← Book details Kaine Sirrina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 43

Sashe 9

Kaine Sirrina Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

19
Gidan wata mata dake saida magani a kauyen taje,saidai matar batanan sai yayan ta yan mata guda uku da bazasu wuce sa’ointa ba.
Sallama tayi suka amsa suna mata kallon banza tace “abani maganin ciwon kai da zazzabi” tashi daya daga cikinsu tayi ta dauko mata wani kullin maganin gari guda biyu. Rufaida ta karba ta mika naira hamsin, yarinyar tana karba tace”jar ubanchan,lallai nema yarnan, dan kin rainamin hankali antaba saida maganin zazzabi da bauri naira hamsin?ko angaya miki na gadon ubankine?” Rufaida girgiza kai tace “wlh hamsin gareni,dan Allah kiyakuri wlh Mara lafiya zanba “sauran yayyin yarinyar biyu suka taso sukace “maiya faru lami”yarinyar tace “ba wanan jikar Duduwan bace wai magani naira dari taban hamsin” da sauri Rufaida tace “dan Allah kubini bashi wlh Mara lpy zanba” takarasa maganan da muryan tausayi, Babban yarsu tace “zaki kawo cikon kudin gobe, inba hakaba wlh saimun tareki abakin rafi mun miki dukan tsiya,mu daki kudinmu”. Rufaida tace “na yarda, tajuya tabar gidan da gudu tabiya shago tasai buredin ishirin sai madara cow bell ta goma da choco na goma sai sigan goma.

Ta shiga gidan hartana tuntube saboda sauri,har alokacin Duduwa bata dawoba,kofi ta dauka ta jika mishi garin maganin,sanan tadau wani kofi ta kada mishi tea da ruwan sanyi duk takai dakin sanan ta tasheshi, “ga magani kasha”, da kyar ya zauna ya jingina da bango daukan kofin maganin tayi takai bakinshi tace “bude bakinka” bude bakinshi yayi ta zubamai maganin, feso maganin yayi a fuskatta batare daya saniba ya yamuse fuska saboda wani azaban daci d bauri dayaji, ta share fuskan ta batare data damuba tace” kasha dan Allah” girgiza mata kai yayi. Tace” ga tea kasha” shima girgiza mata kai yayi ta tashi daga wurin takoma gefe tana kallon yanda yake mutsu mutsu. Kara dawowa kusa dashi tayi tarike mai hannu tafashe da kuka sosai, dudda cikin ciwo yake amma saiyaji kukan kaman na kurman yarinyar nan dayahadu da ita a Minna. Tace”Dan Allah ktashi kasha,kanka naciwo,wlh bazan iya inta kallonka kana ciwo ba kaji,kanada kirki Allah” wani iri yaji datana kuka ahankali yace “ban nasha”daukan magananin tayi tabashi da kyar yasha rabin kofi yana tabe baki sanan yakoma ya kwanta zama tayi a gefenshi tasa hannu tacire mai takalmin kafanshi sanan tadau mahici tana fifitashi ganin yana zufa.

Gafaradai mutan gida. Sallaman Duduwa yasa Rufaida tayar da maficin ta mike tsaye ta rike kirji Duduwa tadawo,arude tasa bakinta a kunnenshi tace “kakata tadawo dan Allah karkai magana taji kaji?” Tsigar jikinshi yatashi yarr, tashi tayi tafita daga bukkan ta rufo kofan ta tsaya a wurin tana kallon Duduwa dake kallon ta, “ina ruwan danace ki debo?” Rufaida takara makewa ajikin bango tana makyarkyata “Duduwa wlh tulun yafashe ahanya, ba laifina bane Allah bom… Duduwa ta daka mata tsawa ” ke! yimin shiru shegiya mai kama da ifiritu, wlh tunda kika fasamin tulu wlh saina fanshi abuna ajikin ki zaki gamu Dani,laifin ki biyu baki debo ruwa ba ga fasa Randa, bazaki zo nanba ina magana dake kina kallona da bakaken idonki” Rufaida tunkafin takai tafara matsar kwalla,Takai gaban Duduwa ta tsugunna “gani”, katuwar buhun danyar gyadar dake kanta ta jefa mata ajiki, Rufaida tasaki ihu mai karfi wanda yasa Barr Barraq tashi zaune da sauri, wai mafarki yakeyi,yanzu yakarajin muryan kurman yarinyar nan daya taimaka a Minna, itace? Kwanciya yayi da sauri saboda yanda kanshi yasara.

Rufaida tace “Duduwa kiyakuri bazan karaba” saida Duduwa taga tana zufa sanan ta janye buhun gyadan daga jikinta tace “dan ubanki tashi kije ki wankesu ki daura a wuta, inyayi zakikai dandali,sai bayan kin dawo zanci ubanki kuma wlh saikin biyani tuluna” ta sakar mata rankwashi aka,Rufaida ta share hawaye ta dauko langa ta juye gyadar ta wanke ta,taje ta hura wuta da kyar sanan ta daura akan wuta, kuka take acikin kitchen din tana Sosa jikinta rabonta da wanka kwana 5 kenan Duduwa tahanata jikinta kaikayi yakeyi sosai,kullum kaya daya take sawa salla ko saida da daddare tayi su duka aboye dan Duduwa bata barinta salla daga safe har dare aiki take bata zama hutawa ko sau daya arana.

Maman Abd Shakur😘
[5/2, 9:10 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

20
Karfe bakwai Muzzamil yakara kiran Dad yace “Dad har yanzu bai isoba fa,nadamu wlh,nasan ba lafiya ba,Dad I can feel it”Dad yace ” me too Muzzamil, yanzu yaza ayi?” Yace”Dad zanbi hanya Nagani” Dad yace “ka sanar da police, in sha Allah inhar bakuga komiba very early gobe zan biyo flight” Muzzamil yace “to”tareda katse wayan. Daukan keys yayi yafita daga hotel din dashi da friends dinshi sukai lodging.
*****

Sai Wuraren mangariba tagama dafa gyadar, idanunta sunyi jaa saboda zafin hayaki, tsumma ta dauka tarike tukunyan zata juye gyadar a langa garin juyewa ruwan ya zuba a hannunta ihu tayi ta saki tukunyan a wurin ragowan gydar tazube akasa,da sauri Duduwa tafito daga daki tana sallallami “Allah yasa ba zubarmin da gyada mayyar nan tayiba” ta shigo kitchen din Rufaida dake kuka tarike hanunta tana ganin Duduwa takara rudewa tafara ja baya, bata ankaraba taji takara taka rushi a kafanta ihun dayafi nada tasaki zata gudu Duduwa ta damki hannunta”zonan ballagaza”iche ta dauka ta bubbuga mata ajiki “kika bararmin da gyada,kinsan da Yaya nasamu nasiyo gyadar nan akasuwa kuwa?” Rufaida tsabagen azaba tama kasa kuka sai ihu “bazan karaba Duduwa, yakuri bazan karaba, wayyo Umma na” saida Duduwa taga tana neman sumewa sanan ta ajiye ichen ta wurgota tsakar gida, ta kwashe gyadar kasan sanan ta fito tazuba gyadar a faranti ta daura gwangwani Kwara daya akai da fara leda tazo gaban bukkan da Rufaida ke kuka tace “dan ubanki tashi kuwuce dandali inba asiyaba komin dare kije har bakin titi ki tsaya sai ansiye tass sanan zaki dawo, kina jina?” Rufaida ta girgiza mata kai,Mari to koda mata tace “cemin to” Rufaida tace “to” tana kuka. Duduwa tasa hannu ta tunbuke dan kwalin kanta ta barbaza gashin kanta dake wari saboda rashin wankewa tace “ahanka zaki tafi saboda aga tsayin gashinki asiye gyadan duka”,ta daura mata farantin gyadar dakeda zafi akai tace “wuce kitafi, gwangwani daya naira goma ne” haka ta tafi,tana tafiya tana dingishi saboda konewar kafanta,tana tafiya tana girgiza hanunta dayay bororo saboda zafin kunar,garin ma yay duhu dan tuni akai sallan mangariba.
Chapter 9 · 0% Book details