Sashe 10
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ba zato Sa'a ta ji Mk ya ja uban tsaki mai tsayi, sai kuma ta ji yana cewa "Mahmoud saka mini wa'kar Auren Dole ta Ali jita".
Dariya Mahmoud ya yi ya ce "bansan jita yayi wakar auren dole ba, ta aure mai da'di nasan ya yi"
A gajarce Mk ya ce "to lalubo mini wadda zata dace da halin takurar da nake ciki, banda Hajiya da Baffa sun matsa mini, ina zan zo gurin wannan shugabar masu wula'kancin da niyyar wata magana, ai tun wulakantani da ta yi a ziyarar Jawad na gane idan ka shekara dubu baka mutum ba, kar ka tambaye shi komai binciki halinsa".
Ya nisa ya sake jan tsaki ya ce " Ta tisa ni tana kukan gulma da iskanci, alhalin kasan ranta murna da farin-ciki ne fal, dan kuwa ban tsammaci zata iya barci ba, mafi yawa butulcin mace ke kaita wuta, abin da aka jima ana rokon ya tabbata ne, ya zo kuma sai a bude shafin iyashege, har da kuka kala kala tamkar wata yar yarinya alhalin gyara da kwalliya ne kawai domin ana kallon Jawad za'a gane ta tsufa".
Wani irin daskarewa Sa'adah ta yi, wato Mk da rashin mutunci ya zo, ta tabbatar da hakan tunda a gaban Baffa ma ya yi mata diban karan mahaukaciya, amma ba laifinsa bane, Baffa ne ya bada ita, dama kuma ance naka ne yake bada kai.
Duk yadda ta so shanye maganar Mk kasawa ta yi, ta yi jarumtar shanye kukan ta ce "duk tsufana dai ka girme ni, kuma ina rokonka ka koma ka fadawa wadda suka yi maka dolen aurena! na ce bana sonka, bana sha'awar zama da kai, domin wadda ya soni ina budurwa, yanzuma da na tsufa son nawa ya nan a tare da shi saboda ba sha'awata yake yi ba, idan kuma na so ma saurayi zan aura wadda ni zan cire masa samartakarsa fiye da yadda na ta'ba cirewa wasu".
Ai bata karasa ba, ya shammaceta ya wawurota ya kama bakinta ya murde da karfin gaske, dan kansa ya saketa bayan ya tabbatar ta ji a jikinta. Jikinsa na rawa ya ce "wallahi idan baki kiyaye harshen ki a gabana ba, zaki sha wahala ai yanzu ke ba yarinya karama bace da zaki dinga mini kaifin harshe".
Mahmoud kuwa da ya lura da abin da Mk yake yi ya kasa juyowa balle ya bude baki yayi magana saboda tamkar ya fashe da kuka haka yake ji.
Kuka sosai Sa'adah take tana fadin idan yafi karfinta ai bai fi karfin ubangiji ba, ya fa'da mata bakar magana, dan ta rama shine zai mata wannan wulakancin?
Har suka iso layin gidan Sumayya kuka sosai take yi, yayin da Mk ya biris tamkar bai ji ta ba, wani wula'kanci da Mahmoud ya yi mata, maimakon ya isa gidan sai ya samu gefe ya yi perking ya kunna musu a.c ya fice ya barsu, a kokarinsa na su dan sami daidaito shima kuma ya fita ya shaki isakar da zai dan samu sukunin zuciyarsa, da gaske da son Iyah zai mutu a ransa, wannan na cikin kaddararsa rashin cikar buri.
Tsawon mintina Sa'a na kuka sosai, Mk da ya tabbatar ta yi shi ba ka'dan ba, ya santa da son a rarrasheta.
Dan haka ya matsa sosai daga jikinta, ya yi gyaran murya ya ce " kukan ya isa haka My first love".
Wani azabben kishi ya duro mata na ba zata, ta sake karfin kukanta tare da cewa "karka kuma cemin first love dinka, domin ni ba ita bace, kaima kasan ba ni bace. First love dinka tana can tana jiranka wacce ba zata tsufa ba tunda bata da kamar Jawad, Ni barni a makiyarka domin bansan komai da ka mini, kuma kake kan yi mini ba Sai kiyayyya da zalunci hadi da wulakanci".
Jikin Mk ya yi sanyi ya ce da bakinki kika ce ban miki komai ba sai kiyayya da zalunci?".
Da azama ta ce "kwarai kuwa! zan kuma rokeka ka koma ka fa'dawa Hajiya da Baffah su janye dolen da suka yi maka, domin ni ba sonka nake yi ba, ko ina sonka to na ha'kura, domin a yanzu sun nuna mini ka fini a gunsu tunda sai yanzu ne zasu maka dole,to ni kuwa ina tabbatar maka na wuce haka wallahi".
Ya ce "Zan so kwarai mu fahimci juna, domin ni ban zo gurinki bisa ra'ayin wani ba, tsokanar ki nake yi, na gane ke ce cikon farin ciki na, ki zo mu rayu tare na sauran shekarun da ubangiji zai ara mana a gaba. kin san ina son ki, kin san ke kika mini laifi, na dauka ko wani kika ji ya ce na zalunce ki, zaki kare ni, amma fa'da mini me nayi miki na zalunci?"
Ta yi shiru tana kuka kasa kasa, tana jin tamkar ta tashi ta yi ta rawa dan ta nunawa duniya irin farin cikin da kasan zuciyar ta yake ciki.
Ta kasa cewa komai, ya nisa ya ce "Yanzu mu ba yara bane Sa'adah, ya kamata mu bar komai mu manta komai, mu gina sabuwar rayuwar da babu gillin bacin rai a ciki, ubangiji shine shaidata ba komai a zuciyata na yafe miki, na kuma manta komai".
"Kema ki daure ki manta duk wani zaluncin da kike ganin na yi miki, ina tsananin son na rayu da ke my Sa'adah".
Da kuka sosai ta ce "Ba haka bane a zuciyarka, kaima kasan ba haka bane, akwai dalilin da ya saka ka yafe mini amma ba dan kana sona ko dan kana son ka rayu da ni ba, daga ranar da ka jefe ni da mafi munin al'amari, a ranar na gane baka sona, wata kake so, kake neman hanyar da zaka rayu da ita, tunda ni amfani na ya kare a gurinka, ka riga ka dandana ni, shiyasa ka 'karanta tunaninka, ka kasa shaidata, ka kasa gane abin da zan yi da wadda ba zan yi ba, dama Kuma ai tun bamu yi aure ba, kake jifana da wannan zargin, yanzu kuma idan na koma maka ai cewa zaka yi har dakinka nake iskancin".
Ta nisa ta sake cewa "na tabbatar ita baka ta'ba dukanta ba, amma ni saboda rashin gata da 'kin da kake mini kanka tsaye kake duka na"
Ta fa'da cikin kuka, maimakon hankalin Mk ya tashi sai ya ji wata irin nutsuwa ta zo masa domin kuwa ya gane da gaske 'Karfi ya ke da ya ce akwai soyayyarsa mai yawa a zuciyarta duk da bakinta na kirarin 'kinsa.
Kishin Farida ke ya galgalata wannan kuwa ba yadda zata yi sai hakuri. Domin ya riga ya kudire ba zai ta'ba barin matsanancin son da yake yiwa Sa'a ya sa ya zalunci Farida ba, ba kuma zai yi kuskuren rabuwa da ita dan zai dawo da tsohuwar matarsa ba.
Bashi da burin auren mata biyu, amma tunda kaddara ta zaba masa to kuwa zai yi iya kokarinsa bai bari soyayyar daya tasa ya danne daya ba.
Cikin lallashi ya ce "sonki ne yake rufe mini ido shiyasa nake dukan ki, Amma ai kinsan iya bakinki nake duka dan shine mai dafi, amma ta yaya zan doki jikin ki alhalin shine abin hutawata. Na rantse miki banda tsoron ubangiji da a motar nan sai na shige, dan ki gane ba karamin kewar ki nake yi ba, har yau din nan 'kwarar Farida nake yi domin idan ina tarawa da ita bana samun nutsuwa, sai na ayyano ke ce a 'kasana amma kina fa'din wai ban miki komai ba sai zalinci".
Kuka sosai Sa'adah ta fashe masa maimakon ta ji da'din kalamansa, ai sai ta ji tamkar cin fuskarta yake yi, yanzu ya murde mata baki Dan ta yi jam'u ta ce wasu samarin alhalin yasan shi ka'dai ta cirewa samartaka. Amma shi yana fa'da mata yana tarawa da wata kansa tsaye.
A cikin kukan ta ce " in Sha Allah Babu sauran zama a tsakanin mu, zan yi dukkan kokarina naga ban jefa kaina a uku ba, a satin nan zan fitar da wadda zan aura, ba zan iya auren ka ba Mukhtar. Ka yiwa Allah ka rabu da ni bana sonka yanzu".
Cikin rashin damuwa ya ce "Ban damu da ki so ni ba, domin son da nake miki ya isa ya ri'ke auren mu, idan kuma kin kafe ba zaki yarda mu yi auren ba, shikenan amma ki sani ban yi al'kawarin zan iya cigaba da jarumtar kawar da ido akan ki ba, kin sanni sarai! Billahillazi ki shirya yin jegon da babu sannu, domin kuwa ciki zan miki, ki haifarwa Innah, kafin a ankara zan sake dirka miki wani sai akaiwa Hajiyar Bichi".
Gaban Sa'a ya buga da karfin gaske, mafarkin Innah ya Fa'do mata, amma sai ta waske ta daure fuska ta ce "saboda kana jin isa, ko dan ka raina gidanmu?"
Ya make kafada ya ce " whatever".
"Dan Allah Mukhtar ka bude min kofa zan fita na gaji da jin Wannan maganganun marasa azanci da kan gado".
Dariya Mahmoud ya yi ya ce "bansan jita yayi wakar auren dole ba, ta aure mai da'di nasan ya yi"
A gajarce Mk ya ce "to lalubo mini wadda zata dace da halin takurar da nake ciki, banda Hajiya da Baffa sun matsa mini, ina zan zo gurin wannan shugabar masu wula'kancin da niyyar wata magana, ai tun wulakantani da ta yi a ziyarar Jawad na gane idan ka shekara dubu baka mutum ba, kar ka tambaye shi komai binciki halinsa".
Ya nisa ya sake jan tsaki ya ce " Ta tisa ni tana kukan gulma da iskanci, alhalin kasan ranta murna da farin-ciki ne fal, dan kuwa ban tsammaci zata iya barci ba, mafi yawa butulcin mace ke kaita wuta, abin da aka jima ana rokon ya tabbata ne, ya zo kuma sai a bude shafin iyashege, har da kuka kala kala tamkar wata yar yarinya alhalin gyara da kwalliya ne kawai domin ana kallon Jawad za'a gane ta tsufa".
Wani irin daskarewa Sa'adah ta yi, wato Mk da rashin mutunci ya zo, ta tabbatar da hakan tunda a gaban Baffa ma ya yi mata diban karan mahaukaciya, amma ba laifinsa bane, Baffa ne ya bada ita, dama kuma ance naka ne yake bada kai.
Duk yadda ta so shanye maganar Mk kasawa ta yi, ta yi jarumtar shanye kukan ta ce "duk tsufana dai ka girme ni, kuma ina rokonka ka koma ka fadawa wadda suka yi maka dolen aurena! na ce bana sonka, bana sha'awar zama da kai, domin wadda ya soni ina budurwa, yanzuma da na tsufa son nawa ya nan a tare da shi saboda ba sha'awata yake yi ba, idan kuma na so ma saurayi zan aura wadda ni zan cire masa samartakarsa fiye da yadda na ta'ba cirewa wasu".
Ai bata karasa ba, ya shammaceta ya wawurota ya kama bakinta ya murde da karfin gaske, dan kansa ya saketa bayan ya tabbatar ta ji a jikinta. Jikinsa na rawa ya ce "wallahi idan baki kiyaye harshen ki a gabana ba, zaki sha wahala ai yanzu ke ba yarinya karama bace da zaki dinga mini kaifin harshe".
Mahmoud kuwa da ya lura da abin da Mk yake yi ya kasa juyowa balle ya bude baki yayi magana saboda tamkar ya fashe da kuka haka yake ji.
Kuka sosai Sa'adah take tana fadin idan yafi karfinta ai bai fi karfin ubangiji ba, ya fa'da mata bakar magana, dan ta rama shine zai mata wannan wulakancin?
Har suka iso layin gidan Sumayya kuka sosai take yi, yayin da Mk ya biris tamkar bai ji ta ba, wani wula'kanci da Mahmoud ya yi mata, maimakon ya isa gidan sai ya samu gefe ya yi perking ya kunna musu a.c ya fice ya barsu, a kokarinsa na su dan sami daidaito shima kuma ya fita ya shaki isakar da zai dan samu sukunin zuciyarsa, da gaske da son Iyah zai mutu a ransa, wannan na cikin kaddararsa rashin cikar buri.
Tsawon mintina Sa'a na kuka sosai, Mk da ya tabbatar ta yi shi ba ka'dan ba, ya santa da son a rarrasheta.
Dan haka ya matsa sosai daga jikinta, ya yi gyaran murya ya ce " kukan ya isa haka My first love".
Wani azabben kishi ya duro mata na ba zata, ta sake karfin kukanta tare da cewa "karka kuma cemin first love dinka, domin ni ba ita bace, kaima kasan ba ni bace. First love dinka tana can tana jiranka wacce ba zata tsufa ba tunda bata da kamar Jawad, Ni barni a makiyarka domin bansan komai da ka mini, kuma kake kan yi mini ba Sai kiyayyya da zalunci hadi da wulakanci".
Jikin Mk ya yi sanyi ya ce da bakinki kika ce ban miki komai ba sai kiyayya da zalunci?".
Da azama ta ce "kwarai kuwa! zan kuma rokeka ka koma ka fa'dawa Hajiya da Baffah su janye dolen da suka yi maka, domin ni ba sonka nake yi ba, ko ina sonka to na ha'kura, domin a yanzu sun nuna mini ka fini a gunsu tunda sai yanzu ne zasu maka dole,to ni kuwa ina tabbatar maka na wuce haka wallahi".
Ya ce "Zan so kwarai mu fahimci juna, domin ni ban zo gurinki bisa ra'ayin wani ba, tsokanar ki nake yi, na gane ke ce cikon farin ciki na, ki zo mu rayu tare na sauran shekarun da ubangiji zai ara mana a gaba. kin san ina son ki, kin san ke kika mini laifi, na dauka ko wani kika ji ya ce na zalunce ki, zaki kare ni, amma fa'da mini me nayi miki na zalunci?"
Ta yi shiru tana kuka kasa kasa, tana jin tamkar ta tashi ta yi ta rawa dan ta nunawa duniya irin farin cikin da kasan zuciyar ta yake ciki.
Ta kasa cewa komai, ya nisa ya ce "Yanzu mu ba yara bane Sa'adah, ya kamata mu bar komai mu manta komai, mu gina sabuwar rayuwar da babu gillin bacin rai a ciki, ubangiji shine shaidata ba komai a zuciyata na yafe miki, na kuma manta komai".
"Kema ki daure ki manta duk wani zaluncin da kike ganin na yi miki, ina tsananin son na rayu da ke my Sa'adah".
Da kuka sosai ta ce "Ba haka bane a zuciyarka, kaima kasan ba haka bane, akwai dalilin da ya saka ka yafe mini amma ba dan kana sona ko dan kana son ka rayu da ni ba, daga ranar da ka jefe ni da mafi munin al'amari, a ranar na gane baka sona, wata kake so, kake neman hanyar da zaka rayu da ita, tunda ni amfani na ya kare a gurinka, ka riga ka dandana ni, shiyasa ka 'karanta tunaninka, ka kasa shaidata, ka kasa gane abin da zan yi da wadda ba zan yi ba, dama Kuma ai tun bamu yi aure ba, kake jifana da wannan zargin, yanzu kuma idan na koma maka ai cewa zaka yi har dakinka nake iskancin".
Ta nisa ta sake cewa "na tabbatar ita baka ta'ba dukanta ba, amma ni saboda rashin gata da 'kin da kake mini kanka tsaye kake duka na"
Ta fa'da cikin kuka, maimakon hankalin Mk ya tashi sai ya ji wata irin nutsuwa ta zo masa domin kuwa ya gane da gaske 'Karfi ya ke da ya ce akwai soyayyarsa mai yawa a zuciyarta duk da bakinta na kirarin 'kinsa.
Kishin Farida ke ya galgalata wannan kuwa ba yadda zata yi sai hakuri. Domin ya riga ya kudire ba zai ta'ba barin matsanancin son da yake yiwa Sa'a ya sa ya zalunci Farida ba, ba kuma zai yi kuskuren rabuwa da ita dan zai dawo da tsohuwar matarsa ba.
Bashi da burin auren mata biyu, amma tunda kaddara ta zaba masa to kuwa zai yi iya kokarinsa bai bari soyayyar daya tasa ya danne daya ba.
Cikin lallashi ya ce "sonki ne yake rufe mini ido shiyasa nake dukan ki, Amma ai kinsan iya bakinki nake duka dan shine mai dafi, amma ta yaya zan doki jikin ki alhalin shine abin hutawata. Na rantse miki banda tsoron ubangiji da a motar nan sai na shige, dan ki gane ba karamin kewar ki nake yi ba, har yau din nan 'kwarar Farida nake yi domin idan ina tarawa da ita bana samun nutsuwa, sai na ayyano ke ce a 'kasana amma kina fa'din wai ban miki komai ba sai zalinci".
Kuka sosai Sa'adah ta fashe masa maimakon ta ji da'din kalamansa, ai sai ta ji tamkar cin fuskarta yake yi, yanzu ya murde mata baki Dan ta yi jam'u ta ce wasu samarin alhalin yasan shi ka'dai ta cirewa samartaka. Amma shi yana fa'da mata yana tarawa da wata kansa tsaye.
A cikin kukan ta ce " in Sha Allah Babu sauran zama a tsakanin mu, zan yi dukkan kokarina naga ban jefa kaina a uku ba, a satin nan zan fitar da wadda zan aura, ba zan iya auren ka ba Mukhtar. Ka yiwa Allah ka rabu da ni bana sonka yanzu".
Cikin rashin damuwa ya ce "Ban damu da ki so ni ba, domin son da nake miki ya isa ya ri'ke auren mu, idan kuma kin kafe ba zaki yarda mu yi auren ba, shikenan amma ki sani ban yi al'kawarin zan iya cigaba da jarumtar kawar da ido akan ki ba, kin sanni sarai! Billahillazi ki shirya yin jegon da babu sannu, domin kuwa ciki zan miki, ki haifarwa Innah, kafin a ankara zan sake dirka miki wani sai akaiwa Hajiyar Bichi".
Gaban Sa'a ya buga da karfin gaske, mafarkin Innah ya Fa'do mata, amma sai ta waske ta daure fuska ta ce "saboda kana jin isa, ko dan ka raina gidanmu?"
Ya make kafada ya ce " whatever".
"Dan Allah Mukhtar ka bude min kofa zan fita na gaji da jin Wannan maganganun marasa azanci da kan gado".