Sashe 29
Hamshakiyar Uwa Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ya hura min ƙwayar idanu tare da faɗin "Kamar kina min kallon tuhuma Baby." Nace Me zaka yi wanda zai sa in tuhume ka? Kai mijina ne mai gaskiya da riƙon amana,ga ibada kyauta da sadaka gidan ku ya yi fice, gashi ka tsare kanka daga sharholiyar zamani ta bin matan banza da yawancin mazaje ke yi,ko tunanin bayansu basa yi,. Ina matuƙar tausayin ahalin mazinata, domin sai uba ya ja a yi wa 'yarsa a banza ba tare da hakkinta ba .Ko miji ya ja wa matar sa ɗa ya jawa uwarsa...Hannu ya sa ya rufe min baki tare da faɗin "Ki taya su addu'a Allah ya shirye su. Ni yaushe ma na samu lokacin matata har bare in tsaya neman wasu matan. Ina da kamar ki wace damuwa gare ni. Baby komai na ke so kina min yadda ki ke sakin jiki da ni a gurin kwanciya ban taɓa samun haka ba. Kina kore duk wata sha'awa tawa. A zuciya ta nace kaji ƙarya. Ko a wannan daren na yi bincike a wayarsa, kuma sunyi alƙawari da wata za su haɗu ranar Lahadi da ƙarfe sha biyu.
....
A Cikin kwanaki kullum ina yin tunani aka yadda ya kamata in daƙile wannan haduwar ta sa da karuwar nan, kwata kwata bana son yasan nasan abinda ya ke aikatawa domin ɓoye min ɗin ma alfarma ce, in har namiji ya na aikata wani laifi ya ɓoye miki alfarma ce kar ki sake ki binciko, sannan in har kin gano to karki nuna masa domin zai yi borin kunya ne ya nuna miki bai damu ba, sannan zaman lafiya ya ƙare. Zuciya ta ce ta yi min wannan karatun don haka sai na ƙara yin ƙoƙarin daurewa. Kuma na fahimci cewa kowane iyali suna da tasu matsalar wasu rigingimu da munafirci, kamar ahalin su Abbanmu kenan. Wasu 'yan shaye shaye suke da su a cikin nasu ahalin.Wasu kuma ɓarayi. To sukuma nan manemin mata Allah ya basu gane nima ya zama cikin ƙaddara ta. In na tada bala'i na tafi bansan dawa zan haɗu ba a gaba.
Ranar asabar na sake bincika wayar sunyi magana cewa zai aiko a ɗauke ta tsakanin shabiyu zuwa ƙarfe ɗaya.
Na tashi zaune na ƙare mishi kallo cikin dare yana bacci nace zan gwada wata dabara Allah ka tsaya min.
Na riƙe cikina ina ta juyi ina ɗan kuka ina faɗin wayyo cikina. Ya farka a gigice ya kamani yana tambaya ta, da kyar nace cikina ne ke ciwo. Ya tashi ganin yadda ciwon ke ƙara tsananta ya kira wayar Hajiya ya faɗa mata. Tace "Subhanallah! Ka zo ka amshi ko plagin ka bata kafin asbashi a kira likita." To haka dai aka kwana a kaina ina birgima,yau da ga salla wannan zaman na safe na gurin Hajiya ranar bai samu ba, da zai tafi salla sai na yi laf kamar bacci ya sace ni. Yana fita na tashi na yi salla na dawo na ɗora ina juya juya har na faɗo daga kan gadon. Shi kuma bayan sun gaisa da Hajiya ta tambayi jikina yace sai gefin asbahi sannan bacci ya ɗan sace ni, yace shi kanshi bacci ya ke ji yanzu idanunshi sai raɗaɗi suke yi. Hajiya tace "Ka kira likitan ko?" Yace munyi waya yana hanyar zuwa nan ɗin,. Hajiya tace "Allah ya sawaƙa kuma ba ciki gareta ba ko?" Shamaki yace gaskiya dai bansani ba, amma a wannan sati tayi al'adar ta. Hajiya tace To" bari likitan ya ƙaraso muji."
Kiran likitan ya shigo,Shamaki ya ce gashi nan ma bari in shigo da shi. Har Hajiya suka nufin ɗakin Shamaki ni kuwa lokacin ina tsaka da kukan baƙin ciki jin motsin su ya sa na dafe ciki na shiga juyi. Shamaki ne ya rugo da gudu yana faɗin "Subhanallah faɗowa ki kayi haƙa Baby! Ya ɗauke ni ya mayar kan gadon yana min sannu, sai naji muryar Hajiya itama tana min sannu cikin magana da ƙyar nace a kai ni gurin Ummanmu zan mutu ne. Hajiya tace "Inda mutuwar ce 'yannan wane ke ki furta ta,zafin ciwon ne Allah ya baƙi lafiya likita ka duba ta sosai ni bari in koma Allah ya sawaƙa."
Duk inda likita ya latsa da hannu a cikina sai in saki ƙara, yace a sani a mota kawai muje Asibiti a yi hoto domin a gano ina matsalar ta ke, ya kira Hajiya ya faɗa mata, sannan ya canza kaya ni kuma ya zira min hijabi akan kayan bacci ya ɗakko ni kamar ya ɗau jinjiri muka fita mota.
Iya gwaje gwajen likita bai iya go komai a cikina ba, don haka sai ya gayyaci wani likita wanda ya yi shura a fanni cikin kafin yazo aka min allurai dan rage raÉ—aÉ—i sannan aka samin ruwa da allurar saka bacci. Bacci ya yi gaba da ni wanda har likitan ya zo suka yi hoto an gane wane ina da sanyin mara da kuma tsakuwa wanda ake ganin tsakuwar ce ma ta soma taruwa, za a bani maganin ta taru guri guda in ya so sai a yimin aiki. In kuma anga yiwuwar ba sai anyi aiki ba sai a bani magani ta narke.
Ni dai ban farka ba tunda a kwai bashin bacci sai kusan ƙarfe biyu, ina ganin Asibiti na tuno komai da komai zan motsa sai ƙaran wayar shi ce ta tashe ni, bai san na farka ba yana magana can ƙasa ƙasa daga can kusa da bakin ƙofa da yake kunne na kamar na maciji ya ke ba dai jiyo magana ba, naji yana faɗin. "Na faɗa miki cewa na miki magana ta Whatsapp ki duba mana mata ta bata da lafiya yanzu haka muna Asibiti in na samu lokaci za mu sake saka rana don haka karki sake kiran wayata.
Alhamdulillah na furta a hankali, na wahala kuma na yi ƙarya,amma na yi nasarar hana aikata babban laifi wato zina. Ya dawo ina miƙa tare da salati, yace "Baby kin farka sannu ya jikin.?" Ya kama hannu na yana murzawa. Na zuba mishi idanu, kishi da son shi suka sake tirniƙe ni. Nima na matsa hannun shi a hankali nace dan Allah kana so na sosai? Ya tsuguno ya ɗora karan hanci shi a kan nawa, yace "Baby me yasa ki ke ta kokwanto?" Ka sake tabbatar min, na faɗa hawaye suna zubowa daga cikin idanuna. Yace "Baby ina matuƙar son ki." Na sa tafin hannuwa na guda biyu na ɗora akan kumatunsa, nace Ni kuma nayi maka alƙawarin zan yi maka duk wata biyayya zan rufa maka duk wani asiri zan baka duk wata kariya wadda nake da iko.
Ya ɗanyi shiru, can ya yi murmushi "Baby za dai ki min biyayya amma rufin asiri ko kariya ai nine zan miki wannan amma ki taya ni da addu'ao nan da ki ka saba." Nace to ba damuwa muje gida tunda na samu sauƙi, gashi baka je kasuwa ba kai sam yau. Yace "Ya zanje kasuwa mata ta tana cikin mawuyacin hali." Nace na gode da kulawa. Yace bari inje in yiwa likitan magana.
An sallame ni da tarin magunguna,muna isa gida Hajiya ta min sannu su Juma kuwa har É—aki. Ranar dai Shamaki bai fita kasuwa ba,kuma banga Hajiya ta damu da rashin fitarsa ba, yana gurinta kaÉ—an kaÉ—an ya zo ya duba ni.
Kwana uku bayan wannan diramar ina zaune gaban Hajiya ina yi mata tausa a ƙafa, tace "Me yasa baki sanar da iyayenki rashin lafiyar ki ba? Irin wannan ciwo da ki ka yi mai azaba zai iya kai mutum lahira." nace na ga ana kula dani sosai kuma kar in tada musu hankali shiyasa. Tace "Kinyi tunani mai kyau, Allah ya ƙara lafiya, ta ci gaba Shamaki ya na sonki, ki yi amfani da hakan ki taimaki rayuwarsa." Kalaman suka ɗaure min kai, me hakan ke nufi? Na tambayi zuciya ta. Hajiya ce kawai zata iya wayar min da kai, don haka sai na ce. Tayaya zan iya amfani da haka in taimake shi? Kuma wane irin taimako? Tace "Babu buƙatar dogon bayani ni dai zan ci gaba da kula da yiwuwar hakan." Nace to Allah ya bani iko, ni zanyi koma menene matsawar hakan zai taimake shi. Hajiya tace kin kyauta
Juma ta shigo ta zauna tace ina son magana da ke ne Hajiya.
A duk lokacin da Juma ta yi irin wannan furucin Hajiya ta san tana buƙatar su keɓe ne. Dan haka sai ta ce, " Rabi'atu ba mu guri mu yi magana. Na tashi na nufi gurin yara. Azima tana zaune kamar kullum da littafin a hannun ta. Ban damu da ƙin amsa sallama ta ba,domin nasani ta saba. Yaran suka nufo ni su duka suna tambaya ko zanyi musu tatsuniya. Nace su bari sai gobe Alhamis tunda babu islamiyya in mun gama karatu sai in yi musu. Juma tayi sallama muka amsa tace "Azima Hajiya tana kira." Sai da ta ja dogon tsaki sannan tace faɗa mata ina zuwa. Juma ta jima da tafiya kafin Azima ta sake yin tsaki ta yashi tana ƙunƙunai. Nabi bayanta da kallo ina mamakin wani faɗi da naga ta yi. Ji nayi duk na tsargu, na tashi na nufi ɗakina,
....
A Cikin kwanaki kullum ina yin tunani aka yadda ya kamata in daƙile wannan haduwar ta sa da karuwar nan, kwata kwata bana son yasan nasan abinda ya ke aikatawa domin ɓoye min ɗin ma alfarma ce, in har namiji ya na aikata wani laifi ya ɓoye miki alfarma ce kar ki sake ki binciko, sannan in har kin gano to karki nuna masa domin zai yi borin kunya ne ya nuna miki bai damu ba, sannan zaman lafiya ya ƙare. Zuciya ta ce ta yi min wannan karatun don haka sai na ƙara yin ƙoƙarin daurewa. Kuma na fahimci cewa kowane iyali suna da tasu matsalar wasu rigingimu da munafirci, kamar ahalin su Abbanmu kenan. Wasu 'yan shaye shaye suke da su a cikin nasu ahalin.Wasu kuma ɓarayi. To sukuma nan manemin mata Allah ya basu gane nima ya zama cikin ƙaddara ta. In na tada bala'i na tafi bansan dawa zan haɗu ba a gaba.
Ranar asabar na sake bincika wayar sunyi magana cewa zai aiko a ɗauke ta tsakanin shabiyu zuwa ƙarfe ɗaya.
Na tashi zaune na ƙare mishi kallo cikin dare yana bacci nace zan gwada wata dabara Allah ka tsaya min.
Na riƙe cikina ina ta juyi ina ɗan kuka ina faɗin wayyo cikina. Ya farka a gigice ya kamani yana tambaya ta, da kyar nace cikina ne ke ciwo. Ya tashi ganin yadda ciwon ke ƙara tsananta ya kira wayar Hajiya ya faɗa mata. Tace "Subhanallah! Ka zo ka amshi ko plagin ka bata kafin asbashi a kira likita." To haka dai aka kwana a kaina ina birgima,yau da ga salla wannan zaman na safe na gurin Hajiya ranar bai samu ba, da zai tafi salla sai na yi laf kamar bacci ya sace ni. Yana fita na tashi na yi salla na dawo na ɗora ina juya juya har na faɗo daga kan gadon. Shi kuma bayan sun gaisa da Hajiya ta tambayi jikina yace sai gefin asbahi sannan bacci ya ɗan sace ni, yace shi kanshi bacci ya ke ji yanzu idanunshi sai raɗaɗi suke yi. Hajiya tace "Ka kira likitan ko?" Yace munyi waya yana hanyar zuwa nan ɗin,. Hajiya tace "Allah ya sawaƙa kuma ba ciki gareta ba ko?" Shamaki yace gaskiya dai bansani ba, amma a wannan sati tayi al'adar ta. Hajiya tace To" bari likitan ya ƙaraso muji."
Kiran likitan ya shigo,Shamaki ya ce gashi nan ma bari in shigo da shi. Har Hajiya suka nufin ɗakin Shamaki ni kuwa lokacin ina tsaka da kukan baƙin ciki jin motsin su ya sa na dafe ciki na shiga juyi. Shamaki ne ya rugo da gudu yana faɗin "Subhanallah faɗowa ki kayi haƙa Baby! Ya ɗauke ni ya mayar kan gadon yana min sannu, sai naji muryar Hajiya itama tana min sannu cikin magana da ƙyar nace a kai ni gurin Ummanmu zan mutu ne. Hajiya tace "Inda mutuwar ce 'yannan wane ke ki furta ta,zafin ciwon ne Allah ya baƙi lafiya likita ka duba ta sosai ni bari in koma Allah ya sawaƙa."
Duk inda likita ya latsa da hannu a cikina sai in saki ƙara, yace a sani a mota kawai muje Asibiti a yi hoto domin a gano ina matsalar ta ke, ya kira Hajiya ya faɗa mata, sannan ya canza kaya ni kuma ya zira min hijabi akan kayan bacci ya ɗakko ni kamar ya ɗau jinjiri muka fita mota.
Iya gwaje gwajen likita bai iya go komai a cikina ba, don haka sai ya gayyaci wani likita wanda ya yi shura a fanni cikin kafin yazo aka min allurai dan rage raÉ—aÉ—i sannan aka samin ruwa da allurar saka bacci. Bacci ya yi gaba da ni wanda har likitan ya zo suka yi hoto an gane wane ina da sanyin mara da kuma tsakuwa wanda ake ganin tsakuwar ce ma ta soma taruwa, za a bani maganin ta taru guri guda in ya so sai a yimin aiki. In kuma anga yiwuwar ba sai anyi aiki ba sai a bani magani ta narke.
Ni dai ban farka ba tunda a kwai bashin bacci sai kusan ƙarfe biyu, ina ganin Asibiti na tuno komai da komai zan motsa sai ƙaran wayar shi ce ta tashe ni, bai san na farka ba yana magana can ƙasa ƙasa daga can kusa da bakin ƙofa da yake kunne na kamar na maciji ya ke ba dai jiyo magana ba, naji yana faɗin. "Na faɗa miki cewa na miki magana ta Whatsapp ki duba mana mata ta bata da lafiya yanzu haka muna Asibiti in na samu lokaci za mu sake saka rana don haka karki sake kiran wayata.
Alhamdulillah na furta a hankali, na wahala kuma na yi ƙarya,amma na yi nasarar hana aikata babban laifi wato zina. Ya dawo ina miƙa tare da salati, yace "Baby kin farka sannu ya jikin.?" Ya kama hannu na yana murzawa. Na zuba mishi idanu, kishi da son shi suka sake tirniƙe ni. Nima na matsa hannun shi a hankali nace dan Allah kana so na sosai? Ya tsuguno ya ɗora karan hanci shi a kan nawa, yace "Baby me yasa ki ke ta kokwanto?" Ka sake tabbatar min, na faɗa hawaye suna zubowa daga cikin idanuna. Yace "Baby ina matuƙar son ki." Na sa tafin hannuwa na guda biyu na ɗora akan kumatunsa, nace Ni kuma nayi maka alƙawarin zan yi maka duk wata biyayya zan rufa maka duk wani asiri zan baka duk wata kariya wadda nake da iko.
Ya ɗanyi shiru, can ya yi murmushi "Baby za dai ki min biyayya amma rufin asiri ko kariya ai nine zan miki wannan amma ki taya ni da addu'ao nan da ki ka saba." Nace to ba damuwa muje gida tunda na samu sauƙi, gashi baka je kasuwa ba kai sam yau. Yace "Ya zanje kasuwa mata ta tana cikin mawuyacin hali." Nace na gode da kulawa. Yace bari inje in yiwa likitan magana.
An sallame ni da tarin magunguna,muna isa gida Hajiya ta min sannu su Juma kuwa har É—aki. Ranar dai Shamaki bai fita kasuwa ba,kuma banga Hajiya ta damu da rashin fitarsa ba, yana gurinta kaÉ—an kaÉ—an ya zo ya duba ni.
Kwana uku bayan wannan diramar ina zaune gaban Hajiya ina yi mata tausa a ƙafa, tace "Me yasa baki sanar da iyayenki rashin lafiyar ki ba? Irin wannan ciwo da ki ka yi mai azaba zai iya kai mutum lahira." nace na ga ana kula dani sosai kuma kar in tada musu hankali shiyasa. Tace "Kinyi tunani mai kyau, Allah ya ƙara lafiya, ta ci gaba Shamaki ya na sonki, ki yi amfani da hakan ki taimaki rayuwarsa." Kalaman suka ɗaure min kai, me hakan ke nufi? Na tambayi zuciya ta. Hajiya ce kawai zata iya wayar min da kai, don haka sai na ce. Tayaya zan iya amfani da haka in taimake shi? Kuma wane irin taimako? Tace "Babu buƙatar dogon bayani ni dai zan ci gaba da kula da yiwuwar hakan." Nace to Allah ya bani iko, ni zanyi koma menene matsawar hakan zai taimake shi. Hajiya tace kin kyauta
Juma ta shigo ta zauna tace ina son magana da ke ne Hajiya.
A duk lokacin da Juma ta yi irin wannan furucin Hajiya ta san tana buƙatar su keɓe ne. Dan haka sai ta ce, " Rabi'atu ba mu guri mu yi magana. Na tashi na nufi gurin yara. Azima tana zaune kamar kullum da littafin a hannun ta. Ban damu da ƙin amsa sallama ta ba,domin nasani ta saba. Yaran suka nufo ni su duka suna tambaya ko zanyi musu tatsuniya. Nace su bari sai gobe Alhamis tunda babu islamiyya in mun gama karatu sai in yi musu. Juma tayi sallama muka amsa tace "Azima Hajiya tana kira." Sai da ta ja dogon tsaki sannan tace faɗa mata ina zuwa. Juma ta jima da tafiya kafin Azima ta sake yin tsaki ta yashi tana ƙunƙunai. Nabi bayanta da kallo ina mamakin wani faɗi da naga ta yi. Ji nayi duk na tsargu, na tashi na nufi ɗakina,