Sashe 22
Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na tafi ina mamakin 'yar ƙaramar yarinya ta iya kishi haka. Ɗakinsa na koma na shiga gyarawa har na gama bai zo ba, na fito Juma ta dawo daga kai min abinci nace a kawo turaren gefena tace to, har zan tafi sai nace bari injirata domin inyi amfani da damar in ji wani abu a gurin Juma.
Ta kawo turare, ta ake zata tafi, nace ni ko Baba Juma dan Allah ina da tambaya, sai naga ta juya da sauri tamkar bata jini ba. Na cika da mamaki na kama hanya na yi ɗakina. Kaina gaba ɗaya ya kulle,sai naji an ƙwaƙwasa ƙofa, ina buɗewa sai naga Juma da turaren gefena tace ai 'yannan na jiki ɗazu kiyi hankali ba ko ina ake magana a gidan nan ba domin cike yake da kyamarori. Na zaro ido tace zan samu wani dalili da zan shigo ɗakin baccin ki a ciki ne ba a saka kyamara. Bata jira jin me zance ba ta wuce.
Na koma na zauna daɓas akan kujera, ina tunanin wace irin kyamara, a zuciyarsa nace ƙila irin ta gidan Ya Umar Soja wadda ya sawa Asmy a littafin da na taɓa karantawa na fuska biyu. Ashe dai akwai shi a gaske kenan. To in Yaya Umar Faruk ya saka wa Asmy kyamara domin ya ga abinda take yi in baya nan ko tsoron karya na ƙarta kawo masa namiji gida su kuma nan gidan saboda me suka saka? Dole akwai buƙatar in shiga taitayina sosai, tunda shi kanshi da yake iƙrarin sona bai sanar da ni cewa in kula akwai kyamara ba.
Laf na yi a cikin ɗaki a saman gadona, hatta karin na kasa yi, can naji an buɗe ƙofar falona an shigo. Nasan shine domin naji ƙamahinsa. Na tashi zaune yace "Wai har an yaye ni ne?" Nace kamar yaya? Yace baza a zaɓa min kayan ba? Nace to ai kai nake jira, ga mamakina sai yace "To ba sai a ciro a ajiye min ba tunda an gyara min ɗakin." Na miƙe to muje in baka. Ya kamoni zuwa jikinsa, yace "Baby sai inga kamar kina guduna ne, jiya ki ka ƙi zuwa ɗakin mijin ki." Nace Barci ne ya kwashe ni. Ya ɗago fuskata ya haɗa tsinin hancinmu yace "Ba sai kije can ki yi bacci ba?" Na kumshe ido nace yau zan yi haka.
A ɗakinsa duk da nayi wanka sai da muka sake yi tare domin sai da ya ja dalilin haka, gaskiya na yarda da son da yake min domin ya nuna min zallar hakan sannan ya iya tafiyar da mace cikin sati ɗaya na amarci bani da bakin magana. Damuwata shine ƙaranci lokacin da muke yi da shi. Duk dare sai nayi bacci yake shigowa, ba bu haduwar asbashi, sai da safe kurum muke soyayyar da bata fi ta minti talaatin ko arba'in ba. Ba hira sam, Lokaci dai da zamu zauna mu yi hira babu shi, ko ya fita kasuwa sai dai in masa text na miƙa gaisuwa amma fa in na jiraci amsa to ni ce zanji haushi, ɗan lokacin da ya kan samu ya kira ni ma ba kullum ba.
Ranar da na cika kwana goma sai na tashi da mura da zai fita ya sanar da Hajiya. Tace assha sai an kira likita ne ko kokuwa dai akai mata magani?Yace Ina ganin kawai akai mata magani tunda ta yi aiki ma. Hajiya tace Allah ya sawaƙa.
Ina kwance akan gado naji sallamar Juma nace ta shigo ciki, ta kawo min magani muta tace "Hajiya tace ayi miji sannu." Nace ina amsawa. Tace to tace ayi miki sannu in kinji ba wani sauƙi sai a kira likita. Nace ba komai.
Tace kwanaki kin ce zaki tambaye ni wani abu." Nace e ta ce "To ga shawara duk wani bayani da za ki so ji in kin kwantar da hankalinki zaki same shi, amma in kin fi son ki tambaye ni to kina iya tambaya amma zance ka iya tasowa in faɗawa Hajiya cewa kin tambaye ni abu kaza, bansanta ba amma hakan ka iya shafar jarabawarki. Ta ƙara matsawa kusa ba a banza ki ka ga na kwashe shekaru a gidannan ba, 'yar amanar gidance dan na yaba da halinki ba shine zai sa in zaɓe ki in buɗe musu sirri ba. Na ɗan taɓaki ne domin ku lura da zaman gidan ba wai domin ni da ke mu zama munafukan Hajiya ba." Tuni na yi mutuwar zaune, amma sai na dake nace, Allah sarki Baba Juma waccan ranar dama zan tambaye ki ne ko zan iya zuwa kicin inke tayaku aiki saboda in koyi wanda ban iya ba, to kuma na riga ma na tambayi Hajiya tace in rubuta abinda zan koya sai ta sa a koya min. Juma ta ce "Allah Sarki to ai Hajiya baza ta yarda ki shiga kicin ba, domin Hajiya bata yarda ɗanta ya ci abincin wata matarsa ba. Amfanin ki ɗaya ki biya wa ɗanta buƙata ki haifa masa 'ya'ya. Na danne tsoron da ya taso min nace, to ita matar aure ai bata da yadda zata yi sai abinda mijinta yace. Juma ta juya ta ce ashe dai kin gano." Na bi bayanta da kallo a fili nace akwai aiki.
.....
Na koma na kwanta ina tunani, kullum in na kalli sauƙi ta nan sai ya zama tsuri, na tabbatar wa kai na Juma tana sanar da ni ne cewar bata da sirri sam. Ga gida cike da na'urorin ɗaukar hoto. Yawata ta soma ruri, na duba lambar Umma ce, na ɗaga Jamila ce, cikin rawar murya ta ce Yaya Baby Umma ba lafiya gamu zamu tafi asibiti haihuwa ce tun jiya jini ne ya ɓalle mata da sauri na diro daga gado ina faɗin wane Asibitin ne gani nan zuwa. Tace Murtala zamuje. Da gudu na ja hijabi na saka na sa takalmi har na fita daga falo sai wata zuciyar ta tambaye ni da cewa,kin tambayi mijinki? Na ciri wayar a jaka na yita kiran wayarsa amma bai ɗaga ba. Na nufi gurin Hajiya na tsugunna a gaban ta idanuna sun ciko da hawaye. Tace "Jikin ne?" Nace a a ko maganin ban kai ga sha ba, aka kira Ni daga gida Ummanmu za akai asibiti jini ya ɓalle mata. Tace Ya Salam! To yanzu ya akayi? Nace zanje ne. Tace kin faɗawa mijinki? Na dubeta bai ɗauki wayata ba. Tace to kiyi haƙuri ki koma har sai kin samu izni daga gare shi. Na sake rusunawa nace Hajiya ko ku zaku kirashi wallahi bata cikin hayyacita. Hajiya tace "Samu nutsuwa mana Rabi'atu, ki koma ɗakinki ki jira mijinki ya dawo ko ya ɗaga wayarki, ko kinje baki da wani taimako da zaki iya yi mata bayan addu'a ki koma ciki ki yi mata.
Na miƙe a hankali hawaye suna tsiyaya daga idanuna, na nufi ciki a hankali kamar kazar da ƙwai ya fashe mata na nufi sashe na.
Ina shiga na cire hijabi kaina nayi jifa dashi na na zube nan a ƙasa ina rera sabon kuka tare da kiran dukkan layukan Shamaki amma babu wanda ya ɗaga. Na kira wayar Umma itama Jamilan bata ɗaga ba. Na kira ta Abba shima sai a kira na uku ya ɗauka, cikin kuka nace Abba ta haihu? Yace "Kash waya faɗa miki ba na hana kowa ya sanar da ke ba!" Nace Abba saboda me? Yazun ma saboda baya nan ne shiyasa ban taho ba,amma ya jikin nata? Yace "To a ci gaba da addu'a sun dai shiga da ita ciki har yanzu ba su fito sun ce mana komai ba, sai faɗa suke wai anbarta a gida ta galabaita. Su kuma kowa yasan cewa in ba kuɗi baza su taɓa taɓa mara lafiya ina ta buga bugar neman kuɗinne bansamu na kirki ba gara a gurinta an samu dubu tara."
Nace Abba ka turo Jamila ina da dubu goma ta kawo maka su. Yace "Ina ki ka samu karfa kice zaki taɓa kuɗin mijinki." Nace nawa ne abokan sa suka bani Jamilan ma tasan ina da kuɗin tunda agaban su ne aka bani.
Yace "To zan turo ta yanzu daga nan Asibitin Murtala sannan karki sake ki fito ba tare da sanin mijinki ba." na. Cikin kuka nace to Abba.
Muna aje waya na ɗora sabon kuka ina addu'a. Kamar minti arba'in sai wata wayar tarho da ke maƙale jiki bangon ɗakina kusa da gado ta shiga tsuwa, ni har na tsorata zan fita da gudu na jiyo tsuwa a ɗakin bacci tunda ban taɓa ji ba. Na leƙa na kalli inda nake jin ƙarar sai naga ashe gurin wayar ne, naje na ciro na saka a kunne, muryar Hajiya naji tana cewa "Kece ki ke da baƙuwa a gate? Nace e ni ce ƙanwata ce Jamila. Tace koma waye ba ƙanwarki ba, kamata ya yi ki sanar a faɗawa mutanen da ke gate in ba haka ba baza su barta ta shigo ba.
Cikin dasashiyar muryar da na sha kuka nace zan kiyaye gaba insha Allahu Hajiya tace shike nan. Jamila tana shigowa muka rungume juna muka É—ora sabon kuka,kunsan minti uku sannan na lallasheta na É—akko kuÉ—in na bata, nace su da waye a asibitin tace Umman Amina ce da Umman su Zuhra, sai Abba.
Ta kawo turare, ta ake zata tafi, nace ni ko Baba Juma dan Allah ina da tambaya, sai naga ta juya da sauri tamkar bata jini ba. Na cika da mamaki na kama hanya na yi ɗakina. Kaina gaba ɗaya ya kulle,sai naji an ƙwaƙwasa ƙofa, ina buɗewa sai naga Juma da turaren gefena tace ai 'yannan na jiki ɗazu kiyi hankali ba ko ina ake magana a gidan nan ba domin cike yake da kyamarori. Na zaro ido tace zan samu wani dalili da zan shigo ɗakin baccin ki a ciki ne ba a saka kyamara. Bata jira jin me zance ba ta wuce.
Na koma na zauna daɓas akan kujera, ina tunanin wace irin kyamara, a zuciyarsa nace ƙila irin ta gidan Ya Umar Soja wadda ya sawa Asmy a littafin da na taɓa karantawa na fuska biyu. Ashe dai akwai shi a gaske kenan. To in Yaya Umar Faruk ya saka wa Asmy kyamara domin ya ga abinda take yi in baya nan ko tsoron karya na ƙarta kawo masa namiji gida su kuma nan gidan saboda me suka saka? Dole akwai buƙatar in shiga taitayina sosai, tunda shi kanshi da yake iƙrarin sona bai sanar da ni cewa in kula akwai kyamara ba.
Laf na yi a cikin ɗaki a saman gadona, hatta karin na kasa yi, can naji an buɗe ƙofar falona an shigo. Nasan shine domin naji ƙamahinsa. Na tashi zaune yace "Wai har an yaye ni ne?" Nace kamar yaya? Yace baza a zaɓa min kayan ba? Nace to ai kai nake jira, ga mamakina sai yace "To ba sai a ciro a ajiye min ba tunda an gyara min ɗakin." Na miƙe to muje in baka. Ya kamoni zuwa jikinsa, yace "Baby sai inga kamar kina guduna ne, jiya ki ka ƙi zuwa ɗakin mijin ki." Nace Barci ne ya kwashe ni. Ya ɗago fuskata ya haɗa tsinin hancinmu yace "Ba sai kije can ki yi bacci ba?" Na kumshe ido nace yau zan yi haka.
A ɗakinsa duk da nayi wanka sai da muka sake yi tare domin sai da ya ja dalilin haka, gaskiya na yarda da son da yake min domin ya nuna min zallar hakan sannan ya iya tafiyar da mace cikin sati ɗaya na amarci bani da bakin magana. Damuwata shine ƙaranci lokacin da muke yi da shi. Duk dare sai nayi bacci yake shigowa, ba bu haduwar asbashi, sai da safe kurum muke soyayyar da bata fi ta minti talaatin ko arba'in ba. Ba hira sam, Lokaci dai da zamu zauna mu yi hira babu shi, ko ya fita kasuwa sai dai in masa text na miƙa gaisuwa amma fa in na jiraci amsa to ni ce zanji haushi, ɗan lokacin da ya kan samu ya kira ni ma ba kullum ba.
Ranar da na cika kwana goma sai na tashi da mura da zai fita ya sanar da Hajiya. Tace assha sai an kira likita ne ko kokuwa dai akai mata magani?Yace Ina ganin kawai akai mata magani tunda ta yi aiki ma. Hajiya tace Allah ya sawaƙa.
Ina kwance akan gado naji sallamar Juma nace ta shigo ciki, ta kawo min magani muta tace "Hajiya tace ayi miji sannu." Nace ina amsawa. Tace to tace ayi miki sannu in kinji ba wani sauƙi sai a kira likita. Nace ba komai.
Tace kwanaki kin ce zaki tambaye ni wani abu." Nace e ta ce "To ga shawara duk wani bayani da za ki so ji in kin kwantar da hankalinki zaki same shi, amma in kin fi son ki tambaye ni to kina iya tambaya amma zance ka iya tasowa in faɗawa Hajiya cewa kin tambaye ni abu kaza, bansanta ba amma hakan ka iya shafar jarabawarki. Ta ƙara matsawa kusa ba a banza ki ka ga na kwashe shekaru a gidannan ba, 'yar amanar gidance dan na yaba da halinki ba shine zai sa in zaɓe ki in buɗe musu sirri ba. Na ɗan taɓaki ne domin ku lura da zaman gidan ba wai domin ni da ke mu zama munafukan Hajiya ba." Tuni na yi mutuwar zaune, amma sai na dake nace, Allah sarki Baba Juma waccan ranar dama zan tambaye ki ne ko zan iya zuwa kicin inke tayaku aiki saboda in koyi wanda ban iya ba, to kuma na riga ma na tambayi Hajiya tace in rubuta abinda zan koya sai ta sa a koya min. Juma ta ce "Allah Sarki to ai Hajiya baza ta yarda ki shiga kicin ba, domin Hajiya bata yarda ɗanta ya ci abincin wata matarsa ba. Amfanin ki ɗaya ki biya wa ɗanta buƙata ki haifa masa 'ya'ya. Na danne tsoron da ya taso min nace, to ita matar aure ai bata da yadda zata yi sai abinda mijinta yace. Juma ta juya ta ce ashe dai kin gano." Na bi bayanta da kallo a fili nace akwai aiki.
.....
Na koma na kwanta ina tunani, kullum in na kalli sauƙi ta nan sai ya zama tsuri, na tabbatar wa kai na Juma tana sanar da ni ne cewar bata da sirri sam. Ga gida cike da na'urorin ɗaukar hoto. Yawata ta soma ruri, na duba lambar Umma ce, na ɗaga Jamila ce, cikin rawar murya ta ce Yaya Baby Umma ba lafiya gamu zamu tafi asibiti haihuwa ce tun jiya jini ne ya ɓalle mata da sauri na diro daga gado ina faɗin wane Asibitin ne gani nan zuwa. Tace Murtala zamuje. Da gudu na ja hijabi na saka na sa takalmi har na fita daga falo sai wata zuciyar ta tambaye ni da cewa,kin tambayi mijinki? Na ciri wayar a jaka na yita kiran wayarsa amma bai ɗaga ba. Na nufi gurin Hajiya na tsugunna a gaban ta idanuna sun ciko da hawaye. Tace "Jikin ne?" Nace a a ko maganin ban kai ga sha ba, aka kira Ni daga gida Ummanmu za akai asibiti jini ya ɓalle mata. Tace Ya Salam! To yanzu ya akayi? Nace zanje ne. Tace kin faɗawa mijinki? Na dubeta bai ɗauki wayata ba. Tace to kiyi haƙuri ki koma har sai kin samu izni daga gare shi. Na sake rusunawa nace Hajiya ko ku zaku kirashi wallahi bata cikin hayyacita. Hajiya tace "Samu nutsuwa mana Rabi'atu, ki koma ɗakinki ki jira mijinki ya dawo ko ya ɗaga wayarki, ko kinje baki da wani taimako da zaki iya yi mata bayan addu'a ki koma ciki ki yi mata.
Na miƙe a hankali hawaye suna tsiyaya daga idanuna, na nufi ciki a hankali kamar kazar da ƙwai ya fashe mata na nufi sashe na.
Ina shiga na cire hijabi kaina nayi jifa dashi na na zube nan a ƙasa ina rera sabon kuka tare da kiran dukkan layukan Shamaki amma babu wanda ya ɗaga. Na kira wayar Umma itama Jamilan bata ɗaga ba. Na kira ta Abba shima sai a kira na uku ya ɗauka, cikin kuka nace Abba ta haihu? Yace "Kash waya faɗa miki ba na hana kowa ya sanar da ke ba!" Nace Abba saboda me? Yazun ma saboda baya nan ne shiyasa ban taho ba,amma ya jikin nata? Yace "To a ci gaba da addu'a sun dai shiga da ita ciki har yanzu ba su fito sun ce mana komai ba, sai faɗa suke wai anbarta a gida ta galabaita. Su kuma kowa yasan cewa in ba kuɗi baza su taɓa taɓa mara lafiya ina ta buga bugar neman kuɗinne bansamu na kirki ba gara a gurinta an samu dubu tara."
Nace Abba ka turo Jamila ina da dubu goma ta kawo maka su. Yace "Ina ki ka samu karfa kice zaki taɓa kuɗin mijinki." Nace nawa ne abokan sa suka bani Jamilan ma tasan ina da kuɗin tunda agaban su ne aka bani.
Yace "To zan turo ta yanzu daga nan Asibitin Murtala sannan karki sake ki fito ba tare da sanin mijinki ba." na. Cikin kuka nace to Abba.
Muna aje waya na ɗora sabon kuka ina addu'a. Kamar minti arba'in sai wata wayar tarho da ke maƙale jiki bangon ɗakina kusa da gado ta shiga tsuwa, ni har na tsorata zan fita da gudu na jiyo tsuwa a ɗakin bacci tunda ban taɓa ji ba. Na leƙa na kalli inda nake jin ƙarar sai naga ashe gurin wayar ne, naje na ciro na saka a kunne, muryar Hajiya naji tana cewa "Kece ki ke da baƙuwa a gate? Nace e ni ce ƙanwata ce Jamila. Tace koma waye ba ƙanwarki ba, kamata ya yi ki sanar a faɗawa mutanen da ke gate in ba haka ba baza su barta ta shigo ba.
Cikin dasashiyar muryar da na sha kuka nace zan kiyaye gaba insha Allahu Hajiya tace shike nan. Jamila tana shigowa muka rungume juna muka É—ora sabon kuka,kunsan minti uku sannan na lallasheta na É—akko kuÉ—in na bata, nace su da waye a asibitin tace Umman Amina ce da Umman su Zuhra, sai Abba.