← Book details Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 45

Sashe 3

Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 4 min read

Asalima Inna sai take ganin tamkar so yake ya shafawa Sa'adah kashin kaji. kuma raina arzikinsu ya yi.
Kwanaki biyu suka ragewa Mk ya wuce, ya dauki Farida da hantsi suka je ta gaida Hajiyar Bichi, duk yadda Hajiya take jin dama Sa'a ya dawo da ita, ta karbi Farida da sakakkiyar fuska, yayin da Jawad ya ke ta murnar Malam ya ce zasu bishi Ingila a jirgi da wannan balabiyar Auntin. Dai dai lokacin shekarun Jawad goma.
Kunyar Farida da sanyin ta yasa Hajiya ta dan rage 'kin data ke yiwa auren na su.
A hanyar su ta komawa gida ta ga ya sauka daga kan titin da zai bi ta unguwar su, ya hau wani daban.
Bata ce kala ba, ta zuba masa ido kawai.
Bai tsaya ko ina ba sai a harabar hotel din Tahir.
Jikin Farida ya yi sanyi sosai, ta shiga cikin rudani da fargaba, amma haka ta bishi, har dakin da ya riga da ya kama a safiyar yau, domin taga a aljihunsa ya fito da mukallin daki mai lamba 008.
A dadare ta shiga ta zauna, shikuma ya juya ya fita, ba'a jima ba ya dawo da leda mai dauke da yougurt da gasasshen kifi, sai lemuka masu sanyi hadi da ruwa.
Ka'dan ta dan ta'ba adalilin matsawar da ya mata, shi kuwa da dama yunwa yake ji sosai ya ci, sannan ya shiga ya yo wanka, ya fito daure da tawul iya kugunsa.
Mk da kansa ya dinga mamakin kansa bai yi zaton zai ji sha'awar wata macen bayan Sa'a ba, bai yi zaton zai yi rawar jiki har ya kasa ha'kuri su isa Uk kafin ya tare da amaryarsa ba, amma abin mamaki jiya kwana ya yi yana juyi, rabon da ya shiga irin wannan yanayin ya manta, bai sani ba ko dan yasan bai da wadda ta halatta a gare shi ne.
Ganin abin na neman kassara shi, shiyasa ya murje kunya ya je har gidansu ya daukota da zummar zai kaita ta gaida mahaifiyarsa sannan sisters dinsa na son ganinta sosai.
Sanin mijinta ne yasa ba a nemi ba'asi ko fargabar fitar su tare ba, asalima kyakkawan shiri aka mata, domin turaren da mahaifiyarta ta dinga bin duk wata ga'ba tana shafa mata na alfarma ne, takanas ake yiwa manyan matan da suka amsa sunansu a sanin duniyar kamshi.
Sannan ta bata wani irin tsumi da tunda aka fara aurenta kullum sai ancika mata ciki da shi, akan Dole Farida ke Sha, saboda kasancewarta masaniyar magaganuwa bata yarda da Shan kowanne irin abu da sunan magani ba.
Wannan kamshin ya sake rikita Mk yana jin tamkar wani maganadisu ke jansa ga Farida, shi ka'dai yasan yaddda ya kosa su kadaice.
Duk yadda Farida ta ke da kunya ta yi iyakcin bakin kokarinta ta bashi hadin kai, duk da yadda ta ke cin kwakwa a hannunsa kasancewar ita din cikakkiyar budurwa ce ta daure ya samu nutsuwa sosai.
Koda ya kammala kifa ta ya yi akan cikinsa fatar jikinsu na manne, yana jin nisha'di sosai ya dinga mata addu'a, yana gode ma ubangiji na yadda duk shine ya fara bude matan da ya aura, ya tsare kansa bai taba Zina ba, ubangijinsa kuma sai ya mutuntata shi ta hanyar bashi katangaggun mata.
Zuciyarsa ta buga da ya tuno Sa'a yasan sharrin zuciya ne da yake jin tamkar tana ha'intarsa ne, amma shi da kansa yasan zai yi wahalar gaske ta aikata wannan al'amarin.
Jikinsa ya dinga bari har Farida ta dinga jin barin, saboda yadda ya ke jin wani iri abu da baisan dalilinsa ba, yau gashi da Farida a cikin yanayin da Sa'adah kawai ya ta'ba tsintar kansa a ciki, ko ya take ji a dalilin aurensa yasan idan itace ta yi aure tabbas sai ya kwanta a gadon likita.
A sanyaye Farida ta ce "baka da lafiya ne? jikinka na rawa fa".
Murya a dashe ya ce" farin cikin yadda na same ki ne, duk son ki ne yake kidima Ni"
A ransa kuma fa'di yaushe zan iya fa'da miki abin da ya kidima ni ai ya zama tamkar cin fusaka ne, gangar jikinmu a hade amma tunanina da zuciyata na wani waje daban.

Ita kuma zuciyarta ta yi fari kal har tana ganin sannu a hankali zata iya mantar da shi Gogel kamar yadda Gogel din tasa ya manta da lamarinta a baya.
Chapter 3 · 0% Book details