← Book details Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 34

Sashe 30

Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Gaban hoton mu na tsaya wanda yake bani kyauta ina kallo shi. wayata ta yi ringin na ɗauka na kalli fuskar wayar na sa a kunne tare da faɗin babban baƙo ka dawo ne? Yace "Duk jan lokacin da aka yi ana nema min suna ƙarshe in ƙare da wani babban baƙo babu ko daɗin ji." Na yi dariya nace in har kaine Babban baƙon mu na ranar saukar karatunmu to kuwa sunan da zaka ci gaba da amsawa ke nan. Yace "A hakan ma ni ne da godiya, domin a keɓaɓɓen lokaci akan kira ni da Baby sweet heart da sauran sunaye cikin shagwaɓa. To kina ina ne yanzu?" Nace ina zani ina gida akwai wani abu ne?" Yace "a'a' Na kira Hajiya ne bata ɗaga ba, nace ina ɗakina ne amma bari in duba maka, kariƙe wayar har inja falon, yace "to kije ina jinki.
Na isa falon Azima ce zaune su da Hajiya kan Azima a ƙasa kamar dai tana kuka, Hajiya kuma cikin wani yanayi da bazan iya fassarawa ba. Na ƙarasa nace Hajiya Shamaki ne ya ke son ku yi magana. Hannu kawai ta ɗaga min, wanda bana bukatar sai an faɗamin cewa bata son jin maganar kowa.
🖊️🖊️🖊️
*HAMSHAƘIYAR UWA🧕🏻*

*NA*

*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*

_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_

*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_

*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*

*Page 34*

Ta katse ni, "Bakya buƙatar dogon tunani Rabi'atu, akwai wani sirri ne da ki ke ɓoye wa na sa?" Na girgiza kai babu Hajiya. Tace "Gaskiya ban yarda ba, kina dai rufawa mijin ki asiri ne, ina son ki sani kalmar ki da kika furta ita take nuna cewa mijinki ya na leƙe leƙe." Na ce Subhanallah Hajiya bana zargin sa kuma bashi da kama da haka, in kin duba sam bashi da lokacin kansa bare na yawon banza,kawai dai na furta ne saboda akwai masu yi, ni kuma godiya ce ga Allah da bai bani irin wancan ba,ya bani wanda zai aje mu mu huɗu.
Hajiya tace "To iya magana Sarkin zance Allah ya shiryar da duk ɗan musulmi. Nace Ameen,tace tashi ki kai masa kankanar, saura kije ki faɗa masa abinda na ce game da ƙara aurensa. Na ce bazan ce komai ba.

Na tafi da kankana na tura falon a hankali na shiga baya fakon na aje masa a gurin da yake ajewa na nufi ɗakin zan shiga da yake tun da na saka shi a tarkon zargina bana yin wani kwakwaran motsi in zan shiga gurinsa. Cikin Sa'a naji yana waya, yana faɗin "Sweetheart gaskiya ban taɓa samu mace mai suna mace kamar ki ba, a tafiyar nan ta sati ɗaya kin ji dadi banso muka rabu ba. Ta faɗa masa wani abu sai naji ya ce "Da gaske Babyna to ai kin haɗu ne, bana son a yi min kishiya don Allah a dai riƙe min amana. Kuma a turo min hotuna in kalli abubuwan... Hannu na saka na toshe kunnuwa na,sannan na juya da sauri, cikin rashi sa'a na bigi wata tukunyar fulawa da ke aje a gefe sai ta faɗi. Da sauri ya katse wayar ya fito,daidai lokacin na murɗa ƙofar zan fita, yace Baby! Yadda ya kira ni kasan cikin fargaba ya ke.
Bazan iya juyowa in Kalle shi ba,kalaman sa suna min yawo a cikin kai dan haka sai kawai na fice,da gudu na ƙarasa ɗakina kan gado na faɗa ina maida numfashi na soma karanta duk wata addu'a da ta zo baki na. Ina jin ƙarar buɗe ƙofa nasan shine, don haka sai na soma ƙokarin daidaita yanayi na. Ya shigo ya tsaya yana kallo na. Na ɗago da kyar na zuba mishi ido. Hawaye suka soma kwaranya a idanuna. Ya zauna jiki a sanyaye, ya ce. "Menene ki ka fita da sauri ina kiran ki?" Cikin rawar murya da zubar hawaye nace babu komai. Ya kama hannuwa na, a yau sai naji tafin hannun sa mai taushi kamar ƙaya . Yace Baby dole akwai wani abu ki faɗa min. Na girgiza kai ba komai. Na saɓule hannu na daga nasa,kaje ka ci kankanar ka na ajiye. Ya ƙara kama hannu na "To tashi muje mu sha sai mu kwanta. " Na sunkuyar da kai, ka yi haƙuri yau zan kwana a nan. Ya yi shiru, yana ƙoƙarin tabbatar da zargin sa,tabbas yarinyar nan ta ji wayar sa. Ya sunkuyar da kai yana tunanin abinda ya kamata ya yi. Na zame a hankali na kwanta ina nanata ambaton sunaye Allah a zuciyata ba shakka duk matar da mijinta ke neman matan waje alal haƙiƙa tana cikin masifa.Na lumshe ido hawaye suna kwaranya ta gefe. Ina jinsa ya miƙe jiki ba ƙarfi ya kama hanya,na bishi da kallo har ya fice ya rufo min ƙofa,na tashi na zauna zaman dirshan na saka kuka. Nayi mai isata, sannan na miƙe na shiga ban ɗaki na ɗauro Alwala na zo na shiga jero salla, ba zan iya ƙirga yawan sallamar da na yi ba har sai da naji ina jin kiri sannan na zube a sujjada ina raira kuka a gaban Ubangiji na kasa furta komai sai faɗi nake Ya Allah! kai ne mahalicci na, Allah ka gani,Ya Allah! Ka gani. Bacci ya ɗauke ni a nan, a durƙushe.

Kiran sallar farko ya farkar da ni, na tashi duk jikina ya yi tsami saboda irin kwanciyar da nayi dakyar na yo alwala nazo na ɗora sallah. Aka tayar da sallah inajin yana ƙwanƙwasa ƙofa ta,ban tashi ba na ci gaba da sallah. Bayan na idar na zauna ina tunanin kishin me zan tsaya yi da duk wadda zai auro, domin da ya kawo su ya aje zai komawa matan waje, kuma duk yadda aka yi Hajiya tasan yana bin mata, tana zaton ko na gano ne. Yanzu wane mataki ya kamata in ɗauka shine damuwa ta. Na farko bazan nemi ya sake ni ba, domin yin hakan babban laifi ne,banda haka sonshi ko kyas bai ragu a zuciyata ba amma na san tabbas ina jin haushin sa a yanzu,yana faɗawa wata ƙaruwa wai shi bai taɓa jin mace irinta ba,ni kuma fa?
Wata zuciyar tace ki dafa shi da ruwan sanyi dan kina sonshi kar ki yarda ki zama kamar wata shashasha. A fili nace Allah ka bani basirar yadda zan tafiyar da wannan bawan naka.Allah ka shiryar da shi.
Wayata ta soma ringin a firgice na É—akko ta kardai wani abu ne ya faru a gidan mu. Ashe shine, yace ki zo ki same ni a gurin Hajiya. Nace to.
Ashe shima haka ya kwana cikin tashin hankali ya tabbatar taji maganar dan haka sai da ya gama tunanin abinda ya kamata ya yi ƙarshe ya yanke shawarar kawai ya faɗawa Hajiya ko ma dai menene ta shawo kanta domin shi duk nauyin ta ya kamashi balle da ya zauna yana tuna kalaman batsa da suka dinga musaya da yarinyar bai san tun yaushe ta shigo ba. Inhar ta ji komai gaskiya ya yi abin kunya babba.

Na durƙusa na gaida Hajiya kamar yadda na saba. Na dube shi shima na gaishe shi kamar ba komai.
Ya kalli Hajiya ya sunkuyar da kai, sannan yace Hajiya na kawo kaina ne bisa ga wani laifi da nayi Wa Baby,ina son a taya ni bata haƙuri kuma insha Allahu zan kiyaye. Ciki mamaki Hajiya ta ke kallon baƙon lamari Shamaki yana neman afwar Babu har da haɗawa da ita,to wane irin laifi ne haka? Na katse mata tunani da cewa Ya Salam! ni ce kaimin laifi? Yace ki bar wani alaye Baby na yi kawai tun jiya kin dage ba komai,amma kina ta kuka shi kuka dama ana yin shi haka kawai ne, kuma na ga tsanata a ƙwayar idanunki kin ƙauracewa shimfiɗa ta ko bacci banyi ba. Bazan jure kiyi fushi da ni ba. Na kalli Hajiya wadda ta tsura min ido, na sunkuyar da kai. Hajiya tace ka tashi ka shiga ciki ka bamu guri.
Chapter 30 · 0% Book details