Sashe 18
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read
Ta yi kamar ba ta ji ba, ta doshi hanyar shigewa da azama ya sha gabanta, ya ce "kwanakin baya fa a gabana Baffa ya ce miki ko rago ya kawo ya kamata ya shiga rigarsa".
Ta turo baki ta ce " Ai son rai ne yasa shi fa'din hakan, ya san komai yake so ina taya shi son abin ina kuma girmama shi. Amma kai Baffa ne yake sonka ya daukaka lamarinka ya girmamaka. Yayin da kai baka sonsa kana amfani da shi ne dan cikar burinka da zarar ka samu, zaka iya ture komai ka kunyata shi, ka cusa masa takaicin da yake fakar idon mutane yana goge hawayen ba'kin cikin ka".
Idonta ya ciko da hawaye, ta shanye ta zarce da fadin " wannan karon wallahi har Baffan na shirya shayar da shi mamaki tunda baya kishina. Matu'kar Sharia ta damka mini zabin mijin aure a hannuna to ina tabbatar maka zan yi iyakacin yi na na dora hukuncin Sharia akan hukuncin Baffah. Ka rabu da ni, ka daina zuwa wurin ubana, kai ba 'dan-uwanmu bane, bamu da alakar komai da kai, akan me zaka zo ka dinga yi mini katsalandan a tsakanina da ubana, alhalin lokacin da ya kamata na shiga rigar uban nawa nuna mini ka yi bai isa ba, amma yanzu kana mini karfa karfar dole ka shiga rigarsa".
Jikin Mk ya yi sanyi kwarai da gaske ya ce "Allah dai ya so ba daga sama na fado ba Sa'adatu, kina yawan yi mini gorin bamu hada komai ba, na yarda bamu hada komai ba, amma Jawad ya hadamu, Baffa ai kakansa ne wannan hadin ai ya wuce ace na zama bare".
Ta kufulo ta ce "oh saboda Jawad kake mini wannan bibiyar, kake neman hada ni ya'ki da tsohona, to albishirinka, duk duniya uwace kawai ta san ainihin uban danta".
Wannan karon bai kai hannu jikinta da niyyar duka ba, amma ya yi matu'kar kidima, wani irin tashin hankali ya bayyana a fuskarsa da jikinsa, sai ta ganshi tamkar ranar da ya saketa.
Ya jingina da bango yana fa'din"Ya Hayyu ya QAYYUM bi Rahamatika astagisu".
Abin mamaki tausayinsa ya shigeta soasai, amma ta daure ta hadiye shi.
Ido jawur ya kalleta ya ce "Ki yiwa Allah da Ma'aiki ki fa'da mini mai zan yi ki daina jifana da irin wadannan kazaman kalaman da suke nufin tarwatsewata".
Yana rufe baki ta ce "ka daina shiga tsakanina da ubana saboda kai Baffa ya mini abin da har na mutu ba zan daina takaici ba, ba zan daina zubar da hawaye ba, ba dan darajar sa ta zarta komai a gurina ba, wallahi da ba zan yafe ba domin iyakacin cin fuska anyi mini, ba kuma dan komai ba sai dan ya faranta maka".
Ya tausasa murya ya ce " Fada mini abin da ya miki saboda ni, na miki al'kawarin idan na ji kina da hujja ba zan sake zuwa wajensa akan maganar ki ba, ke kawai zan tunkara, ke kuma ai sai kin amince".
Murya na rawa ta ce "kasan dai ai kusan sadakata Baffah ya baka, Nima nasan haka aka kai ni ba wata hidima, amma dai naje da gadona da kayayyakin amafanin da suka fi zama Dole. Na so a mini kayan daki da lefe kamar yadda ake yi a al'ada amma na yi hakuri na bi ra'ayinsa, dan samun albarka.
Bayan mun rabu na tattara komai da nake ganin kamaar lefe na ne, har da gold dina sai da ya nutse na sayi filaye da zummar idan hidimar iyayena ko aure ya zo mini a siyar ayi hidima, kawai Baffa ya je ya siyar mini ya baka kudin ka yi aure kana jin dadinka ni kuma ko na mutu ko na yi rai ko oho".
Wani irin kuka ya kwace mata, fiye da wadda ta yi a ranar rabuwarsu a mota, sosai take yinsa saboda yadda abin yake dafata.
Kukan da take yi ya wanke bacin ran da ta jefa shi a farko.
Tausayinta ya maye gurbin takaicin maganar da ta caba masa ya ce "Tabbas ba a miki adalci ba Sa'adatu, amma ki yi hakuri, na yarda kuma Baffah ya na sona, amma ko daya cikin goman son da yake miki ban samu ba. Da ciwo sosai, da gaske kuma na taya ki jin takaici, amma bari na tuna miki wasu abubuwa, Ni dai na da'de ban ga mai sa'a irinki ba, tabbas kin ci sunan ki na Sa'a".
Ya nisa ya ce da" kin san irin soyayyar da Baffah yake Miki da kin ji kunyar takaicin ya siyar da abinki ya bani na yi aure."
Ta turo baki ta ce " Ai son rai ne yasa shi fa'din hakan, ya san komai yake so ina taya shi son abin ina kuma girmama shi. Amma kai Baffa ne yake sonka ya daukaka lamarinka ya girmamaka. Yayin da kai baka sonsa kana amfani da shi ne dan cikar burinka da zarar ka samu, zaka iya ture komai ka kunyata shi, ka cusa masa takaicin da yake fakar idon mutane yana goge hawayen ba'kin cikin ka".
Idonta ya ciko da hawaye, ta shanye ta zarce da fadin " wannan karon wallahi har Baffan na shirya shayar da shi mamaki tunda baya kishina. Matu'kar Sharia ta damka mini zabin mijin aure a hannuna to ina tabbatar maka zan yi iyakacin yi na na dora hukuncin Sharia akan hukuncin Baffah. Ka rabu da ni, ka daina zuwa wurin ubana, kai ba 'dan-uwanmu bane, bamu da alakar komai da kai, akan me zaka zo ka dinga yi mini katsalandan a tsakanina da ubana, alhalin lokacin da ya kamata na shiga rigar uban nawa nuna mini ka yi bai isa ba, amma yanzu kana mini karfa karfar dole ka shiga rigarsa".
Jikin Mk ya yi sanyi kwarai da gaske ya ce "Allah dai ya so ba daga sama na fado ba Sa'adatu, kina yawan yi mini gorin bamu hada komai ba, na yarda bamu hada komai ba, amma Jawad ya hadamu, Baffa ai kakansa ne wannan hadin ai ya wuce ace na zama bare".
Ta kufulo ta ce "oh saboda Jawad kake mini wannan bibiyar, kake neman hada ni ya'ki da tsohona, to albishirinka, duk duniya uwace kawai ta san ainihin uban danta".
Wannan karon bai kai hannu jikinta da niyyar duka ba, amma ya yi matu'kar kidima, wani irin tashin hankali ya bayyana a fuskarsa da jikinsa, sai ta ganshi tamkar ranar da ya saketa.
Ya jingina da bango yana fa'din"Ya Hayyu ya QAYYUM bi Rahamatika astagisu".
Abin mamaki tausayinsa ya shigeta soasai, amma ta daure ta hadiye shi.
Ido jawur ya kalleta ya ce "Ki yiwa Allah da Ma'aiki ki fa'da mini mai zan yi ki daina jifana da irin wadannan kazaman kalaman da suke nufin tarwatsewata".
Yana rufe baki ta ce "ka daina shiga tsakanina da ubana saboda kai Baffa ya mini abin da har na mutu ba zan daina takaici ba, ba zan daina zubar da hawaye ba, ba dan darajar sa ta zarta komai a gurina ba, wallahi da ba zan yafe ba domin iyakacin cin fuska anyi mini, ba kuma dan komai ba sai dan ya faranta maka".
Ya tausasa murya ya ce " Fada mini abin da ya miki saboda ni, na miki al'kawarin idan na ji kina da hujja ba zan sake zuwa wajensa akan maganar ki ba, ke kawai zan tunkara, ke kuma ai sai kin amince".
Murya na rawa ta ce "kasan dai ai kusan sadakata Baffah ya baka, Nima nasan haka aka kai ni ba wata hidima, amma dai naje da gadona da kayayyakin amafanin da suka fi zama Dole. Na so a mini kayan daki da lefe kamar yadda ake yi a al'ada amma na yi hakuri na bi ra'ayinsa, dan samun albarka.
Bayan mun rabu na tattara komai da nake ganin kamaar lefe na ne, har da gold dina sai da ya nutse na sayi filaye da zummar idan hidimar iyayena ko aure ya zo mini a siyar ayi hidima, kawai Baffa ya je ya siyar mini ya baka kudin ka yi aure kana jin dadinka ni kuma ko na mutu ko na yi rai ko oho".
Wani irin kuka ya kwace mata, fiye da wadda ta yi a ranar rabuwarsu a mota, sosai take yinsa saboda yadda abin yake dafata.
Kukan da take yi ya wanke bacin ran da ta jefa shi a farko.
Tausayinta ya maye gurbin takaicin maganar da ta caba masa ya ce "Tabbas ba a miki adalci ba Sa'adatu, amma ki yi hakuri, na yarda kuma Baffah ya na sona, amma ko daya cikin goman son da yake miki ban samu ba. Da ciwo sosai, da gaske kuma na taya ki jin takaici, amma bari na tuna miki wasu abubuwa, Ni dai na da'de ban ga mai sa'a irinki ba, tabbas kin ci sunan ki na Sa'a".
Ya nisa ya ce da" kin san irin soyayyar da Baffah yake Miki da kin ji kunyar takaicin ya siyar da abinki ya bani na yi aure."