← Book details Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 34

Sashe 34

Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Na fito da sauri ina shiga sam na manta da kowa ita kawai idanun na ke gani a falon naje na rungume ta ina faɗin Oyoyo Umma. Tace "Kai jama'a to ɗagani mana. Na tashi na zauna muka gaisa, na kalli Hajiya wadda ta zuba mana ido tana murmushi. Tace "To kije ki ce Juma ta kawo mata abin sha da abinci." Nace Umma ina su Jafar ke kaɗanki wai ki ka zo? Tace "Abbanku ya hana." Nace Allah sarki ina son in gansu. Na tafi gurin Juma nace a kawo wa Ummanmu abinci. Tace "Au dama Ummanki ce baƙuwar da Hajiya ta sa ayi wa girki na musamman? Lallai ke da alamu kina samun shiga a gurin Hajiya,ko kuma ku ƙarawa malamin ku sadaka domin ina ganin canje canje a gurin Hajiya." Nace ki kawo mata abincin yanzu. Tace "To za 'a kawo yanzu, ɗakin ki za"a kai ko kuwa gurin Hajiya? Ina ki ke ganin zai fi dacewa? Na tambaye ta. Tace "Tunda ki nemi shawara za a baki tsaya kinibibin cewa a kawo musu ɗakin ki ba, a kai mata gurin Hajiya su yi hirar su ta manya. Sannan kar ki tsoma musu baki wai domin kinga Ummanki, abu na gaba ki jira har sai Hajiya da kanta tace Ummanki taje ta ga ɗakinki. Nace Na gode Baba Juma. Na dawo na zauna a gefe shi Shamaki ma ya shiga ciki. Nace Hajiya suna shiryo abincin. Hajiya ta zura min ido tana tambaya ta. Ɗakin ki za'a kai mata ne?" Nace A"a nan dai gurin ku ko Hajiya..Juma ta zo tana jerewa. Umma tace kayya sai da na gama abinci na taho a ƙoshe nake. Nace haba Umma ai dai ko yaya kyaci abincin gidanmu. Hajiya tace "Ai wajibi ne ma ki ɗauki plate ki zuba mata, sai kije mijinki ya shiga ciki zai shirya ya tafi kasuwa." Umma ta yi karaf ta ce kije ki sallame shi zanci kafin in tafi yanzu dai bana jin yunwa. Nace to. Na tafi da sauri, na same shi yana waya da wasu kwastomomin shi ya ce zai fito nan da awa ɗaya.
Na buɗe durowa na fara zaɓo mishi kaya, ya kamo ni "Zo nan mana kinsan yadda ki ka fito da murna da tsalle ki ka faɗa jikin Umma ina kallon ki sai naji kawai ina bukatar ki, dama yanzu zanje in kira ki. " Cikin mamaki nace haba dai aiko ka ɗaga min ƙafa yau ɗaya Ummana ta zo tana gidan fa kuma ba jimawa zata yi ba, yace ai nima ba jimawa zamu yi ba...

KARSHEN LITTAFI NA BIYU
Mu hadu a littafi na uku
Taku Halima Abdullahi K/Mashi.
Chapter 34 · 0% Book details