← Book details Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 34

Sashe 28

Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Cikin kwanaki yanayi na ya fara canzawa na rame kuma na rage walwala. Shima ya lura da haka ya matsa min da tambaya na ce ba komai, ya siya min waya Iphone 13 yace in bawa Jamila waccan buɗe min Whatsapp duk wai dan in saki raina, ya min gargaɗi wai kar in shiga wasu groups irin na Whatsapp ɗinnan wanda ake zuga mata, wai Maman Mubina ta taɓa shiga wani group wanda suka yi ta samun matsala da shi. " Nace masa zan kiyaye nace wa Hajita ta taya ni yi masa godiya dama a gaban ta ya bani. Yana ta ƙoƙarin in saki jiki in koma walwala ta amma na kasa. Ina kuma ci gaba da bibiyar shi ta wayarshi ina ganin yadda yake ci gaba da hulɗa da mata, abinda na gama lura shine ya kan haɗu da wasu, wasu kuma baya haɗuwa da su,amma yana ba su kuɗi.
Cikin haka azumi ya gabato. Da dare yana falon Hajiya da yake tun daga wannan ranar nike zuwa ina zuba masa abincin dare da na safe, wanda da ashe Azima ke zuba masa na daren na safe kuma da kansa. Daga shi har Hajiya ni ce ke zuba musu.
Hajiya tace Baby kin kuwa san Azima bata da lafiya kin duba ta? Nace bansani ba,tace to ya kamata ki yi mata sannu jiya da yau bata je makaranta ba. Nace Subhanallah! Na tashi na nufi duba ta tunda na zuba musu abincin. Tana lullɓe na mata sannu ta amsa,har zan fita sai tace "Ki faɗawa Yaya ina jiran shi." Na yi shiru,sai na juyo nace kamar yaya kina kina jiranshi? Tace " Shi ya sani." Sai na ji gaban ya yi wata muguwar faɗuwa tsoro da fargaba sun kamani kar dai har wannan yarinyar...Ta katseni, "Ko kina nufin baki san ni wacece a gurinsa ba?" Bance ƙala ba na fice domin yin sa'insa da yarinyar zai zama zubda ƙimata.
Na koma Falo na samu su Hajiya suna zancan Umara, nace da Hajiya zan jira in shafa maki maganin ƙafa tunda Azima ba lafiya. Tace "To Allah ya yi miki albarka jiya ma ba'a shafa ba. Na koma gefe ina kallo a talabijin.
Yace "Hajiya kujeru goma ne a wannan karon an ƙara biyu, yanzu sai ki bada sunayen mutane bakwai ni da ke da kuma Baby mune cikon na goma." Kamar a mafarki na ji maganar, zani Umara, amma sai dai ba dani suke magana ba dan haka sai na share na yi kamar banji ba.
Hajiya ta ce ka cire Baby a maganar ta fiya Ummara da aikin Hajji sai wata shekarar. Ban waigo ba kuma ban nuna ina jinsu ba. Ba tare da ya tambayi ba'asi ba ya ce "To an cire ta." Suka ci gaba da lissafin su. Sai kusan goma da rabi tace zo ki shafa min maganin nan. Na zo na fara shafa mata gami da matsa ƙafafun, tace "Kai amma na ji daɗin yadda ki ka matsa min ƙafafun nan, ina ganin ma dai ke zaki koma shafa. min maganin nan domin Azima sai ta koya. Nace to insha Allahu zan ke shafa miki. Shamaki yace, "wai kuwa likita ya duba jikin Azimar ? Hajiya tace ya duba ta,kasan bata rabo da zazzaɓin cizon sauro, can take zuwa ɗan lambu can har magariba. Na dube shi, baka je ka duba ta bane? Yace "Sai na shiga zan kwanta sai in duba ta.'
Daya ke ina son in wanke zargi sai na raya cewa zan bi bayanshi. Haka kuwa nayi mun tafi tare mun sallami Hajiya na ce masa bari inje ɗakina in ɗakƙo kayan bacci.
Yana shiga falon shi na dawo na shiga falon dai-dai lokacin yana fita ƙofar da zata kai shi gurin su. Na bishi sai da
na ga ya tura ɗakin Azimar ya shiga sannan na bishi ciki faduwa gaba tare da fatan kar zargi na ya zama gaskiya. Dai-dai Window bana jin komai na yanke shawarar in afka ɗakin kawai tare da sallama ko zan tsinci kalma guda ɗaya da zan gamsu. Dan haka sai na afka kawai tare da sallama. Yana tsaye bakin gadon ya maida hannuwan shi duka baya, tana kwance riginnine tana kallon shi yana magana. Kalma ɗaya na tsinta a maganar itace.. " Baruwana..." Na kalleshi sai na ga ya yi alamar rashin gaskiya amma sai ya da ke. Na dube ta sannu da jiki Azima fuskarta ba walwala tace Yawwa. Na dube shi, Nace ta ƙi tasha magani ne baji kana cewa baruwanka? Da sauri ya ce ba maganar ki ɓace, muje ya dube ta yace "Allah ya ƙara sauƙi." Na sake kallon ta ƙwalla ce a idanunta,gaba na ya faɗi ko dai ya haiƙewa yarinyar nan ne to Allah ya sa ba ciki ne da ita ba. Sai naji na kasa jan ƙafafuna na tsaya ina kallon ta. Muryar shi ce ta katse ni. "Muje mana Baby" Na ja ƙafa na bishi dai dai window yara ya tsaya yana kallon su. Ni kuma shi nake kallo ina me takaici abinda ya ke aikatawa amma kamannin shi na salihan mutane ba zai taɓa bari a zarge shi ba. Ya yafito ni da hannu na isa gurinsa ya kama kafaɗa ta yace Kalli yaranki suna ta bacci 'yan rigim. Na lalle su abin sha'awa kowacce laf a gadon ta. Nace Ina son yaran nan sosai musamman Anisa ƙila domin ta kasance ita ce ƙara. Yace "Ba domin tana ƙarama bane, tun ranar da mahaifiyar ta ta haifeta kowa ya ganta sai ta shigar masa rai." Nace Allah sarki, wai kuwa iyayen su suna zuwa su gan su? Yace "Gaskiya dai ba sa zuwa,kuma Hajiya ce ta tsara haka,amma duk hutu ana kai su suyi sati ɗaya sai a ɗakko su." Na ɗaga kai sannan nace Allah sarki amma kana yi wa yara nan addu'a ko Allah ya tsare su daga sharrin zamani. Yace "Baby daga dukkan sharri na ke musu addu'ar tsari." Ya kama hannu na muje muje ɗaki ki faɗa min yaushe zaki bani ta wajen ki Baby Zeena ɗin? " Na bishi ina faɗin ni bana son ma in haihu. Bansan a fili na furta kalmar ba sai da naga ya tsaya can. Na kalli fuskar shi launin fuskar shi ta canza gaba ɗaya, wannan ce rana ta farko tunda na zo gidan da naga ɓacin ransa a kaina, ya tsira min ido take fargaba da tsoro suka tsirga min. Ya fincike ni zuwa ɗakin baccin sa ya tura ni kan gado ya jawo kujera ya zauna a gabana ya ce "Maimaita abinda ki ka faɗa." Na girgiza kai cikin tsoro tare da ɗora tafin hannuna a bakina. Yace "Ki maimaita!" Yadda ya yi maganar da ƙarfi sai na tsorata hawaye suka soma zubo wa,nace nifa na yi tsammanin a zuciya na yi maganar. Yace "To me yasa zaki fadi hakan ko a zuciyar ki? Kice ke bakya son ki haihu to faɗa min da lilinki kuma kar ki sake ki min ƙarya." A zuciyata dalilina saboda neman matan da ya ke yi ne, kuma naji ance duk abinda ka yi wa ɗan wani sai anyi wa naka. Amma bani da damar faɗar hakan dan haka sai nace Ni dama na faɗi haka ne saboda ina jin tsoro kada in haihu ni ma ka sake ni kamar yadda ka saki su Maman Anisa kuma ka karɓi 'yar ka kabar ni ina tunanin ku. Na kai ƙarshen maganar da sakin wani kukan. Ya tashi ya dawo bakin gado ya janyo ni jikinsa ya rungume ni tsam. Yace" Baby ni da ke babu abinda zai rabamu sai mutuwa, akan ki na fara soyayya duk auren baya ashe ba soyayya na yi ba sha'awa ce kawai." Na ɗago na dube shi nace dama ana aure saboda sha'awa? Yace "Ni kaina ban gane hakan ba sai bayan auren sai inji duk sun fita a raina." Nace sai kawai ka sake su? Yace 'A'a Baby babu wadda na saka saboda hakan sai bisa wani dalili na Hajiya wanda har yanzu ban san shi ba." Nace Ni ma na fara fita a kan ka ko? Cikin far gaba na yi tambayar. Yace "Baby kullum ƙara son ki nake yi, da kika ce baki son ki haihu kalmar ta min zafi, ya kai hannu ya shafa cikina, na ƙosa inga wannan shafafen cikin ya tasa ya ɗanyi tudu, ina son inga naki salon laulayin dame zai zo." Na zuba mishi idanu a zuciya ta kuwa tunowa ta ke da kalaman da ya ke rubutawa na batsa da hannun sa yana turawa matan banza,ga waccan yarinyar da nake zargin su da ita.
Chapter 28 · 0% Book details