Sashe 27
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sai da aka kwana biyu Baffa ya samu labarin ciwon Mk adalilin Bai ganshi ba, bai ga Mahmoud ba, haka Abbas, har shagon su ya je, anan ya samu labarin ai yana asibiti an kwantar da shi.
Akeel ne ya raka shi asibitin, ba karamin damuwa ya shiga da ganin Halin da Mk ya ke ciki ya yi ba.
Ya dinga yi masa addu'a yana tofa masa.
Har ya gama zamansa Mk bai farka ba, ya isa gida ya tarar da Innah a tsakar gida tana yanke farce, ta masa sannu, ya amsa, ya samu gefe ya zauna.
Ya nisa ya ce "Mutari ne bai da lafiya rabona da shi yau kwanaki uku kenan, dazu na je shagonsa jin ba'asi sai ake fa'da mini bai ji da'di ba, na je na gano shi, Amma ban ji da'din ganin sa ba, domin gaba'daya yana kwance tamkar gawa.
A sanyaye Inna ta ce "Assha Ubangiji yasa zakkar jiki ce".
"Ameen dai! Amm an tabbatar mini jininsa ne ya hau fiye da 'kima, na san baya rasa nasaba da bijirewar ku, Ayyah Salamatu ba zaku yiwa yaron nan sassauci ba, ko bai ci arzikin kowa ba, ya ci na tilon 'dansa mana".
A sanyaye ta ce "Àllah zai bashi lafiya, Iyah har karamin hauka ta yi, amma da aka yi hakuri ai gashi nan ta mike, har ya zama tamkar ba a yi ba, shima zai tashi ne".
Ran Baffa ya fara 'baci da lamarin ta sosai, Amma sai ya mike ya fice domin ya san cigaba da zamansa a cikin gidan yana nufin rikici mai tsanani a tsakanin su, abin da ba zai iya tuna ko sau nawa suka yi a tsayin rayuwar aurensu ba.
Sa'a da ke daki take jiyo su, hankalin ta yayi tashin gauron zabi, ta da'de tana wasi-wasin fishi su Dr 'Karfi suka yi, ko kuwa jikin Mk ne har yanzu domin yadda ta ganshi kwance a gaban mota da irin gudun da Mahmoud ya yi ta tsorata.
Gashi kwana biyu bata sake jin su ko a waya ba.
Hawaye ya 'balle mata, ta tuno sadda yake ce mata, yana jiye mata fargar jaji, yana jiye mata kar 'danta ya zama maraya.
Ta kasa fitowa waje dan idan Inna ta ga tana kuka akan Mk to kuwa ta kade har ganyen ta.
Ta rasa inda zata tsoma ranta.
Washagarin ranar sai ga Baba Isa sun zo har da su Baba umaru, daga asibiti suke, ganin Halin da Mk ya ke ciki, yasa suka ji tausayi, suka saka Mahmoud ya kawo su, su zo ko Allah zai sa a samu yarinya ta huce .
Amma wani abu da Sa'adah ta kasa gane menene ya daure mata baki da zuciyarta, ba abin da take hange sai Mk da Farida cikin mayafi guda, duk tambayar da suke yi mata ta kasa amsawa sai kuka take yi, tana satar kallon mahaifiyarsu.
Hade ran da Inna ta yi, yasa ta ce "Na yafe masa, amma ni bana sonsa da aure".
Jikin su Baba Isa ya mutu kwarai da gaske, dan haka suka ha'kura domin dai sun san yarinyar ta hadiyi ba'kin ciki kala kala.
Ran Baffah bai ta'ba baci irin na yau ba, gaba'daya ya ji Sa'adah da mahaifiyarta sun kunyata shi, sun tozarta shi.
A daddafe ya sallame su, ya dawo gida, ya dinga surfawa Inna sababi, yana fa'din "Ban san ladabin karya kika yi mini ba, a tsawon shekarun da muka kwashe ba sai yanzu".
Ya nisa ya ce "wallahi Salamatu kin yi 'karko irin na kifi ace wai ke kika raba mini gida zuwa jami'iya biyu, kin hana yarinya zabin zuciyarta, saboda son rai irin naki.
Yanzu haka yaro yana gadon asibiti rai a hannun Allah! Tabbas idan ya mutu, ke ce sila, kin bada muhimmiyar gudunmawa wurin kisan rai"
Ta fara kuka ta na cewa "Eh ai da yake shi ka damu da lafiyarsa, shiyasa kake akilon samo masa mafita, amma sadda ta dinga zabura tana surutai ai duk ka manta. Ina nan akan bakana bana son Muutar da Iyah".
Ya hassalo ya ce "to kuwa ba zan iya zama da ke da wannan bakar zuciyar ta ki ba, har kina iya buda baki kina ce wa wanii mai ru'ko da 'Kullaci, to ke ai zuciyar ki tafi ta kafiran farko ma tauri".
Da kuka sosai ta shige 'daki ta fara tattara kayanta tana fa'din "akan Iyah ta komawa Muutar gara na ha'kura da zaman tunda ka ce ba zaka iya zama da ni ba".
Sa'adah da take tsaye tana kukan bacin ran yau akanta iyayenta da bata ta'ba ganin sunyi ko da musu ba, suke wannan tashin hankalin.
Ta bi Inna daki tana bata hakuri amma ko kallonta ba ta yi ba, sai hawaye take yi, tana cigaba da hada kayanta.
Baffa ya shigo ya ce "daina ha'da kayan ki, yau shekaru arbain har da uku da auren mu, kike tunanin dan na rabu da ke zan tura ki gidanku? Ai ni ba azzalumi bane, ba zan karar miki da karfinki da kuruciyarki sannan na sallama ki ba".
Ya nisa sosai ya ce "mahaifiyata ita ta sha nono ta barwa mahaifin ki, kenan a ko ina ni mai tsaya miki ne, ba me tozarta ki ba.
Ni ne zan fita na barki miki gida, ki yi yadda kike so da yaranki, tunda ni ban isa na yi iko da su ba, kin riga kin zama 'Yar birni, son ya'ya kawai shine a gabanki ba tare da tunanin abin da zai biyo baya ba".
Ya sake cewa "ki yi zamanki, ko ban aure ki ba, aike kanwata ce da zan baki 'daki a gidana, bare kuma nine na karar miki da komai".
Ya juya ya fice zuwa dakinsa ya dinga ha'da kayansa. Sa'a ce ta ankara da yadda yake ta fito da kayayyakinsa tsakar gida.
Ta fito da sauri, cikin kuka sosai ta zube tana cewa "Na ro'ke ka Baffah ka yi hakuri, kar ka bar mu ina zaka tafi ka barmu?
Muryarsa na rawa ya ce "ko ina ma zan shiga menene matsalar ku, ina ce yanzu kun yi wayewar da zaku iya rike kanku, ku zartar da hukuncin da ni ne zan yi muku biyayya, ba kune zaku mini ba, saboda kuna gamsar da kanku da uwarku, kyale-kyalen duniya fiye da yadda zan yi muku. Dan haka gara na nesanta kaina da ku, tunda ban isa na ce ga yadda za'ayi a gidana ace mini to ba".
Inna da take bakin kofar daki hawayenta ya kasa tsayawa, da sauri ta tsugunna tana cewa "Ka mini hakuri, na yarda na yi kuskure, na yi laifi, ka gafarce Ni, na amince Muutar kaddarar Iya ne, ina fatan ubangiji ya sa karshen bacin ran mu kenan. Ka yi hakuri na ce to, na amince, ka yi yadda kake so da 'yarka".
Dadi ya mamaye zuciyar Baffa ya ce "Na gode miki Salamatu! Ubangiji ya kore shaidanun da suke son tarwatsa mana kyakkawan zaman mu".
Ya kalli Iyah ya ce "A lokacin da na barki ki yi karatun ki, na tabbatar miki bana so, amma na amince miki dan na yarda alfanu ne a gare mu baki'daya. A lokacin na ro'ke ki duk sadda nima zan zo miki da wata bukata ki daure ki mini biyayya ko da ba kya so, sai dan kin san ba zan dora ki akan abu marar alfanu ko cutarwa a gare ki ba".
Kafin ta amsa masa, ya sake zarcewa da fa'din "To yau ina son na roke ki, ki koma dakin ki, burina a duniya bai wuce ace kina dakin mijinki a zaune kin nutsu ba. Mutari shi nake so ya zame miki miji a karo na biyu".
Da rawar murya ta ce "To Baffah! Na ji, na kuma amince zan yi maka biyayya, zan yi ha'kuri na zauna lafiya da shi komai runtsi".
Da murna Baffa ya ke cewa "Na gode miki in sha Allah ba zaki yi nadama ba, ubangiji ya miki Albarka, ya zaunar da ku lafiya, ya baku zuri'a mai albarka".
Ya nisa ya ce " ku shirya gobe zamu je Gogel ki fa'dawa Yaya Ayuba kin amince ba dole na yi miki ba,
Sannan ku samu lokaci ku gano Mutari domin yana jin jiki"
Da sauri lya mike yana cewa "Bari na bi su Alhaji na fa'da musu wannan labarin mai da'di".
Inna ta bi bayansa da ido har ya fice daga gidan, tana ayyana girman soyayyar da yake yiwa Mukhtar.
Kai tsaye gidan Alh Isa ya dosa, a kofar gidan ys tarar da Dr 'Karfi zai shiga mota, ai kuwa ya ce "Mahmouda zo mu shiga, ba tafiya zaka yi ba".
Baffa da murna yake fa'da musu "ai yanzun nan yarinya ta tabbatar masa ta amince, dan haka ku zama cikin shirin zuwa Gogel, a satin nan. Domin a son raina ku tafi da sadaki, a ranar da kuka je a daura auren a huta, kafin ta sake botsarewa saboda na lura kishin banza ta bari yake rinjayar ta".
Daga Baba umaru har Baba Isa kowa ya yi shiru amma suma jinjina alherin bawan Allahn nan suke yi, da karfin son da yake yiwa 'dansu.
Baba Isa ne ya yi karfin halin cewa "Malam Basiru ka dai matsa mata ta amince, gashi muma zamu sake yin son rai, mu amince da abin da ka zartar domin a samu lafiyar yaron nan ta dai-daita, bamu da bakin godiya, abin da zamu ce maka daya ne, da ikon Allah mu kabawa amanar yarinyar nan, mune iyayensa abin da ya faru a farko ba zai sake maimaituwa ba da ikon ubangiji.
Kira mini yarinyar a waya"
Baffa da ya san bashi da fargaba da azama ya fito da wayarsa.
Bugu 'daya ta dauka, ya ce " Baban ku na Na'ibawa ne zai yi magana da ke".
Kalaman kwantar da hankali tare da yabo da kuma girman mai hakuri Alh Isa ya dinga yi Mata, ya sake jaddada mata kar ta sake yin shiru har sai abu ya girmama, komai ya taso matu'kar yafi karfinta to ta sanar da shi zai magance mata da ikon Allah.
Ya rufe maganar da cewa ko kina da korafi domin mun tsayar da kwanaki biyar masu zuwa na daurin auren ku".
Akeel ne ya raka shi asibitin, ba karamin damuwa ya shiga da ganin Halin da Mk ya ke ciki ya yi ba.
Ya dinga yi masa addu'a yana tofa masa.
Har ya gama zamansa Mk bai farka ba, ya isa gida ya tarar da Innah a tsakar gida tana yanke farce, ta masa sannu, ya amsa, ya samu gefe ya zauna.
Ya nisa ya ce "Mutari ne bai da lafiya rabona da shi yau kwanaki uku kenan, dazu na je shagonsa jin ba'asi sai ake fa'da mini bai ji da'di ba, na je na gano shi, Amma ban ji da'din ganin sa ba, domin gaba'daya yana kwance tamkar gawa.
A sanyaye Inna ta ce "Assha Ubangiji yasa zakkar jiki ce".
"Ameen dai! Amm an tabbatar mini jininsa ne ya hau fiye da 'kima, na san baya rasa nasaba da bijirewar ku, Ayyah Salamatu ba zaku yiwa yaron nan sassauci ba, ko bai ci arzikin kowa ba, ya ci na tilon 'dansa mana".
A sanyaye ta ce "Àllah zai bashi lafiya, Iyah har karamin hauka ta yi, amma da aka yi hakuri ai gashi nan ta mike, har ya zama tamkar ba a yi ba, shima zai tashi ne".
Ran Baffa ya fara 'baci da lamarin ta sosai, Amma sai ya mike ya fice domin ya san cigaba da zamansa a cikin gidan yana nufin rikici mai tsanani a tsakanin su, abin da ba zai iya tuna ko sau nawa suka yi a tsayin rayuwar aurensu ba.
Sa'a da ke daki take jiyo su, hankalin ta yayi tashin gauron zabi, ta da'de tana wasi-wasin fishi su Dr 'Karfi suka yi, ko kuwa jikin Mk ne har yanzu domin yadda ta ganshi kwance a gaban mota da irin gudun da Mahmoud ya yi ta tsorata.
Gashi kwana biyu bata sake jin su ko a waya ba.
Hawaye ya 'balle mata, ta tuno sadda yake ce mata, yana jiye mata fargar jaji, yana jiye mata kar 'danta ya zama maraya.
Ta kasa fitowa waje dan idan Inna ta ga tana kuka akan Mk to kuwa ta kade har ganyen ta.
Ta rasa inda zata tsoma ranta.
Washagarin ranar sai ga Baba Isa sun zo har da su Baba umaru, daga asibiti suke, ganin Halin da Mk ya ke ciki, yasa suka ji tausayi, suka saka Mahmoud ya kawo su, su zo ko Allah zai sa a samu yarinya ta huce .
Amma wani abu da Sa'adah ta kasa gane menene ya daure mata baki da zuciyarta, ba abin da take hange sai Mk da Farida cikin mayafi guda, duk tambayar da suke yi mata ta kasa amsawa sai kuka take yi, tana satar kallon mahaifiyarsu.
Hade ran da Inna ta yi, yasa ta ce "Na yafe masa, amma ni bana sonsa da aure".
Jikin su Baba Isa ya mutu kwarai da gaske, dan haka suka ha'kura domin dai sun san yarinyar ta hadiyi ba'kin ciki kala kala.
Ran Baffah bai ta'ba baci irin na yau ba, gaba'daya ya ji Sa'adah da mahaifiyarta sun kunyata shi, sun tozarta shi.
A daddafe ya sallame su, ya dawo gida, ya dinga surfawa Inna sababi, yana fa'din "Ban san ladabin karya kika yi mini ba, a tsawon shekarun da muka kwashe ba sai yanzu".
Ya nisa ya ce "wallahi Salamatu kin yi 'karko irin na kifi ace wai ke kika raba mini gida zuwa jami'iya biyu, kin hana yarinya zabin zuciyarta, saboda son rai irin naki.
Yanzu haka yaro yana gadon asibiti rai a hannun Allah! Tabbas idan ya mutu, ke ce sila, kin bada muhimmiyar gudunmawa wurin kisan rai"
Ta fara kuka ta na cewa "Eh ai da yake shi ka damu da lafiyarsa, shiyasa kake akilon samo masa mafita, amma sadda ta dinga zabura tana surutai ai duk ka manta. Ina nan akan bakana bana son Muutar da Iyah".
Ya hassalo ya ce "to kuwa ba zan iya zama da ke da wannan bakar zuciyar ta ki ba, har kina iya buda baki kina ce wa wanii mai ru'ko da 'Kullaci, to ke ai zuciyar ki tafi ta kafiran farko ma tauri".
Da kuka sosai ta shige 'daki ta fara tattara kayanta tana fa'din "akan Iyah ta komawa Muutar gara na ha'kura da zaman tunda ka ce ba zaka iya zama da ni ba".
Sa'adah da take tsaye tana kukan bacin ran yau akanta iyayenta da bata ta'ba ganin sunyi ko da musu ba, suke wannan tashin hankalin.
Ta bi Inna daki tana bata hakuri amma ko kallonta ba ta yi ba, sai hawaye take yi, tana cigaba da hada kayanta.
Baffa ya shigo ya ce "daina ha'da kayan ki, yau shekaru arbain har da uku da auren mu, kike tunanin dan na rabu da ke zan tura ki gidanku? Ai ni ba azzalumi bane, ba zan karar miki da karfinki da kuruciyarki sannan na sallama ki ba".
Ya nisa sosai ya ce "mahaifiyata ita ta sha nono ta barwa mahaifin ki, kenan a ko ina ni mai tsaya miki ne, ba me tozarta ki ba.
Ni ne zan fita na barki miki gida, ki yi yadda kike so da yaranki, tunda ni ban isa na yi iko da su ba, kin riga kin zama 'Yar birni, son ya'ya kawai shine a gabanki ba tare da tunanin abin da zai biyo baya ba".
Ya sake cewa "ki yi zamanki, ko ban aure ki ba, aike kanwata ce da zan baki 'daki a gidana, bare kuma nine na karar miki da komai".
Ya juya ya fice zuwa dakinsa ya dinga ha'da kayansa. Sa'a ce ta ankara da yadda yake ta fito da kayayyakinsa tsakar gida.
Ta fito da sauri, cikin kuka sosai ta zube tana cewa "Na ro'ke ka Baffah ka yi hakuri, kar ka bar mu ina zaka tafi ka barmu?
Muryarsa na rawa ya ce "ko ina ma zan shiga menene matsalar ku, ina ce yanzu kun yi wayewar da zaku iya rike kanku, ku zartar da hukuncin da ni ne zan yi muku biyayya, ba kune zaku mini ba, saboda kuna gamsar da kanku da uwarku, kyale-kyalen duniya fiye da yadda zan yi muku. Dan haka gara na nesanta kaina da ku, tunda ban isa na ce ga yadda za'ayi a gidana ace mini to ba".
Inna da take bakin kofar daki hawayenta ya kasa tsayawa, da sauri ta tsugunna tana cewa "Ka mini hakuri, na yarda na yi kuskure, na yi laifi, ka gafarce Ni, na amince Muutar kaddarar Iya ne, ina fatan ubangiji ya sa karshen bacin ran mu kenan. Ka yi hakuri na ce to, na amince, ka yi yadda kake so da 'yarka".
Dadi ya mamaye zuciyar Baffa ya ce "Na gode miki Salamatu! Ubangiji ya kore shaidanun da suke son tarwatsa mana kyakkawan zaman mu".
Ya kalli Iyah ya ce "A lokacin da na barki ki yi karatun ki, na tabbatar miki bana so, amma na amince miki dan na yarda alfanu ne a gare mu baki'daya. A lokacin na ro'ke ki duk sadda nima zan zo miki da wata bukata ki daure ki mini biyayya ko da ba kya so, sai dan kin san ba zan dora ki akan abu marar alfanu ko cutarwa a gare ki ba".
Kafin ta amsa masa, ya sake zarcewa da fa'din "To yau ina son na roke ki, ki koma dakin ki, burina a duniya bai wuce ace kina dakin mijinki a zaune kin nutsu ba. Mutari shi nake so ya zame miki miji a karo na biyu".
Da rawar murya ta ce "To Baffah! Na ji, na kuma amince zan yi maka biyayya, zan yi ha'kuri na zauna lafiya da shi komai runtsi".
Da murna Baffa ya ke cewa "Na gode miki in sha Allah ba zaki yi nadama ba, ubangiji ya miki Albarka, ya zaunar da ku lafiya, ya baku zuri'a mai albarka".
Ya nisa ya ce " ku shirya gobe zamu je Gogel ki fa'dawa Yaya Ayuba kin amince ba dole na yi miki ba,
Sannan ku samu lokaci ku gano Mutari domin yana jin jiki"
Da sauri lya mike yana cewa "Bari na bi su Alhaji na fa'da musu wannan labarin mai da'di".
Inna ta bi bayansa da ido har ya fice daga gidan, tana ayyana girman soyayyar da yake yiwa Mukhtar.
Kai tsaye gidan Alh Isa ya dosa, a kofar gidan ys tarar da Dr 'Karfi zai shiga mota, ai kuwa ya ce "Mahmouda zo mu shiga, ba tafiya zaka yi ba".
Baffa da murna yake fa'da musu "ai yanzun nan yarinya ta tabbatar masa ta amince, dan haka ku zama cikin shirin zuwa Gogel, a satin nan. Domin a son raina ku tafi da sadaki, a ranar da kuka je a daura auren a huta, kafin ta sake botsarewa saboda na lura kishin banza ta bari yake rinjayar ta".
Daga Baba umaru har Baba Isa kowa ya yi shiru amma suma jinjina alherin bawan Allahn nan suke yi, da karfin son da yake yiwa 'dansu.
Baba Isa ne ya yi karfin halin cewa "Malam Basiru ka dai matsa mata ta amince, gashi muma zamu sake yin son rai, mu amince da abin da ka zartar domin a samu lafiyar yaron nan ta dai-daita, bamu da bakin godiya, abin da zamu ce maka daya ne, da ikon Allah mu kabawa amanar yarinyar nan, mune iyayensa abin da ya faru a farko ba zai sake maimaituwa ba da ikon ubangiji.
Kira mini yarinyar a waya"
Baffa da ya san bashi da fargaba da azama ya fito da wayarsa.
Bugu 'daya ta dauka, ya ce " Baban ku na Na'ibawa ne zai yi magana da ke".
Kalaman kwantar da hankali tare da yabo da kuma girman mai hakuri Alh Isa ya dinga yi Mata, ya sake jaddada mata kar ta sake yin shiru har sai abu ya girmama, komai ya taso matu'kar yafi karfinta to ta sanar da shi zai magance mata da ikon Allah.
Ya rufe maganar da cewa ko kina da korafi domin mun tsayar da kwanaki biyar masu zuwa na daurin auren ku".