiga zayyad ya yanki jiki ya faÉ—i amman hakan bai wani dame mu ba saidai a yanzu hankalin Sulaiman ya fara tashi haka suka haÉ—u suka kinkime shi zuwa ciki,
Saida muka shiga ne akayi ma malam arɗo bayani dalla_dalla sulaiman ne ya saka aka gyara musu gidan, shidai baisan mai zaiyi ma wannan ɗan albarkan ba, yana ganin koda goyon shi yayi ba zai isa ba yayi masa alkhairori masu yawa wanda bayi da abinda zai biya shi dashi saidai yayi ta mishi addu'a, ai kuwa ya shata daga bakin kowa a gidan ni kuwa kuka nake kaman anyi mini mutuwa wani ƙima da daraja na sulaiman na daɗuwa a cikin rayina, ya gama min komai a rayuwa da ace ina da abinda zan biya shi dashi definitely zan biya shi,
Hutawa mukayi zuwa ƙarfe 10 sannan muka ɗau haraman ɗaura abinci ga komai da ake buƙata Sulaiman ya tanade shi ya jibge mana a store ɗin gidan, akace hannu da yawa maganin ....miiya cikin abinda bai wuce awanni biyu ba muka gama abincin mu kala guda biyu da wanda kowa zaici da kuma irin wanda ni da su Sulaiman muka saba dashi na yan birni har zuwa lokacin Zayyad na barci bai farka ba, daga nan nayi wanka nayi sallah aka ci abinci na ɗan zauna ƙarin hutu zuwa sallan la'asar saboda nafison sai rana tayi sanyi kafin na fita yanda zan karaɗa ko ina nayi son raina tunda a yanzu ina da goyon baya,
3:47pm
Wani motar ya ƙaraso ƙofar gidan dai_dai inda sauran motocin suke shima yayi parking, da gudu na ƙaraso na ruƙunƙume ta inajin farinciki mara misaltuwa bayan sintirin da na dinga yi a gidan su Ruma yau itama gashi tazo namu gidan kuma ina alfahari da hakan,
Tare suke da Yusrah da mahaifiyar khamis da mahaifiyar ita yusran harda Nasreen amman duk cikin su babu wanda yazo da yara dukda haka dai munyi full house,
Har zamu wuce muryan Fa'iza ya jawo attention ɗinmu, ta fito ta ɗaya ƙofar bayan tana tsaye dare da murfin motan a yatsine take binmu da kallo,
"Hey bush head!! Baku ganin mutane ne da tsiraran kafafunku kaman masilla da ba zaku kulani ba? Dukda dai ke ba laifin ki bane" ta faÉ—a tana gwada ni "kina fama da makanta ba zanga laifin ki ba idan baki gani"
_wato nana ne kawai bata zo ba! Itace kawai bata taya ni murnan dawowa na mahaifata, toh Allah ya huci zuciyarta_
Cikin farinciki muka ƙarasa muka rungumeta dukda sai ihu take wai zamu saka mata bola kasancewar fararen kaya ne a jikinta muka jasu ciki, gaisawa kaɗan aka zauna sake yi sulaiman yayi shirin tafiya zai kuma bi ya haɗa kan ƴan ƙwayan da zai kaisu rehab su tafi tare,
Unknown to us har motan police ya tattari na tafiya sun riga sun tafi su tsohon mai gari ne ake ta faman artabo dashi ya hana a ɗauki ƙanin yarima sun ɓoye shi a wani wurin da ba'a ma san ina bane,
_wannan tsoho mai ran dalma har yanzu yana raye?_🤦ðŸ»â€â™€ï¸
*Here i comes again, na zama maman excuse gashi bani iya replying comments😣 like seriously yanzu na dawo sai a hankali a ci gaba da hakuri dani a haka dan Allah ana manage😠saidai duk da haka ina bin sharhin ku ɗaya bayan ɗaya ina karantawa kuma yana sani farinciki matuƙa na gode na gode💃🥰*
*Ummu excuse ce😂😘*
(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)
ðŸ¤ðŸ’šðŸ¤
  *ƘARAMAR BAZAWARA*
      💚ðŸ¤ðŸ’š
  _(Cigaban matar kulle)_
тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsÑ‚ ιмÏσÑтαηт qυαℓιтү α ωÑÎ¹Ñ‚ÎµÑ cαη нαvε, ωε *_ÏÑσғιcιεηт ωÑιтεÑ's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαÑε тнεsε qυαℓιтιεs.
WATTPAD: https://my.w.tt/4ZfEeBpVecb
OR
@ayeeshatmuhd
     *BY UMMU NAJMA*
*DEDICATED TO, MAI DAMBU*
And *AISHA ALTO*
41ðŸ§ðŸ»â€â™€ï¸Â
Bai ankara ba sai ganin hawaye yayi zirr a idanunta abin har yaso bashi mamaki dukda yasan za'a rina, gimtse dariyar shi yayi ya ɗan karkace wuya yana kallon yanda ta haɗa kai da guiwa tana matsar ƙolla yace
Dukda nasha rarrashi a wurin su aunty da su hajiya amman saida nayi kukan takaici bayan sun tafi, nidai Allah yamin katangar ƙarfe tsakanina da yarinyar nan banma san yaya zamu ƙare ba idan na shiga gidansu a matsayin matar Zayyad,
******
Ba zato ba tsammani ya jawota baya ya dungurata a tsakiyar ɗaki sannan ya rufe ƙofar ɗakin, yaushe ya shigo ciki bata sani ba? Tunaninta ne ya katse lokacin da sulaiman ya ɗaga bulala ya shargwaɗa mata a gadon baya ta wani boƙare tare da saka ihu, da gudu ta miƙe ta nufi ƙofa amman a rufe ya garƙame da key,
Ihu nana take kaman wanda ake zare ma rai tana buga ƙofar ɗakin wanda yasa mutane fitowa don ganin abinda ke faruwa, taku ɗaya sulaiman yayi ya sake jawota ya shauɗa mata wani a kan cinya,
bata san laifin me tayi mishi ba, ita dai tasan bayi duka amman bata san me ta masa yake son kasheta a halin yanzu ba,
Taƙarƙarewa yayi ya sake zuba mata wani a take numfashinta ya tsaya cakk sautin kukanta ya daina tashi sai gurnani,
Shi da yayi dukan ma sai haki yake yi ya gwada ta da bulalan hannun shi yana jifanta da mugun kallo yace,
"Na daɗe ina taraki Nana Hafsah yanzu kin fara ƙure ni, wallahi kinji na rantse miki indai ba zaki nutsu kiyi hankali ba zaki sha baƙar wahala a hannu na shashasha mai banzan ɗabi'a, ziciyar ki baƙiƙƙirin kamar fuskar ki shiyasa har yanzu kika rasa mashinshini baki nufin kowa da alkhairi, Allah idan baki gyara ba haɗuwar mu na gaba ba zata kai wannan kyau ba"
Ita dai ta saurare shi sama_sama amman bata iya fassara kalamansa ga numfashinta dake barazanar barin jikinta tana kuka mai haɗe da gurnani, sai yanzu ya kula buga ƙofar da hajiya takeyi tana kiran sunan sa, hankalin sa kwance ya ƙarasa ya buɗe ƙofar ya fita,
"Me yake damunka ne sulaiman wannan wani irin zalunci ne?"
Kallon yanda su Ruma sukayi kanta suna kuka yayi yaja tsaki saikace wanda ya kasheta, Junior kuwa abin yayi mishi sugar don a gaban idanunshi taci mutuncin iyayen girlfriend É—inshi,
"Hajiya she is just putting a drama ni babu abinda nayi mata bayan barazana, razana ta kaɗan kawai nayi" daga faɗan haka yayi gaba ya bar hajiya da baki sake cike da al'ajabi da kunnuwanta taji sauƙan bulalu amman yace mata wai _barazana_
Bayan ya koma gida bai samu nutsuwa ba saida ya kirani a waya ya ƙara bani hakuri gashi sadiya ta shiga partial yaji don ta zama kaman babu itane cikin gidan harta yaranta ta daina kula su ta daina musu komai wai tana so sulaiman ya gano amfaninta ne yasan tana da muhimmanci a rayuwan dukkan su shi kuma hakan dq takeyi yana kara saka mishi matsuwa na ganin ya auro Saudat tazo ta ɗauki ragamar gidan baki ɗaya sai yaga ta allon ta,
Munsha hira na kusan rabin hour dukda taɗinmun ya ta'allaƙa ne akan shirin tafiyan mu wuroɓokki amman hakan ya sama mishi nutsuwa sosai, while a nawa fannin i can tell that sulaiman is becoming soft...so tender indeed da har yasa tsoro da kuma fargaban shi da nakeji a raina ya ragu sosai,
8 days later
7:30am
Annashuwa, nutsuwa, farinciki, ga kuma iska mai daÉ—i dake kaÉ—awa a hankali cikin albakataccen daji mai kawace da bishiyoyi daban_daban da tsuntsaye masu shawagi suna daÉ—aÉ—a kunnuwan bil adama da sautin muryoyin su masu daÉ—i,
Zaune nake a passenger seat na rungume kanwata indo a ƙirjina idanu na a lumshe babban yaya zaune a gefe na hankalin shi a kan titi yana driving, mahaifiyata da mahaifina kuma suna back seat, ya aminu, jaɗe, khamis, da zayyad suna motar dake gabanmu da motar police suma guda daya a gaban su motar bayanmu kuma ya Nafi'u ne ke driving da matan jaɗe da na ya aminu sai kuma ƴaƴansu, suma da na police guda ɗaya a bayan su making 5 cars in total,
Na daɗe ina burin irin wannan dawowar, na daɗe ina mafarkin ɗaukar fansa gashi tun kafin muzo babban yaya ya bani wuƙa da nama ni kuma nayi alƙawarin ba zan bar wuroɓokki ba sai na tabbar an kama mai gari wanda ya kasace ƙanin tsohon mijina yarima tacaccen ɗan shaye_shaye aje ayi ta gana mishi azaba a rehabilitation center shima mahaifinshi yaji yanda uba yake ji idan an raba shi da jininshi, kaiii harda ƴan uwan shi da abokan shi dan saka a kama don na rama sharrin da furere tayi wa ya aminu saboda su,
A hankali motocin suka tsaya bakunan mu suna godiya ma Allah sannan baba ya fito, da mamakinsa babu gidanmu a wurin.....tabbas nan ne inda yake amman babu shi a wurin sai wani....wani mai ginin zamani wanda ƙauyen karankaf babu kamarsa,
Juyowa malam ardo yayi kaman zaiyi kuka abin nasu ya fara kaishi bango, koda ace fili ba nashi bane amman ai gida nasi ne shi ya gina da guminsa bai kamata a rushe ba tare da izinin shi ba,
"Mu shiga ciki mana baba! Mai muke jira?" Sulaiman ya tambaya,
A raunane ya juyo yana kallon mu murya can ƙasa yace
"Bamu da wurin da zamu shiga, sun riga sun fitar dani daga garin bani da matsuguni a cikinta a halin yanzu"
"Kaman yaya baka da matsuguni bayan ga gidanka nan? Duk duniya akwai wanda ya isa ya fitar da kai daga cikinta ne bayan ikon Allah?"
Da mamaki malam arɗo ya tsaya yana kallon Sulaiman kanshi ya kasa fassara mishi abinda yake nufi, ganin mutane sun fara cika a ƙofar gidan ciki harda matan aure suna yafo mayafinsu suzo ganin kalan motoci da mutanen da akace saudat tazo dasu,
Muna zuwa shiga zayyad ya yanki jiki ya faÉ—i amman hakan bai wani dame mu ba saidai a yanzu hankalin Sulaiman ya fara tashi haka suka haÉ—u suka kinkime shi zuwa ciki,
Saida muka shiga ne akayi ma malam arɗo bayani dalla_dalla sulaiman ne ya saka aka gyara musu gidan, shidai baisan mai zaiyi ma wannan ɗan albarkan ba, yana ganin koda goyon shi yayi ba zai isa ba yayi masa alkhairori masu yawa wanda bayi da abinda zai biya shi dashi saidai yayi ta mishi addu'a, ai kuwa ya shata daga bakin kowa a gidan ni kuwa kuka nake kaman anyi mini mutuwa wani ƙima da daraja na sulaiman na daɗuwa a cikin rayina, ya gama min komai a rayuwa da ace ina da abinda zan biya shi dashi definitely zan biya shi,
Hutawa mukayi zuwa ƙarfe 10 sannan muka ɗau haraman ɗaura abinci ga komai da ake buƙata Sulaiman ya tanade shi ya jibge mana a store ɗin gidan, akace hannu da yawa maganin ....miiya cikin abinda bai wuce awanni biyu ba muka gama abincin mu kala guda biyu da wanda kowa zaici da kuma irin wanda ni da su Sulaiman muka saba dashi na yan birni har zuwa lokacin Zayyad na barci bai farka ba, daga nan nayi wanka nayi sallah aka ci abinci na ɗan zauna ƙarin hutu zuwa sallan la'asar saboda nafison sai rana tayi sanyi kafin na fita yanda zan karaɗa ko ina nayi son raina tunda a yanzu ina da goyon baya,
3:47pm
Wani motar ya ƙaraso ƙofar gidan dai_dai inda sauran motocin suke shima yayi parking, da gudu na ƙaraso na ruƙunƙume ta inajin farinciki mara misaltuwa bayan sintirin da na dinga yi a gidan su Ruma yau itama gashi tazo namu gidan kuma ina alfahari da hakan,
Tare suke da Yusrah da mahaifiyar khamis da mahaifiyar ita yusran harda Nasreen amman duk cikin su babu wanda yazo da yara dukda haka dai munyi full house,
Har zamu wuce muryan Fa'iza ya jawo attention ɗinmu, ta fito ta ɗaya ƙofar bayan tana tsaye dare da murfin motan a yatsine take binmu da kallo,
"Hey bush head!! Baku ganin mutane ne da tsiraran kafafunku kaman masilla da ba zaku kulani ba? Dukda dai ke ba laifin ki bane" ta faÉ—a tana gwada ni "kina fama da makanta ba zanga laifin ki ba idan baki gani"
_wato nana ne kawai bata zo ba! Itace kawai bata taya ni murnan dawowa na mahaifata, toh Allah ya huci zuciyarta_
Cikin farinciki muka ƙarasa muka rungumeta dukda sai ihu take wai zamu saka mata bola kasancewar fararen kaya ne a jikinta muka jasu ciki, gaisawa kaɗan aka zauna sake yi sulaiman yayi shirin tafiya zai kuma bi ya haɗa kan ƴan ƙwayan da zai kaisu rehab su tafi tare,
Unknown to us har motan police ya tattari na tafiya sun riga sun tafi su tsohon mai gari ne ake ta faman artabo dashi ya hana a ɗauki ƙanin yarima sun ɓoye shi a wani wurin da ba'a ma san ina bane,
_wannan tsoho mai ran dalma har yanzu yana raye?_🤦ðŸ»â€â™€ï¸
*Here i comes again, na zama maman excuse gashi bani iya replying comments😣 like seriously yanzu na dawo sai a hankali a ci gaba da hakuri dani a haka dan Allah ana manage😠saidai duk da haka ina bin sharhin ku ɗaya bayan ɗaya ina karantawa kuma yana sani farinciki matuƙa na gode na gode💃🥰*
*Ummu excuse ce😂😘*
(¯'*•.¸,¤°´✿.。.:*քʀօʄɨƈɨɛռȶ աʀɨȶɛʀֆ*.:。.✿'°¤,¸.•*´¯)
ðŸ¤ðŸ’šðŸ¤
  *ƘARAMAR BAZAWARA*
      💚ðŸ¤ðŸ’š
  _(Cigaban matar kulle)_
тнε αвιℓιтү тσ gυι∂ε ιs тнε мσsÑ‚ ιмÏσÑтαηт qυαℓιтү α ωÑÎ¹Ñ‚ÎµÑ cαη нαvε, ωε *_ÏÑσғιcιεηт ωÑιтεÑ's αssσcιαтιση_* ωιℓℓ sнαÑε тнεsε qυαℓιтιεs.
WATTPAD: https://my.w.tt/4ZfEeBpVecb
OR
@ayeeshatmuhd
     *BY UMMU NAJMA*
*DEDICATED TO, MAI DAMBU*
And *AISHA ALTO*
41ðŸ§ðŸ»â€â™€ï¸Â
Bai ankara ba sai ganin hawaye yayi zirr a idanunta abin har yaso bashi mamaki dukda yasan za'a rina, gimtse dariyar shi yayi ya ɗan karkace wuya yana kallon yanda ta haɗa kai da guiwa tana matsar ƙolla yace