Sashe 9
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ta daga ido ta kalleta ta ce "Ince sai wani satin kike da zama a kotu?"
"A a Gobe ne Innah".
"To ki gaishe da Yayar ta ki, sannan ki fa'da mata lalle ta sake taya mu da addu'a".
Har Sa'adah ta kusa kaiwa zaure Inna ta dawo da ita, ta zaunar da ita ta fa'da mata komai na mafarkin da ta yi, ta rufe da cewa "Dan haka ki nisanci Muutar.
Kunya ta kama Sa'adah amma ta daure ta ce "in Sha Allah hakan ba zata faru ba ubangiji ba zai kunyata ku ba Inna".
Sa'adah na aiki da (supreme Court) ta court road. Watan jiya Alh Mamman ya kawo mata (upper) takardar samun aiki har gida, wadda wannan na cikin abin da ya sake dagulawa Mk lissafi, domin kuwa a bakin Ahamad yà ji Sa'a ta samu aiki, duk da tafi zaman gidan Sumayya adalilin daga gandu zuwa court road ba nisa. Ya fi mata sau'kin zuwa.
A bincikensa ya gano Alh Mamman ne ya samo aikin, ya dinga jin takaici yana kallon Alh Mamman a matsayin a karambana, da ga fitowarta a makaranta sai ka nemo mata aiki? Tamkar ance masa ana bu'katar hakan, kai dattijan mazan nan wuyar sha'anine da su idan suna son Yar yarinya. Ko kunya ba ya ji, zai dage yana son Sa'adah alhalin yana da 'dan da yake sa'anta ne.
A fili Mk ya ja tsaki ya ce "zanga yadda za'ayi ka mallaketa shekaru da yawa ka kasa rabuwa da ita, tamkar ita ka'daice yarinyar mace bayan ga yanmata nan masu shekaru irin na ta".
Ya sake jan dogon tsaki yana cewa "Halima tana nan har yau a kasa ta ke da gudu zata soka, amma wannan kam a yanzu ma ba samunta zaka yi ba". sai dai a zuciyar sa ya tabbatar son gaskiya Alh Mamman ya ke yi mata, wani irin abu mai nauyi ya danne shi a zuciya, wadda shi ya damalmala masa lissafi har ya ji ba zai sami nutsuwa ba, idan ba shiryawa ya yi da ita ba, ya lura ba zai ta'ba iya jarumtar wani ya aureta alhalin yana da rai ba.
A zaure ta tarar da Baffa da Mk da kuma Mahmoud a zaune kan tabarma suna tattaunawa, sai da zuciyarta ta buga tunda ta ganshi da Mahmoud lah shakka maganar kome ya zo yi, a ranta ta dinga jinjina rashin ta ido a gurin namiji, yanzu da yake son komen ya na'de kafar wando zai nemi komenta duk yadda ya jingineta shekaru bakwai, Anya kuwa Mk yana da adalci a yanzu?
A ladabce ta ce "Baffa sannu da yammaci, zan tafi, sai wani satin Kuma".
Da wani irin farin ciki ya amsa mata da fa'din "To ki gaishe su, ki kula da kanki, Allah ya tsare".
Ta amsa da cewa "Ameen".
Ta kalli 'Karfi ta ce " Baban Dadi barka da yamma ya iyali?"
Ya amsa ta saka kai ta fice bata ko kalli inda Mk yake ba, bare ta gaishe shi ko da gaisuwar da zai raina ne.
Ran Baffa ba karamin baci ya yi da abin da ta yi ba, ta ganshi da ba'ki, ta gaishe da 'daya, ta wulakanta 'daya, idan dai da gaske bata son Mutari a yanzu menene zaisa ba zata gaishe shi ba?
"Iyah"
Baffah yasa baki ya kirata da karfi, ta dawo tana cewa "Ga ni Baffah"!
"Me yasa kika gaishe ni, Me yasa baki wuce kanki tsaye ba? Ai na yi zaton ko da rago Ki ka ganni zaki tsaya ki tambayi lafiyarsa saboda ya shiga rigata, akan idona ki yiwa Mutari wannan wulakancin? Amma ba komai ai ni kika yiwa ba shi ba, Na gode miki je ki, yi tafiyar ki".
Ta kasa tafiya, ta yi sukuri tana jin takaici na kamata, hawaye ya balle mata, Mk yana kallonta ta gefen ido, yana ganin yadda ta turo baki gaba, sai ya dinga jin wani irin tsumi na tsumashi, abubuwa masu yawa akanta suka dinga bijiro masa, ya dinga jin wani irin abu na taso masa.
A hankali, kuma cikin bacin rai ta ce "
Mutarin Baffah ina yini?"
Dariya ta kwacewa Mahmoud ya dinga kyaykatawa Baffa kuwa ya gintse tasa dariyar ya dubi Mk da ya hade girar sama da ta kasa kuma bai amsa ba, hakan da ya yi ya sake hassalo da Sa'a.
Baffah ya cije ya ce "Yanzu kuma laifinka ne ta gaisheka baka amsa ba, tunda hakane sai ka tashi ka kaita, ai bazai yiwu ka sace mata iska a banza ba, dole ka hutar da ita tsayuwar jiran mai adaidaita sahu dama kuma garin hadarine sossai".
Mahmoud ya yi maza ya ce "To Baffa bari mu kaita mu dawo, mun gode Allah ya kara girma".
Baffah ya shige gida ya barsu a zauren Sa'a ta na jin tamkar ta yi ta zunduma ihu.
Hawaye ya dinga tsere a idonta, wannan irin bada ita da Baffa ya yi? Duk wula'kancin da Mk ya mata wato Baffah bai ga laifinsa ba, daga zuwa da magana zaice ta shiga motarsa ya kaita a matsayinsa nawa din ta?
Zauciyarta ta kuntata sosai tana jin gara ta tafi da kafa a kan ta shiga motar Mk.
Har suka fita kofar gida kuka take marar sauti, Mahmoud ya bude mata gaban motar, ta cije, a hankali ya ce "a titi muke fa, sannan umarnin Baffa zaki bi, ba son ranki ba" .
"Akan me za'a tilas ni shiga motarsa,?"
Ta fa'da cikin rishin kuka.
"Yi ha'kuri ai dukkan mu umarnin Baffa zamu yi wa biyayya akan kunnen ki dai ya hukunta Mk ta hanyar mayar da shi dureban ki, adalilin amsa gaisuwar ki da bai yi ba. Kina kallon bai yi musu ba sai ke?
Hawaye ya zubo mata ta ce "Ni na yafe masa zan tafi da kaina".
Mahmoud ya ce "Ai tunda Kika bari Baffa ya shige cikin gida dolen Mukhtar ya miki direba kar ki yadda ki sab'awa mahaifin ki adalilin wani Mukhtar".
Take Sa'adah ta gane gaskiyar Mahmoud ne, tunda rashin gaisuwar da bata yi bane ya janyo mata wannan hukuncin mai kama da saukar aradu.
Maimakon ta shiga gaba inda Mahmoud ya bude mata sai kawai ta bude baya ta shiga.
Da azama Mahmoud ya isa setin direba Mk ya juya musu baya tamkar baya wurin hakan da ya yi ya sake tunzura Sa'a tun fil'azal ta tsani a nuna mata rashin kulawa.
Mukullin hannun Mk Mahmoud ya karba, a hankali ya ce "shiga baya mu je".
Ba musu Mk ya bude bayan motar ya zauna, Yana rufewa Mahmoud ya ja motar.
Zuciyar Iyah tamkar ta fa'do kasa dan tsananin ba'kin ciki mussaman da ta tuno irin addu'ar da dinga yi, tun bayan da ya auri Farida na kar Allah ya sake ha'data ko da zaman mota ne da Mukhtar balle kuma zaman aure, sai gashi karon farko da zaman motar aka sake ha'dasu, zuciyar ta dinga bugawa fiye da kima tana fargabar menene zai biyo bayan wannan zaman?
Ta dinga jin takaicin kin shiga gaban motar, da ta shiga ai tasan shine dole zai ja motar, Kuma dolensa ya zauna iya kujerarsa sannan ya kula da tukinsa.
Amma yanzu ya babbake har gefen jikinsu na gogar juna, gilashin motar irin na munafunci ne wato tint, ya matseta sosai tamkar su hudu ne a bayan motar.
Ba'kin ciki ya isheta sai kawai ta fashe da matsanancin kuka mai sauti sosai, Mk ya yi tamkar bai ji ba, yayin da Mahmoud ya juyo da sauri tunda a tsaye suke traffic ya tsayar da su.
"Menene kike yi haka Sa'adatu?"
Zuciyarsa ta buga ganin yadda Rabin jikin Mk na jikinta, wani irin abu ya tsayawa Mahmoud da bai yi zaton zai ji ba, ya juya da sauri ya dauke fuskarsa yana ambaton innalillahi.
Kukanta ya dinga tsuma Mk ya dinga jin tamkar ya danneta ko ya samu sau'kin halin da yake ciki.
Ya lura fishi na fitar hankali take yi da shi, idan ya ce zai lalla'ba ta to ya kai shekara yana fama adalilin taurin kai irin nata.
"A a Gobe ne Innah".
"To ki gaishe da Yayar ta ki, sannan ki fa'da mata lalle ta sake taya mu da addu'a".
Har Sa'adah ta kusa kaiwa zaure Inna ta dawo da ita, ta zaunar da ita ta fa'da mata komai na mafarkin da ta yi, ta rufe da cewa "Dan haka ki nisanci Muutar.
Kunya ta kama Sa'adah amma ta daure ta ce "in Sha Allah hakan ba zata faru ba ubangiji ba zai kunyata ku ba Inna".
Sa'adah na aiki da (supreme Court) ta court road. Watan jiya Alh Mamman ya kawo mata (upper) takardar samun aiki har gida, wadda wannan na cikin abin da ya sake dagulawa Mk lissafi, domin kuwa a bakin Ahamad yà ji Sa'a ta samu aiki, duk da tafi zaman gidan Sumayya adalilin daga gandu zuwa court road ba nisa. Ya fi mata sau'kin zuwa.
A bincikensa ya gano Alh Mamman ne ya samo aikin, ya dinga jin takaici yana kallon Alh Mamman a matsayin a karambana, da ga fitowarta a makaranta sai ka nemo mata aiki? Tamkar ance masa ana bu'katar hakan, kai dattijan mazan nan wuyar sha'anine da su idan suna son Yar yarinya. Ko kunya ba ya ji, zai dage yana son Sa'adah alhalin yana da 'dan da yake sa'anta ne.
A fili Mk ya ja tsaki ya ce "zanga yadda za'ayi ka mallaketa shekaru da yawa ka kasa rabuwa da ita, tamkar ita ka'daice yarinyar mace bayan ga yanmata nan masu shekaru irin na ta".
Ya sake jan dogon tsaki yana cewa "Halima tana nan har yau a kasa ta ke da gudu zata soka, amma wannan kam a yanzu ma ba samunta zaka yi ba". sai dai a zuciyar sa ya tabbatar son gaskiya Alh Mamman ya ke yi mata, wani irin abu mai nauyi ya danne shi a zuciya, wadda shi ya damalmala masa lissafi har ya ji ba zai sami nutsuwa ba, idan ba shiryawa ya yi da ita ba, ya lura ba zai ta'ba iya jarumtar wani ya aureta alhalin yana da rai ba.
A zaure ta tarar da Baffa da Mk da kuma Mahmoud a zaune kan tabarma suna tattaunawa, sai da zuciyarta ta buga tunda ta ganshi da Mahmoud lah shakka maganar kome ya zo yi, a ranta ta dinga jinjina rashin ta ido a gurin namiji, yanzu da yake son komen ya na'de kafar wando zai nemi komenta duk yadda ya jingineta shekaru bakwai, Anya kuwa Mk yana da adalci a yanzu?
A ladabce ta ce "Baffa sannu da yammaci, zan tafi, sai wani satin Kuma".
Da wani irin farin ciki ya amsa mata da fa'din "To ki gaishe su, ki kula da kanki, Allah ya tsare".
Ta amsa da cewa "Ameen".
Ta kalli 'Karfi ta ce " Baban Dadi barka da yamma ya iyali?"
Ya amsa ta saka kai ta fice bata ko kalli inda Mk yake ba, bare ta gaishe shi ko da gaisuwar da zai raina ne.
Ran Baffa ba karamin baci ya yi da abin da ta yi ba, ta ganshi da ba'ki, ta gaishe da 'daya, ta wulakanta 'daya, idan dai da gaske bata son Mutari a yanzu menene zaisa ba zata gaishe shi ba?
"Iyah"
Baffah yasa baki ya kirata da karfi, ta dawo tana cewa "Ga ni Baffah"!
"Me yasa kika gaishe ni, Me yasa baki wuce kanki tsaye ba? Ai na yi zaton ko da rago Ki ka ganni zaki tsaya ki tambayi lafiyarsa saboda ya shiga rigata, akan idona ki yiwa Mutari wannan wulakancin? Amma ba komai ai ni kika yiwa ba shi ba, Na gode miki je ki, yi tafiyar ki".
Ta kasa tafiya, ta yi sukuri tana jin takaici na kamata, hawaye ya balle mata, Mk yana kallonta ta gefen ido, yana ganin yadda ta turo baki gaba, sai ya dinga jin wani irin tsumi na tsumashi, abubuwa masu yawa akanta suka dinga bijiro masa, ya dinga jin wani irin abu na taso masa.
A hankali, kuma cikin bacin rai ta ce "
Mutarin Baffah ina yini?"
Dariya ta kwacewa Mahmoud ya dinga kyaykatawa Baffa kuwa ya gintse tasa dariyar ya dubi Mk da ya hade girar sama da ta kasa kuma bai amsa ba, hakan da ya yi ya sake hassalo da Sa'a.
Baffah ya cije ya ce "Yanzu kuma laifinka ne ta gaisheka baka amsa ba, tunda hakane sai ka tashi ka kaita, ai bazai yiwu ka sace mata iska a banza ba, dole ka hutar da ita tsayuwar jiran mai adaidaita sahu dama kuma garin hadarine sossai".
Mahmoud ya yi maza ya ce "To Baffa bari mu kaita mu dawo, mun gode Allah ya kara girma".
Baffah ya shige gida ya barsu a zauren Sa'a ta na jin tamkar ta yi ta zunduma ihu.
Hawaye ya dinga tsere a idonta, wannan irin bada ita da Baffa ya yi? Duk wula'kancin da Mk ya mata wato Baffah bai ga laifinsa ba, daga zuwa da magana zaice ta shiga motarsa ya kaita a matsayinsa nawa din ta?
Zauciyarta ta kuntata sosai tana jin gara ta tafi da kafa a kan ta shiga motar Mk.
Har suka fita kofar gida kuka take marar sauti, Mahmoud ya bude mata gaban motar, ta cije, a hankali ya ce "a titi muke fa, sannan umarnin Baffa zaki bi, ba son ranki ba" .
"Akan me za'a tilas ni shiga motarsa,?"
Ta fa'da cikin rishin kuka.
"Yi ha'kuri ai dukkan mu umarnin Baffa zamu yi wa biyayya akan kunnen ki dai ya hukunta Mk ta hanyar mayar da shi dureban ki, adalilin amsa gaisuwar ki da bai yi ba. Kina kallon bai yi musu ba sai ke?
Hawaye ya zubo mata ta ce "Ni na yafe masa zan tafi da kaina".
Mahmoud ya ce "Ai tunda Kika bari Baffa ya shige cikin gida dolen Mukhtar ya miki direba kar ki yadda ki sab'awa mahaifin ki adalilin wani Mukhtar".
Take Sa'adah ta gane gaskiyar Mahmoud ne, tunda rashin gaisuwar da bata yi bane ya janyo mata wannan hukuncin mai kama da saukar aradu.
Maimakon ta shiga gaba inda Mahmoud ya bude mata sai kawai ta bude baya ta shiga.
Da azama Mahmoud ya isa setin direba Mk ya juya musu baya tamkar baya wurin hakan da ya yi ya sake tunzura Sa'a tun fil'azal ta tsani a nuna mata rashin kulawa.
Mukullin hannun Mk Mahmoud ya karba, a hankali ya ce "shiga baya mu je".
Ba musu Mk ya bude bayan motar ya zauna, Yana rufewa Mahmoud ya ja motar.
Zuciyar Iyah tamkar ta fa'do kasa dan tsananin ba'kin ciki mussaman da ta tuno irin addu'ar da dinga yi, tun bayan da ya auri Farida na kar Allah ya sake ha'data ko da zaman mota ne da Mukhtar balle kuma zaman aure, sai gashi karon farko da zaman motar aka sake ha'dasu, zuciyar ta dinga bugawa fiye da kima tana fargabar menene zai biyo bayan wannan zaman?
Ta dinga jin takaicin kin shiga gaban motar, da ta shiga ai tasan shine dole zai ja motar, Kuma dolensa ya zauna iya kujerarsa sannan ya kula da tukinsa.
Amma yanzu ya babbake har gefen jikinsu na gogar juna, gilashin motar irin na munafunci ne wato tint, ya matseta sosai tamkar su hudu ne a bayan motar.
Ba'kin ciki ya isheta sai kawai ta fashe da matsanancin kuka mai sauti sosai, Mk ya yi tamkar bai ji ba, yayin da Mahmoud ya juyo da sauri tunda a tsaye suke traffic ya tsayar da su.
"Menene kike yi haka Sa'adatu?"
Zuciyarsa ta buga ganin yadda Rabin jikin Mk na jikinta, wani irin abu ya tsayawa Mahmoud da bai yi zaton zai ji ba, ya juya da sauri ya dauke fuskarsa yana ambaton innalillahi.
Kukanta ya dinga tsuma Mk ya dinga jin tamkar ya danneta ko ya samu sau'kin halin da yake ciki.
Ya lura fishi na fitar hankali take yi da shi, idan ya ce zai lalla'ba ta to ya kai shekara yana fama adalilin taurin kai irin nata.