Sashe 15
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Alhaji ya ce "Ashha Mahmuda ai ba umarninsa zaka bi ba, ni zaka jira na baka damar yin hakan, maida bulalar ka dawo ka ji mai zance muku".
'Karfi ya fita, sai da ya ci dariyarsa mai isarsa ko banza ya rage zafin dukan da Mk ya yi wa zuciyar sa tunda amincin da ke tsakanin su ne ya haramta masa samun abin da yake so, da ya zurfafa tunani sai ya gane abotarsu ta yi karfin da zabin zuciyoyinsu ya zama iri daya. Duk da idan anbashi gida da mota akan a bashi Farida ba zai karba ba, kyan fuskarta da farinta bai zama abin burgewa a gunsa ba.
Da alhini a fuskar sa ya koma falo ya gurfana a gaban Baba yana cewa "Ina rokawa Abokina afuwarka Baba, ni shaida ne akan yadda Mukhtar ya ke girmama lamarin ka".
Dattijon ya miskuta ya ce " aminci na da mahaifin wannan yaron ya zarta karfin naku zumuncin domin ku da hankalin ku, kuka hadu amma ga shi nan kun zama tamkar cikinku guda!
Ni kuwa tsakanin mu abota ne tun bamu wuce shekaru bakwai ba, da aka kaimu gabas almajiranci har zuwa yau din nan".
Ya yi tari ya cigaba da cewa "saboda giraman abotarmu iyayen mu sai da suka zama tamkar shakikai ne duk da ba garinmu daya ba,shi daga Bichi, Ni kuma daga Wudil. A lokacin da Kabiru zai auro uwarka Rabi, mahaifina ne ya zo ya karbar masa, duk da ga kannen mahaifinsa nan hakan ya faru ne bisa amincewar mahaifin nasa da yan'uwansa. Ka san dai kaine dansa namiji na farko amma baisa sunan mahaifinsa ba, sai ya saka sunan yayana da ya fa'da a ruwa ya rasu a shekarar".
Ya yi shiru yana goge hawayen da ya kasa maida su, dukkan jikin Mk da 'Karfi ya yi sanyi, da kyar 'Karfi ya ce "Sannu Baba sai a ha'kuri!"
Ya saki ajiyar zuciya mai nauyi fiye da ta farko ya zarce da cewa "A bayan mun yi aure har mun haife ku na samu matsala da Zuwaira na yi fishin zuciya na saketa, na yi rantsuwar na gama zama da ita.
Bana mantawa dawowar mahaifinka daga Bichi ya samu labarin rabuwarmu a bakin yara, da ya juya Ashe Wudil ya tafi a yammacin, wajen karfe takwas na dare sai gashi ya dawo da ita. Washagari na tashi da azumin kaffara domin bazan iya kunyata Kabiru ba, ko na nuna masa bai isa ya yi hukunci a gidana ba.
Har yau din nan ban sake tada maganar ba sai yanzu da nake baku labarin, amma kai sai ka nuna mu iyayenka bamu isa ka mana alfarmar cigaba da zaama da matarka bare kuma wannan abokin naka".
Ya ja hankici ya goge fuskar sa ya ce "Har Kabiru ya kwanta dama bashi da aljihun kansa, haka nima bani da nawa, koman mu daya ne, Ina da ikon zartar da hukunci a gidansa haka nima yake da cikakken iko, shiyasa na tsorata ainun hankalina yake tashi idan na kalli al'amarin da ka yi mini, na baka umarni, ka kafe ka kasa yi mini alfarma, sai nake ganin da mahaifinka yana da rai da ka ga 'kwanjina. Amma tunda ni ka'dai na saura muku sai na biku da yadda kuke so tunda ubangiji ya nuna mini wannan zamanin da ya zama iyaye sun koma agwagi."
Mk ya ce "Ka yi hakuri, ka kara hakuri Baba"
Ya nisa ya ce "na ha'kura amma ka sani ni ba zan iya zuwa wajen Malam Basiru ba, bani da wannan kwarin guiwar, domin har yau din nan girmama ni yake tamkar shakikin yayansa ba kuma dan kowa yake mini hakan ba, illah dan kai domin ni ban san shi ba, sai adalilinka"
Hankalin Mk ya sake tashi ya ce " Duk cikin Kano bani da wadda ya fika Baba! Idan kuwa ka ha'kura to kaine mai karba mini aure a ko ina".
Alhaji ya ce " ka fadi Gaskiya! sai dai na san daddako irin na Malam Basiru da irin yadda ya girmama lamarinka zai iya tirsasa yarinyar nan ko bata so ya dawo maka da ita dan soyayyar da yake yi maka. Ni kuma na ta'ba fa'da muku kai da ita daya kuke a gurina nine alkalinku, alkalanci na gaskiya zanyi a tsakanin ku.
Zan je na nemar maka aurenta kadai, idan na ji a bakin yarinyar da amincewarta zan nema maka aurenta".
'Karfi ya fita, sai da ya ci dariyarsa mai isarsa ko banza ya rage zafin dukan da Mk ya yi wa zuciyar sa tunda amincin da ke tsakanin su ne ya haramta masa samun abin da yake so, da ya zurfafa tunani sai ya gane abotarsu ta yi karfin da zabin zuciyoyinsu ya zama iri daya. Duk da idan anbashi gida da mota akan a bashi Farida ba zai karba ba, kyan fuskarta da farinta bai zama abin burgewa a gunsa ba.
Da alhini a fuskar sa ya koma falo ya gurfana a gaban Baba yana cewa "Ina rokawa Abokina afuwarka Baba, ni shaida ne akan yadda Mukhtar ya ke girmama lamarin ka".
Dattijon ya miskuta ya ce " aminci na da mahaifin wannan yaron ya zarta karfin naku zumuncin domin ku da hankalin ku, kuka hadu amma ga shi nan kun zama tamkar cikinku guda!
Ni kuwa tsakanin mu abota ne tun bamu wuce shekaru bakwai ba, da aka kaimu gabas almajiranci har zuwa yau din nan".
Ya yi tari ya cigaba da cewa "saboda giraman abotarmu iyayen mu sai da suka zama tamkar shakikai ne duk da ba garinmu daya ba,shi daga Bichi, Ni kuma daga Wudil. A lokacin da Kabiru zai auro uwarka Rabi, mahaifina ne ya zo ya karbar masa, duk da ga kannen mahaifinsa nan hakan ya faru ne bisa amincewar mahaifin nasa da yan'uwansa. Ka san dai kaine dansa namiji na farko amma baisa sunan mahaifinsa ba, sai ya saka sunan yayana da ya fa'da a ruwa ya rasu a shekarar".
Ya yi shiru yana goge hawayen da ya kasa maida su, dukkan jikin Mk da 'Karfi ya yi sanyi, da kyar 'Karfi ya ce "Sannu Baba sai a ha'kuri!"
Ya saki ajiyar zuciya mai nauyi fiye da ta farko ya zarce da cewa "A bayan mun yi aure har mun haife ku na samu matsala da Zuwaira na yi fishin zuciya na saketa, na yi rantsuwar na gama zama da ita.
Bana mantawa dawowar mahaifinka daga Bichi ya samu labarin rabuwarmu a bakin yara, da ya juya Ashe Wudil ya tafi a yammacin, wajen karfe takwas na dare sai gashi ya dawo da ita. Washagari na tashi da azumin kaffara domin bazan iya kunyata Kabiru ba, ko na nuna masa bai isa ya yi hukunci a gidana ba.
Har yau din nan ban sake tada maganar ba sai yanzu da nake baku labarin, amma kai sai ka nuna mu iyayenka bamu isa ka mana alfarmar cigaba da zaama da matarka bare kuma wannan abokin naka".
Ya ja hankici ya goge fuskar sa ya ce "Har Kabiru ya kwanta dama bashi da aljihun kansa, haka nima bani da nawa, koman mu daya ne, Ina da ikon zartar da hukunci a gidansa haka nima yake da cikakken iko, shiyasa na tsorata ainun hankalina yake tashi idan na kalli al'amarin da ka yi mini, na baka umarni, ka kafe ka kasa yi mini alfarma, sai nake ganin da mahaifinka yana da rai da ka ga 'kwanjina. Amma tunda ni ka'dai na saura muku sai na biku da yadda kuke so tunda ubangiji ya nuna mini wannan zamanin da ya zama iyaye sun koma agwagi."
Mk ya ce "Ka yi hakuri, ka kara hakuri Baba"
Ya nisa ya ce "na ha'kura amma ka sani ni ba zan iya zuwa wajen Malam Basiru ba, bani da wannan kwarin guiwar, domin har yau din nan girmama ni yake tamkar shakikin yayansa ba kuma dan kowa yake mini hakan ba, illah dan kai domin ni ban san shi ba, sai adalilinka"
Hankalin Mk ya sake tashi ya ce " Duk cikin Kano bani da wadda ya fika Baba! Idan kuwa ka ha'kura to kaine mai karba mini aure a ko ina".
Alhaji ya ce " ka fadi Gaskiya! sai dai na san daddako irin na Malam Basiru da irin yadda ya girmama lamarinka zai iya tirsasa yarinyar nan ko bata so ya dawo maka da ita dan soyayyar da yake yi maka. Ni kuma na ta'ba fa'da muku kai da ita daya kuke a gurina nine alkalinku, alkalanci na gaskiya zanyi a tsakanin ku.
Zan je na nemar maka aurenta kadai, idan na ji a bakin yarinyar da amincewarta zan nema maka aurenta".