Sashe 10
Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Nace to Zubaina ku nake jira ku shiga ku aje ku zo muje. Suka fara murna ga amarya ga amarya. Da sauri suka fito. Zuhra ta ce, "Wannan ƙamshi Yaya Baby har kin koma kalar bota ɗin." Nace kun fiye surutu. Muka kama hanya Jamila ta ce "Su Mariyan can lungun dama ƙawayanki ne?" Nace wai ta gidan gurasa? Tace "Su." Nace ina ni ina waɗannan marasa kamun kai? Tace "To sau uku suna zuwa nemanki, kuma na gansu gun party sunsha rawa." Na kwashe da dariya, nace yanzu Fati mai awara ta barnan, wai zasu zo mu kwana kin san su dawa? Tace 'a' a, su da Maimunar gidan Alhaji. Gaba ɗaya muka sa dariya. Zuhra tace "Ki kore su ne, saboda abokan ango suke yin wannan shishshigin ko suma wani zai ce yana so." Amina ta ce "Haka ne Yaya Baby. Na ce ba kora su zo. Kuma ba lallai akan tunanin su cewa Yaya shi ɗan Ali Baita ne tunda har zuwa yanzu banji daga bakinsa ba. Jamila tace "Haba yaya Baby karmu ruɗa kan ki mana, wace sauran hujja ki ke jira? Jiya ganin shi da 'yan uwansa ya isa hujja, ƙila ya dai ɓoye miki ne ko yana son ya miki bazata ne, kuma salon ya birge, Abba cewa ya yi shi tun a katin gayyata ya so ya fahimci haka." Da sauri nace wake da katin a cikin ku? To ni ban ma tsaya na kula da katin ba. Amina tace "Mu shiga gida in ɗauko miki." Tabarma muka baza a tsakar gida muna zama sai ga su Fati, nan suma suka saje da mu ana labari. Nace Amina ina katin? Tace "Shi nake dubawa na Abbanmu ne Allah ya sa bai fita da shi ba." Can kuwa sai gashi ta samo. Na kunna fitilar wayata ina karantawa. Tabbas iyalan marigayi A Baita. Shi kuma a sunansa sai aka sa Aliyu A.Baita, sam ban gane komai ba sai yanzu. Na miƙa mata kati tare da faɗin biri ya yi kama da mutum. Na Dulmiya cikin tunani, nifa zuciyata da son Aliyu Shamaki mai tsare kaya ko sai da kaya shagon mai gidansa a Zeena plaza kanti kwari ta kamu. Bawai Aliyu Ali Baita ba. Na ɗauki wayata na soma rubuta saƙo zuwa ga Yaya. Kalmar da na soma rubutawa itace...Yaya akwai babbar matsa. Ina buƙatar sanin wasu abubuwa game da kai.
Ina tura saƙon na tashi naje nayi alwala na shiga ɗakin Umman Amina nayi salla, ina idarwa Jamila tana shigo wa, ta zauna kusa da ni. "Yaya baby wai lafiya naga duk kin canza tunda ki ka karanta katin nan?" Na ce Jamila in har ta tabbata Yaya shine ɗan Ali Baita to bazan aure shi ba. Ta rufe min baki da tafin hannunta. "Menene haka ki ke faɗa, maimakon ki yi murna ki ce Alhamdulillah Allah ya miki gata sai kuma ki ɗebo wata rigima? Na ce Jamila masu kuɗin nan suna da wulaƙanci, in zargin nan ya tabbata Hajiyar da muka je gurinta ita ce mahaifiyar sa. Ta yaya zan iya zama da wannan Hamshaƙiyar. Me yasa har zuwa yau bai faɗa min gaskiyar shi ba, dubi yadda 'yan matannan suka cika gidan nan saboda kawai zan auri ɗan Ali Baita, ki tuna yadda za su yi dariya a lokacin da ya sako ni. Gara yanzu aji ni nace na fasa. Jamila tace "Duk wannan hasashen ki ne, waya faɗa miki zai sake ki?" Nace ya saki mata uku ni ce 'yar gwal? Tace "Shawara ta ɗaya ki kira shi ku yi magana." Nace na tura masa saƙo. Ta amshi wayata da sauri ta shiga ta karanta abinda na rubuta. Ta kalle ni. "Wayyo Allah Yaya Baby, ya zaki masa irin wannan saƙon." Nace To me zance masa. Sautin kiran wayata ya katse mu, ta miƙo min "Gashi yana kira." Na ɗaga tare da sallama. Yace "Babyna kin ci abincin kuwa?" Nace ba zan iya cin abinci a halin da nake ciki ba. Yace "Subhanallah me yafaru?" Nace baka ga saƙon na ba kenan? Yace Gaskiya babu wani saƙo da ya shigo cikin wayata. Ki faɗa min menene?" Amma kafin nan ƙifara cin abinci. Nace ba'a gama miya ba tukunna. Yace "To ki jira ni." Ya kashe wayar. Na kalli Jamila, na san ya gani kawai zai ce min bai gani bane. Jamila ta ce "Ki bari ya zo ɗin karki yanke hukuncin da ba haka bane."
Shigowar 'yan gidan gurasa ya sa raina ƙara ɓaci. Jamila tana ta lallashina da ƙoƙarin nuna min cewa ƙila ya ɓoye min ne saboda wani dalili nashi. Ta tilasta min zuwa gurin da 'yan matan suke muka gaggaisa ana ta hirar gurin Party tare da kallon hotunanmu. Duk kowacce tambaya take wai ina muka haɗu da shi. Nace shi ya kawo kanshi har lungunmu, inda ya ganni. Maimuna tace gashi daga gani yana mugun sonki, ko ina a hoton yana kallonki. Wayata dake hannun Jamila tana tura min hotunanmu a wayar Mariya ta soma ringin. Jamila tace ga ango yana kira, na amsa duk suka bi ni da ido, na ɗaga da sallama. Yace ina ƙofar gida. Nace sai ka ƙaro gaba gida na ƙarshe a lungun can zamu kwana. Yace "To ki fito ki tare ni." Nace to. yace "Kada ki kashe wayar fa." Nace to. Na saka takalmi ina ce musu bari in dawo, sai naji kusan duk sun amsa da to amarya. Ina fita yana ƙarasowa ya aje ledar hannunsa, ya zauna a bakin dakalin. Na ƙarasa na zauna, na gaida shi cikin girmamawa kamar yadda na saba. Ya amsa sanan yace "Faɗa min wane saƙo kika Turi min?" Na sunkuyar da kai cewa na yi akwai matsala. Na ɗago na dube shi, Yaya ka faɗa min waye kai?" Yace "Me kike son sani?" Kai ɗan Ali Baita ne? Na jeho masa tambaya. "Me yasa kika tambaye ni?" Na juya masa baya, ka bani amsa kawai In shine me zai faru?" Ya sake jeho min tambaya. Ban yi soyayya da ɗan Alhaji Baita ba, da Aliyu na yi soyayya talaka mai tsaron kantin Zeena plaza.
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
*HAMSHAƘIYAR UWA🧕ðŸ»*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*
_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_
*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_
*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*
*Page 18*
Ina tura saƙon na tashi naje nayi alwala na shiga ɗakin Umman Amina nayi salla, ina idarwa Jamila tana shigo wa, ta zauna kusa da ni. "Yaya baby wai lafiya naga duk kin canza tunda ki ka karanta katin nan?" Na ce Jamila in har ta tabbata Yaya shine ɗan Ali Baita to bazan aure shi ba. Ta rufe min baki da tafin hannunta. "Menene haka ki ke faɗa, maimakon ki yi murna ki ce Alhamdulillah Allah ya miki gata sai kuma ki ɗebo wata rigima? Na ce Jamila masu kuɗin nan suna da wulaƙanci, in zargin nan ya tabbata Hajiyar da muka je gurinta ita ce mahaifiyar sa. Ta yaya zan iya zama da wannan Hamshaƙiyar. Me yasa har zuwa yau bai faɗa min gaskiyar shi ba, dubi yadda 'yan matannan suka cika gidan nan saboda kawai zan auri ɗan Ali Baita, ki tuna yadda za su yi dariya a lokacin da ya sako ni. Gara yanzu aji ni nace na fasa. Jamila tace "Duk wannan hasashen ki ne, waya faɗa miki zai sake ki?" Nace ya saki mata uku ni ce 'yar gwal? Tace "Shawara ta ɗaya ki kira shi ku yi magana." Nace na tura masa saƙo. Ta amshi wayata da sauri ta shiga ta karanta abinda na rubuta. Ta kalle ni. "Wayyo Allah Yaya Baby, ya zaki masa irin wannan saƙon." Nace To me zance masa. Sautin kiran wayata ya katse mu, ta miƙo min "Gashi yana kira." Na ɗaga tare da sallama. Yace "Babyna kin ci abincin kuwa?" Nace ba zan iya cin abinci a halin da nake ciki ba. Yace "Subhanallah me yafaru?" Nace baka ga saƙon na ba kenan? Yace Gaskiya babu wani saƙo da ya shigo cikin wayata. Ki faɗa min menene?" Amma kafin nan ƙifara cin abinci. Nace ba'a gama miya ba tukunna. Yace "To ki jira ni." Ya kashe wayar. Na kalli Jamila, na san ya gani kawai zai ce min bai gani bane. Jamila ta ce "Ki bari ya zo ɗin karki yanke hukuncin da ba haka bane."
Shigowar 'yan gidan gurasa ya sa raina ƙara ɓaci. Jamila tana ta lallashina da ƙoƙarin nuna min cewa ƙila ya ɓoye min ne saboda wani dalili nashi. Ta tilasta min zuwa gurin da 'yan matan suke muka gaggaisa ana ta hirar gurin Party tare da kallon hotunanmu. Duk kowacce tambaya take wai ina muka haɗu da shi. Nace shi ya kawo kanshi har lungunmu, inda ya ganni. Maimuna tace gashi daga gani yana mugun sonki, ko ina a hoton yana kallonki. Wayata dake hannun Jamila tana tura min hotunanmu a wayar Mariya ta soma ringin. Jamila tace ga ango yana kira, na amsa duk suka bi ni da ido, na ɗaga da sallama. Yace ina ƙofar gida. Nace sai ka ƙaro gaba gida na ƙarshe a lungun can zamu kwana. Yace "To ki fito ki tare ni." Nace to. yace "Kada ki kashe wayar fa." Nace to. Na saka takalmi ina ce musu bari in dawo, sai naji kusan duk sun amsa da to amarya. Ina fita yana ƙarasowa ya aje ledar hannunsa, ya zauna a bakin dakalin. Na ƙarasa na zauna, na gaida shi cikin girmamawa kamar yadda na saba. Ya amsa sanan yace "Faɗa min wane saƙo kika Turi min?" Na sunkuyar da kai cewa na yi akwai matsala. Na ɗago na dube shi, Yaya ka faɗa min waye kai?" Yace "Me kike son sani?" Kai ɗan Ali Baita ne? Na jeho masa tambaya. "Me yasa kika tambaye ni?" Na juya masa baya, ka bani amsa kawai In shine me zai faru?" Ya sake jeho min tambaya. Ban yi soyayya da ɗan Alhaji Baita ba, da Aliyu na yi soyayya talaka mai tsaron kantin Zeena plaza.
🖊ï¸ðŸ–Šï¸ðŸ–Šï¸
*HAMSHAƘIYAR UWA🧕ðŸ»*
*NA*
*HALIMA ABDULLAHI K/ MASHI*
_PAID BOOK_
_Kuɗin karatu ₦600_
_Account number 0700549935 Halima Abdullahi Access Bank a turo shaidar biya ta wannan number 08140004302 ko katin Mtn_
_Phone 08140004302_
*DOKA*
_Ban amince wani ya É—ora littafin nan a wani Social media ba,ko a maida mini shi Audio ba tare da iznina ba yin haka daidai yake da fuskantar fushin hukuma. A kiyaye_
*Masu son a Tallata masu hajarsu suyi magana ta wannan number 09068032427*
*Page 18*