Sashe 24
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Wani irin abu ya soki Mk tunda ga kan kansa har kan yantsunsa . Ya dinga jin kansa na yi masa nauyi, ganinsa ya koma dususu, jiri ya fara katantanwa da shi.
Cikin hikimar ubangiji sai kawai ya zauna dabas angurin, farin yadinsa na tissue original din, ya debi 'kura da ciyayi amma baima sani ba.
Yana zaune sai zufa ke karyo masa, take kuma hakoransa suka dinga kadawa tabbacin zazzabi ya kawo gudunmawa a tashin hankalin da yake ciki.
Da kyar ya ciro wayarsa ya mika mata ya ce "Taimaka ki lalubo mini Abbas".
Jikinta a matu'kar sanyaye har bari take yi saboda halin da yau ta ga Mk a ciki ya matu'kar kidima ta.
Bugu daya Abbas ya dauka. Cikin karfin hali Mk ya ce taimake ni ka zo ka dauke ni, ina nan gandu gidan nan na layin Madugu, ba zan iya tuki bane".
Ya kashe wayar ya kalleta idonsa ya ka'da sosai ya ce "kin manta duk rayuwar da kika yi ta jin da'di a hannuna, kin manta alheri na, kin manta duk kalolin soyayyar da nake gwada miki, kin dora kuskurena akan dukkan wadannan abubuawan".
Ta kasa magana, ya sake kallon ta soasai fuskarsa duk gumi tamkar ya yi alwala ya ce "ki manta dukkan dadin da nake raba dare ina jiyar da ke, kin ri'ke sharri na guda daya. Har yau din nan ban ji a jikina na zalunce ki ba, na san dai babban laifi na auren da na yi ne, aure kuwa ko muna tare idan bu'katar yinsa ta zo ba zaluntarki na yi ba. Amma duk da hakan na yi ta baki ha'kuri, na fada miki kaddara ta ce auren nan da na yi. Amma ubangiji shine shaidata akan ba abin da ya ragu na daga son da nake miki, bana jin kuma a cikin wannan duniyar akwai abin da zan so ya zarta ki".
Ya nisa ya ce "Amma duk kin yi fatali da komai, kin dage sai kin yi ramuwar gayya. Abin da baki sani ba, shine ba ni da karfin guiwar juriya akan kishin ki, amma tunda kin dage shikenan, kawai ina jiye miki fargar jaji ne, ina jiye miki ki maida 'danki maraya. Shiga gida na gode sosai".
Ya yi shiru, zufa na sake karyo masa ta ko ina.
Kafin ta yi magana Abbas ya iso a adaidaita sahu.
Ya gaisheta, tare da tambayar ahalin gidansu.
Mk ya mika masa hannu, shikuma ya mikar da shi.
Suka doshi mota ba tare da Mk ya sake cewa komai ba.
Abbas ya dinga jin tausayin wadannan masoya, a ransa ya dinga musu addu'ar samun daidaito ko hankalinsu ya kwanta.
Kwanan Mk biyu a kwance Farida na jinyarsa domin a wnanan karon har ruwa aka kara masa, a gida.
Mahmoud ya damu sosai ya sake komawa wurin Sa'a Amma ta kafe ita fa ta riga ta ha'kura da Mk.
Haka da Baffa ya tambayeta ta ce ita kam bata sonsa, abin ya farantawa Inna rai, ba irin kabalin da Baffa bai yi ba ta ce ita kam ta riga da ta shafe babinsa. Lamarin da ya farantawa Inna rai ba ka'dan ba.
Da ta ga da gaske Baffa zai mata fin karfi ta shirya suka tafi Gogel ita da Sumayya, ta kai korafi wurin Yayan Baffah da ya ce a Gogel din za'a daura aurenta wannan karon.
Baffah bai san da gaske Iyah take ba, sai da ya ji kokenta akan a roke shi ya barta ta auri wadda zata nutsu da shi.
Ya dawo gida a sanyaye, ya tarar da su duk suna gidan har Sumayya.
Ya zauna a cikinsu, suka gaisa.
Ya kasa daurewa ya ce " Iyah na ji sakon ki, na san wannan hukuncin da kika yanke a iya fatar bakin ki ne, amma tunda kin yarda da shawarwarin makusantan ki, kin tauyewa zuciyar ki, da 'danki fari ciki shikenan. Ai dama ke ce kike da hakkin zabawa kanki miji domin kin girma hankali ya ratsa ki".
Cikin hikimar ubangiji sai kawai ya zauna dabas angurin, farin yadinsa na tissue original din, ya debi 'kura da ciyayi amma baima sani ba.
Yana zaune sai zufa ke karyo masa, take kuma hakoransa suka dinga kadawa tabbacin zazzabi ya kawo gudunmawa a tashin hankalin da yake ciki.
Da kyar ya ciro wayarsa ya mika mata ya ce "Taimaka ki lalubo mini Abbas".
Jikinta a matu'kar sanyaye har bari take yi saboda halin da yau ta ga Mk a ciki ya matu'kar kidima ta.
Bugu daya Abbas ya dauka. Cikin karfin hali Mk ya ce taimake ni ka zo ka dauke ni, ina nan gandu gidan nan na layin Madugu, ba zan iya tuki bane".
Ya kashe wayar ya kalleta idonsa ya ka'da sosai ya ce "kin manta duk rayuwar da kika yi ta jin da'di a hannuna, kin manta alheri na, kin manta duk kalolin soyayyar da nake gwada miki, kin dora kuskurena akan dukkan wadannan abubuawan".
Ta kasa magana, ya sake kallon ta soasai fuskarsa duk gumi tamkar ya yi alwala ya ce "ki manta dukkan dadin da nake raba dare ina jiyar da ke, kin ri'ke sharri na guda daya. Har yau din nan ban ji a jikina na zalunce ki ba, na san dai babban laifi na auren da na yi ne, aure kuwa ko muna tare idan bu'katar yinsa ta zo ba zaluntarki na yi ba. Amma duk da hakan na yi ta baki ha'kuri, na fada miki kaddara ta ce auren nan da na yi. Amma ubangiji shine shaidata akan ba abin da ya ragu na daga son da nake miki, bana jin kuma a cikin wannan duniyar akwai abin da zan so ya zarta ki".
Ya nisa ya ce "Amma duk kin yi fatali da komai, kin dage sai kin yi ramuwar gayya. Abin da baki sani ba, shine ba ni da karfin guiwar juriya akan kishin ki, amma tunda kin dage shikenan, kawai ina jiye miki fargar jaji ne, ina jiye miki ki maida 'danki maraya. Shiga gida na gode sosai".
Ya yi shiru, zufa na sake karyo masa ta ko ina.
Kafin ta yi magana Abbas ya iso a adaidaita sahu.
Ya gaisheta, tare da tambayar ahalin gidansu.
Mk ya mika masa hannu, shikuma ya mikar da shi.
Suka doshi mota ba tare da Mk ya sake cewa komai ba.
Abbas ya dinga jin tausayin wadannan masoya, a ransa ya dinga musu addu'ar samun daidaito ko hankalinsu ya kwanta.
Kwanan Mk biyu a kwance Farida na jinyarsa domin a wnanan karon har ruwa aka kara masa, a gida.
Mahmoud ya damu sosai ya sake komawa wurin Sa'a Amma ta kafe ita fa ta riga ta ha'kura da Mk.
Haka da Baffa ya tambayeta ta ce ita kam bata sonsa, abin ya farantawa Inna rai, ba irin kabalin da Baffa bai yi ba ta ce ita kam ta riga da ta shafe babinsa. Lamarin da ya farantawa Inna rai ba ka'dan ba.
Da ta ga da gaske Baffa zai mata fin karfi ta shirya suka tafi Gogel ita da Sumayya, ta kai korafi wurin Yayan Baffah da ya ce a Gogel din za'a daura aurenta wannan karon.
Baffah bai san da gaske Iyah take ba, sai da ya ji kokenta akan a roke shi ya barta ta auri wadda zata nutsu da shi.
Ya dawo gida a sanyaye, ya tarar da su duk suna gidan har Sumayya.
Ya zauna a cikinsu, suka gaisa.
Ya kasa daurewa ya ce " Iyah na ji sakon ki, na san wannan hukuncin da kika yanke a iya fatar bakin ki ne, amma tunda kin yarda da shawarwarin makusantan ki, kin tauyewa zuciyar ki, da 'danki fari ciki shikenan. Ai dama ke ce kike da hakkin zabawa kanki miji domin kin girma hankali ya ratsa ki".