← Book details In Bani Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 40 OF 101

Sashe 40

In Bani Complete Hausa Novel · about 8 min read

Wanka tayi duk jikinta ba karfi kaman ciwo nason kamata, wani material lace tasaka red sanan ta tsaya gaban madubi taja eyeliner saman idonta sanan tasaka man baki daya fito da pink lips dinta sosai saika rantse jan baki tasaka ta gyara gashin giranta tai carving dinshi da brush yay wani irin kyau har kyalli yake sanan taciro black hijabinta har kasa tasaka tafito da hannayenta tasaka flat sandals dinta na vintage sanan tadan fesa body spray dinta tafito, bakaramin kyau tayiba bakin hijabin yakara fito da hasken ta sosai kaman wata yar larabawa dama gashi anmata tsifa ta taje gashin tai parking sai hijabin da hulan sukai wani irin das ajikinta, fitowa tayi jin Kaka ta kwala mata kira ta shiga dakin Mama da sauri suna zaune suna magana da Anty Lami tace "Mama Kaka tace wai na shirya narakata wani wuri" tabe baki Mama tayi tace "saikun dawo" kallon Maman ta tsaya yi ganin kaman ranta abace yake jin Kaka ta kwala mata kira yasa tafita da sauri harara Kaka ta watsa mata tace "bazaka fitobane" ahankali tace "yakuri" Kaka tai gaba tana binta abaya tamika mata wani leda ta karba tace "hadaddiyar fura ce mai sanyi sosai mukaje sai kibashi" da sauri tace "wane Kaka?" bude gate Kaka tayi tasakai tafice tace "wanda zaki aura" da sauri tana wani irin kallon Kaka tace "wanda zan aura?" daidai Kaka ta tare napep ta shige ta kalleta tace "wai bazaki shigo ba kin isheni da shegiyar tambaya" ahankali ta shiga tace ma mai keken asibitin prestige suka yatada suka tafi, kusan tafiyan minti ishirin ya kaisu asibitin suka fito Kaka tabada kudi sukai ciki itadai bin Kaka kawai take dan batasan inda Kaka zatakai taba to wama takeda shi mara lafiya, har sukahau bene hakanan taji gabanta yasoma fadi, wani daki Kaka ta dosa tace "yauwa ga dakin chan" suka karasa sallama Kaka ta kwada tareda bude kofan, Baffa ne kawai da Mami adakin sai Aadil dayawani irin rame kwance akan gadon yana bacci dan tunda akamai allura wuraren shabiyun rana bai farkaba, kallo daya Hamida tamusa ta saukar da kanta kirjinta nawani irin bugawa, cikin tsananin murna Mami tazo da sauri tadan duka ta gaida Kaka.

"sannu da zuwa Umma, kunsha hanya, ina yini" tai maganan tana kallon Hamida da kanta ke kasa, dan buge Hamida Kaka tayi cikin style hakan yasa tace "ina yininku" kamo hanunta Mami tayi ta shigo da ita dakin ta zaunar da ita kan kujera tace "welcome daughter na" Kaka ta shigo dakin tana kallon Aadil din tace "Allah sarki jibi yanda yarame Allah ubangiji yabashi lpy" Baffa yace "Ameen" cikin wasa Kaka tace "mudai kutashi mufita mubama yaranmu waje anjima ma dawo" murmushi Mami tayi, cikin fara'a Baffa yace "dama akwai wajen shan iska bari mu sauka, muje Maryama" yama Mami magana, fuskarta Mami ta shafa tace "feel free kinji bari muje mundawo" gyadama Mami kai tayi ahankali duk suka wuce suka fita aka rufo kofan dakin yarage daga ita saishi, ahankali ta dago kanta ta sauke manyan eyes dinta akanshi yanda yake kwance kaman wani maraya yay wani irin kyau a kwance yana sanye da white riga mai dogon hannu sabida sanyin ac dakin sai dogon wando da bakin safa akafanshi, gashin sajeshi sun wani irin kwanta lublub na idanunshi sunyi shar sun wani mike yana sauke ajiyan zuciya ahankali, wani irin taji tundaga kanta har dan yatsar kafarta ahankali ta ijiye ledan cup din furan hanunta akasa ta tashi dagakan kujeran ahankali ta zauna a danta bakin gadon tana kallon fuskarshi kirjinta nawani irin bugawa, dan runtse ido tayi dan sosai duk idan yana bacci ta kalleshi takejin wani irin shakkan shi saidai idan idanunshi biyu ne yanamata abin yaranshi takeji normal harta iya wasa dashi, bude idanun tayi ahankali ta saukesu akanshi asanyaye samin kanta tayi da kiran sunanshi cikin siriruwar muryanta batare data shiryaba dan sosai tai wani irin kewanshi gani take kaman yakai shekara daya rabon ta dashi.

"Aadil" dan motsi yayi kaman yaji kiran sunanshi datayi zatai magana kenan taji anbude kofan dakin da sauri ta dago kanta ta kalli kofar ido da ido tayi da Aabid dake sanye da white riga mai dogon hannu irin na Aadil da dogon wando hanunshi rike da wayarshi iPhone 11, wani irin faduwa gabanta yayi sabida kallon dayake mata da sauri ta sauka daga kan gado zata wuce taji Aadil yarike wrist din hanunta gam hakan yasa arude ta kallai taga idanunshi a lumshe kasa koda motsi tayi saima kanta datamaida kasa kirjinta na dukan uku uku, ahankali Aabid yakaraso tsakiyar dakin ya tsaya agabanta kamshin turarenshi nawani irin shiga hancinta tana kokarin karban hanunta da Aadil yarike gam takasa, rungume hanunshi yay akirji yana kallonta tundaga tsakiyar kanta danyafita tsawo sosai har kafafunta cikin wani irin low voice yakira sunanta.

"Amatullah".
[11/26/2019, 9:08 AM] Aishat Muhammad: _
IN BANI
Maman Abd Shakur
36....

Ahankali ta dago manyan idanunta ta kallai, wani irin kallon dayake mata yasa ta saukar da idanunta kasa ahankali, cikin wani irin cool voice yace "i have a request for you" yadanyi shiru yana kallonta kafin ya cije lips dinshi kadan sanan yasaki sabida wani irin zafi da zuciyarshi kemai kaman an zuba wuta aciki, cikin wani irin low voice mai rauni sosai yace "kece mace tafarko dana faraso Amatullah" yasake yin shiru kafin amugun hankali sama da muryan dazu yace "inhar bazaki aure niba please karki bari amiki auren nan da dan uwanshi" yay shiru sabida wani irin zafi da zuciyarshi kemai, cikin wani irin low voice mai rauni sosai yace "kece mace tafarko dana faraso Amatullah" yasake yi shiru kafin amugun hankali sama da muryan dazu yace "inhar bazaki aure niba please karki bari amiki auren nan da dan uwana, bansan tayaya zuciyata zata iya amsar ki amatsayin matar dan uwana ba amatsayin matata ba, i can't accept wacce nakeso amatsayin matar dan uwana, banson na tsani dan uwana sabida ke, inada mugun kishi seeing u as his wife zai iyasa nai abubuwan da daga baya zanzo nai nadamar aikatawa, karki auri dan uwana Amatullah bazan iya jurewa ba ko kadan, i...i....i love you dayawa Amatullah" yakarashe maganan amugun hankali muryanshi nadan rawa kaman zaiyi kuka yana kallonta, kasa koda dagokai ta kalleshi tayi saima ji tayi da hakanan ta tsani zuwa asibitin dasuka yi harta hadu dashi, meyake nufi da auren dan uwanshi?

Kaka ma dazu tace zasuzo wajen mijinta duk mesuke nufi? motsin dayaga Aadil yayi yasa yajuya ahankali zuciyarshi kaman zai tarwatse yafita daga dakin da sauri tareda rufo musu kofa, ahankali Aadil yabude jajayen idanunshi dasukai mugun ja sun wani irin yin yaushi alamun na wanda baida lafiya sosai, sunkuma mai nauyi, jikinshi komi ciwo yakemai, hanunshi ya kalla ganin yana rike da hanun mutun yasa ahankali cikin muryanshi dake fita da kyar tsabagen yanda zuciyarshi takemai wani irin zafi da nauyi yace "M...ma...mi" da sauri ta goge hawayen daya zubomata jin muryanshi dan samin kanta tayi da mugun daukin ganinshi tajuyo da sauri tana ware mai manyan idanunta murmushi kwance kan fuskarta ta kalleshi suka hada ido ta matso da sauri jikin gadon tadan rankwafo da kanta kadan tana kallonshi tanamai wani irin murmushin dake kunshe da tausayinshi dan kana ganinshi kasan ciwo nacinshi bana wasaba, da sauri tasake share hawayen dake neman zubomata ahankali tace "Aadil" cikin wani irin tsananin fushi da zuciya yature ta da duka ragowan karfin dayake dashi yajuya mata baya ya kalli dayan bangaren yaki kallonta, rike gadon tayi da sauri dan data fadi ta kalleshi asanyaye dan tasan fushi yake da ita dan ta tafi bai ganta ba, da sauri ta zaga ta dayan side din gadon ta kalli fuskarshi ya daure fuska tamau hawaye yataru a idanunshi ta tsugunna ta saitin fuskarshi takira sunanshi ahankali.

"Aadil" da sauri yasake juyar da kanshi ta dayan bangaren dan bayaso ya ganta fushi yake da ita sosai, ahankali ta dafa gadon ta mike tsaye tana kallon bayanshi tace "fushi kake dani danna tafi, am sorry kaji" tai maganan tana zagayowa ta bangaren daya juya tana leken fuskarshi, a sanyaye ta tsugunna ta dafa gadon takai hanunta ahankali dake rawa sosai zata tabamai fuska murya chan kasa tace "am sorry kaji" ture hanunta yayi yasake juya mata baya ya kalli dayan bangaren batare daya kulataba, hawayen datake rikewa ne suka zubo da sauri tasa hannu ta share batasan dalilin hawayen ba amma ko kadan bataji dadin abinda yamata ba, tazaci idan yaganta zaiji dadi yayta murna yana tsalle tsalle ne amma sai baiyiba, rike kukan dayake zuwan mata tayi da karfin gaske ta mike tsaye ahankali tace "tunda bakason gani na shikenan, natafi" tadan tsaya ta kalleshi kozataga yajuyo amma saitaga ko motsi baiyiba balle tasaran zai juyo, sosai gwuiwanta yamata wani irin mugun sanyi ahankali tajuya tana share hawayen dayake zubomata da bayan hannu tafara tafiya, wani irin rungumota akayi tabaya dahar saida ta tsorata, wani irin juyoda ita yayi ta gaba ta kalleshi a tsorace danhar mamakin karfinshi take ya riketa sosai dan gabaki dayanta tana cikin jikinshi fuskarta ne kawai yadan koma baya datake kallonshi dashi, jikinshi zafi sosai kaman wuta, idanunshi sunyi jajir kaman gauta, gashi sun ciko da kwalla sosai amma basu zuboba sai wani irin sheki idanun sukayi yana kallonta dasu numfashin na fita da sauri da sauri yana sauka akan fuskarta, hawaye ne ya gangaro daga idanunta ahankali bakinta narawa sosai tace "am so sorry kaji Aad...." wani irin rungumo kanta yayi yasata ajikinshi ya matseta yafashe da mugun kuka danhar tanajin yanda kirjinshi ke bugawa kaman zai fito yana wani irin shesheka yana make mata kafada, rudewa tayi tana kokarin fizge kanta daga jikinshi amma yaki barinta sai makale mata kafada yake yana wani irin kuka dake tsuma mata zuciya, ahankali takira sunanshi itama kaman zatai kukan.
Chapter 40 · 0% Book details