← Book details Kaine Sirrina Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 16 OF 43

Sashe 16

Kaine Sirrina Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

34
Ahankali ya zame hannunshi daga nata dayaga yana rawa yace “barshi zan zuba da kaina” da sauri ta mike tsaye zata fita daga dakin yace “amm nace ba” tadan juyo ta kalli center Capet din dake kasar dakin jikinta na rawa. yace”idan aka wanke miki gashin amiki kitso kinji” dagamai kai tayi, tafita daga dakin da sauri hartana tuntube. girgiza kai kawai yayi yanzu shine keson wanan yarinyar,lallai soyayya bakama Barraq adalci ba.

Tana komawa part dinsu tawuce dakinta ta kwanta akan gado tanamaida numfashin tsoro. kai mutumin nan yacika bata tsoro, to maisa lokacin dabaida glass banji tsoron shiba?take ma kanta tambaya a zuci.

Da yamma Mum tasa aka kaita wurin wanke gashi, wanke mata gashin sosai akayi aka mata kitso irin na turawa nan kaman kalaba tai kyau sosai banbancin ta da turawa fari kawai zasu nuna mata dan itabaka ce.

Zaune take a dakin Mum tagama yima Mum gyaran daki duk tai zufa Mum ta shigo tace”daughter kije kima son sallama,yau zai koma Nigeria ” da sauri Rufaida ta kalli Mum saikuma ta maida kanta kasa, Mum ta dauko wani magazine dake kan drower ta zauna kan gadon tana Karantawa. Ahankali ta mike tabar dakin. dakinta taje tasako karamin bakin hijab dinta akan riga da slet din kantin dake jikinta ja,tayi part dinshi, bude kofan tayi ta shiga jikinta na rawa ta tsugunna a kasa ta chusa kanta cikin cinya batare data kalli wani abu na falon ba.

“Zan koma Nigeria yau,kina bukatan wani abu?” Sassanyar muryarshi ya bugi kunnenta, Kanta akasa ta girgiza, yace”are u sure?”ta sake dagamai kai batare data kalleshi ba. Ahankali yace “Rufaida” tadago kanta taga sun hada ido da sauri ta kauda kai dudda yamata kyau sosai yau,yana sanye da suit mai ruwan toka,da neck tie mai gida gida,gashin kanshi yakara yawa gashi ya kwanta. maganarshi ta tsinkaya yana fadin”yau lesson teacher zai fara zuwa yana miki lesson just to keep u busy,and dan kituna abunda kika sani abaya, meanwhile innakai Nigeria zan nema miki certificate da testimonial na primary school, sai na JSSE,zan saki a school a garinnan, inaso kifara daga Ss1,dazaran nadawo zaki fara school kinjiko Rufaida” ta dagamai kai, yadan kalleta kafin ya dauko wayarshi daga kan table yana daddannawa yace”lastly banasonki da wasa,banason na ganki da any friends, be very very serious da karatun ki,dan banason Wanda bayason karatu,ki zama mai kokari da kwazo banda yawan wasa,and ki kasance mace mai kamun kai, da sitirce kanki,karkice dan kinga yanda yan garin ke shiga da aladarsu kice zaki dauka banaso,banason yawan surutu, take good care of ur self Rufaida, kafin na dawo naga kin iya duk abunda lesson teacher ki ya koyamiki,and I also want u to be social, kidinga zama tareda Mummy kina koyan abubuwan datake yi kinji da yanda take interacting da mutane?” Ta girgiza mai kai hawaye na zuba daga idonta, ya mike tsaye yana kallonta kafin yace “zan tafi”.

Ahankali itama ta mike tana share hawayen datake yi amma sun kasa daina zubowa, yadau yar karaman jakarshi yay hanyar fita, ya daura hanunshi kan door handle yaji kukanta yakara karuwa sama danada,juyowa yayi yana kallonta da sauri ta juyamai baya tana kuka, “kidena kuka Rufaida in sha Allah bazan dadeba,nasan Ni kadai kika sani, but karki damu Mummy zata kula dake more than yanda zan kula dake, karki manta abubuwan Dana fada miki,ga dakina nabar miki akwai wasu abu Dana ajiye miki a bedroom kije ki dauka,saina dawo Bye”. yajuya yafita daga dakin Rufaida takara fashewa da kuka, ahankali ta furta ” KAINE SIRRI NA Mai Gilashi, Allah ya kaika lpy”.

Maman Abd Shakur😘
[5/13, 4:02 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

35
Saida tagama cin kukan ta sanan ta shiga dakin tadake tsammani shine bedroom din,hadadden dakine an mai fenti Golden Brown, babu wani tarkace banda wardrobe na bango sai kuma katon table da computer kekai, gefeshi kuma wani farin karamin fishbowl ne da kifaye yan kanana aciki. Hango Babban akwati akan gado yasa takarasa wajen,ta bude akwatin. kayane na sawa kala kala, sai Novel na turenci guda uku, dawani littafi mai suna ” Educative Lady Behavior” ahankali ta mayar da komi ta kulle akwatin tana kallon dakin kafin taja akawatin tabar dakin, taje ta nunama Mum kayan.
Mum ta dinga murna tana shima Barraq Albarka.

Aranan karfe biyu lesson teacher yazo sai biyar yatafi. Hankalin Rufaida yatashi dan bata gane komiba Maths da Biology yamata ita turencin shima ne bata ganewa, tadau littafin ta dinga Karantawa, ganin taki ganewa yasa tai salla biyu na nafila taroki ubangiji yasa ta dinga ganewa. Cikin ikon Allah washegari dayazo yay mata English tadan gane ba laifi ahaka ahaka ajin yacigaba da tafiya harna tsawon wata biyu Wanda a yanzu Rufaida na gane komi daidai gwargwado, akwaita da kwazon ganin ta iya abu. Tana yawan zama da lidiya a kitchen tana koyan girkin da akeyi, gata da gyara jikinta koda yaushe tsaf tsaf take saisa Mum ke alfahari da ita. Tanajin dadin zama da Rufaida har cikin ranta, dan akwaita da girmama na gaba da ita gata da son aiki, kiri-kiri tahana masu gyarama Mum daki gyarawa,ita keyi da kanta, idan washing machine ya wanke kayan Mum ita kezuwa ta shanya idan sun bushe ta kwaso ta gogesu,Mum tai magana tadenayi akwai masuyi har tagaji ta kyale Rufaida dan taki denawa. aganin Rufaida tahakanne kadai zata saka musu abunda suka mata,sun haskaka rayuwarta sun mayar da ita mutum bayan rasuwar su Umma, sun tsamota daga wahalar Duduwa, sun kuma sota,sun nuna mata kauna tomeza tamusu daya wuce kyautatawa da musu biyayya??..

Rufaida kenan akwaita da tunanin manya wani zubin.

Maman Abd Shakur😘
[5/13, 4:24 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

36
Zaune yake a office shida Muzammil. “Muzzamil wlh nakosa nagama abubuwan gabana natafi Russia, dan nasa Rufaida a school, gashi Dad kullum damuna yake da aure,saisa dukna kosa nabar Nigeria gaba day…a” Wayarshi yay ringing kallon wayan yayi yaga baisan number ba, ya share ganin ansake kira yasa Muzzamil ya kalleshi “pick d call mana,it might be important” yadau wayan ya kara a kunne tareda amsa sallaman dayaji an mishi a natse, Alhaji yace”dafatan ka ganeni Barrister ,Wanda yataba kawoma complain kan yarshi tabata,da sauri Barr ya rike kanshi kwata-kwata yamanta da alkawarin dayama mutanen nan zai nemo musu yarinyar su, baimasan inda paper dasuka rubutamai yanda yarsu take yakeba. Da kyar Barr yace” Alhaji am very sorry wlh aiyuka sunmin yawa,but gobe munada wani meeting na Barristoci a Lagos zanbi nyt flight cus meeting is around 8 nasafe,so idan mun gama by 1 zanzo wajenka mu tattauna da kyau kan yarka, ban address din wurinku ” nan Alhaji yabashi address dinshi sukai sallama.

Muzammil ya kalleshi yace “maisa zakaje gidanshi?” Barr yace “yakamata naje,dannai bincike,kuma kasan dole daga gidansu bincike zaifara,anan ne zan iya gathering all d necessary clues”. Muzammil yace” hakane fa” suka cigaba da fira.

Zaune take a garden ita kadai tasa jumpsuit ja,yay mata kyau gashinta dayasha gyara a sake sun zubo har bayanta,littatafan assignment na gabanta. da alumu tai zurfi cikin tunani dan hankalin ta baya kan book din. Jitayi an dafata, afirgice tajuyo ganin Mum ne yasa tai murmushi tace”Mummy”Mum ta zauna a gefenta tarike hanunta cike da damuwa tace” daughter dis days kina yawan tunani meke damunki tell me d truth ” Rufaida tai shiru kaman bazatayi magana ba, saida ta sauke ajiyan zuciya sanan kwalla yacika idonta tace”Mummy nima bansani ba,tun shekaran jiya nai mafarkin wata mata fara kakkyawa nada cikin 9 month,naga tana rashin lpy sosai,hawan jini yakamata,she is really suffering kuma tanata kiran sunana waini take nema,nine sanadin ciwon ta”, takarasa maganan tana kuka sosai. Mum ta rungume ta tana bubbuga bayanta tace “is ok, kidena tsoro is just mafarki,be prayerful kinji” ta dago kanta daga jikin Mum tana murmushi tana share hawayen.
Juyawa tayi tadau littafin gabanta ta bude ta mikama Mum tace” take a look at this Mummy ” Mum ta karba, ihun murna tasaki tareda mikewa tsaye tace “who Drew dis daughter?” Cike da Murna tace”is me,Nina zanaki Mum dazu” Mum ta kalli drawing din sosai,taga exactly fuskarta ne, ta kalli Rufaida tace”dama kin iya Zane haka? ” Rufaida tadanyi tsallen murna tace “Mum nima kawai naga hannuna nata zanaki,ni bansan yanayi ba”, Mum ta kalli drawing din taga dan karamin signature na zanen baby(jariri) tace” Rufaida wanan signature fa?”Maisa kikai signature na Zane?” Tayi dan dariya tace”Mummy wlh bansani ba,nadaiji da ina zanen kaman ina son baby,kawai sainaga na zana small baby as my signature ” Mum ta tafa mata very good daughter, zan siyo miki abubuwan drawing saiki dinga yi,kin fito da sabon samfarin signature. Rufaida tai ihu ta rungume Mum.

Maman Abd Shakur😘
[5/13, 4:38 PM] Aishat Muhammad: 🖌KAINE SIRRI NA🖌

37
Karfe 2 na rana taima Barr Barraq a kofar gidan Alhaji Muhammad. Da kanshi Alhaji yamai iso zuwa Babban falonshi inda aka wadata gaban Barr da kayan ciye-ciye da shaye-shaye.
Bayan wani dan lokacin gaisuwa da labarta bayan rabuwa, Barr Barraq ya kalli Alh da matarshi dayagani da katon ciki haihuwa yau ko gobe yace” nazo nan gidanne cus inaso nahada all d necessary abubuwan daya kamata nasani kan yarku”. Yabude jakan laptop din jikinshi ya zaro wata zungureriyar takarda ya kalli Hj,yace”I will start with u Ma, cus kece uwa,u know ur daughter morthan anybody so inaso kibani labarin yarki takowani bangare”.
Chapter 16 · 0% Book details