Sashe 12
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Nan kuwa mafarkin da ta yi ne ya saukar mata da rashin walwala.
"Allah ya rufa asiri" Baffa ya fa'da yana kallonta, ta amsa da "ameen a takaice.
"Ina tafe da albishir mai dadi wadda na tabbatar zai tsananta jikin nan naki saboda tsananin karfin farin-cikin da zai saukar Miki a zuciya da ma gangar jikin ki gaba'daya".
Ta gyara zama ta ce " Ai kuwa kana da Babban goro fari kal Baffan Iyah".
Da murmushi ya ce "Abin da muka Dade muna addu'a da fatan ya kasance ne zai tabbata bayan mun debe kauna da samunsa".
Zuciyar Innah ta sake takura amma sai ta shanye ta ce "Al'amarin ubangiji ya wuce hakan, yana zartar da komai a sadda ya nufa".
"Baffa ya ce "kwarai kuwa komai nufin Allah ne, bana dai kukanmu ya kare domin ubangiji ya nufa zaman Iyah yana daf da karewa a gabanmu, dazun nan Mutari ya zo mini da wannan albishir din, tun yamman na so na fa'da miki, ganin ki wani iri yasa na ce wannan maganar mai dadice bari na bari sai mun zauna".
Yana rufe baki ta fashe masa da kuka sosai fiye da wadda ta yi akan auren da Mk ya yi. Kuka sosai ta dinga yi, tana ambaton raini ne zaisa Mukhtar ya iya zuwa gabansa ya ce zai mayar da Iyah a yanzu, bayan ya gama wulakanta ta, ya gama cusa musu ba'kin ciki. Ba dan karfin imani ba da yanzu barin jikinta ba ya aiki saboda tsananin tozarcin da Muutar ya yiwa Iyah har da su, shine yanzu da aka samota da kyar zai dawo ya ce zai mayar da ita, saboda yana ganin komai ya ce maka haka zaka yi masa?"
Baffa ya yi shiru yana sauraronta, wannan ne karon farko tun aurensu da ta zauna take fa'da masa magana cikin kara'di da daga murya, kullum harshenta a kasa yake dan haka ya mata uzziri domin ba dabi'arta ba ce.
Ya zuba mata ido yana kallon yadda take kuka sosai tamkar yarinya karama.
Ya ce "Yanzu wannan kukan na menene Salamatu?"
Kai tsaye ta ce "Na ba'kin ciki ne, saboda wallahi na tsani duk abin da zai hada Iyah da Muutar, Jawad ne a tsakanin su ubangiji ya raya shi, amma ni kam na rufe babin wannan yaron mai kafirin ri'ko, da 'Kullaci da kuma rashin ragayya".
"To kuma idan ubangiji bai rufe babinsa da Iyah ba fa? Ya ya zaki yi ne?"
Kafin ta yi magana ya sake cewa na bashi dama ya nemi amincewarta, zan kuma ta ya shi neman yardarta".
Ta kuwa sake fasa kuka tamkar wata sa'ar Iyah.
Ya hassalo ya ce "lallai kin bani Babban goro fari kal Salamatu! na gode miki, amma abin da zan fa'da miki, 'daya ne, Ni ne na haifi Iyah kuma nine wakilinta, ko da shari'a ta bata damar ta zabi wadda ta aminta da shi, a matsayinta na bazawara, Nima kuma shari'ar bata ba ta bata damar yi mini kwangen biyayya ba, dan haka ba zance miki komai a yau ba, sai ta zo gidan nan a gaban ki zan tambayeta ra'ayinta. Da ra'ayin ta zaku ga matsayata".
Haka tsofaffin masoyan suka kwana zuciyoyinsu ba da'di amma Inna ta ta nan kan ba'kanta tana fatan ko zaman mota kar Allah ya sake hada su bare zaman aure, shekaru bakwai yarinya na zaune, sai yanzu tana shirin tsayar da miji zai lallabo ya watsa maneman, kai Muutar ya cika tabbataccen marar kunya, kuma marar mutunci, ta tabbatar zai iya aikata abin da ta gani a mafarkinta sai dai da ikon ubangiji ba da Iyanta ba.
A bangaren Sa'adah kuwa ta shanye murnar dawowar Mk, domin sai da suka zauna da Suamayyah ta sake gane ba 'karamin wauta ta yi ba da ta bari ta ji da'din dawowarsa cikin rayuwarta, domin washagari da zata fita zuwa kotu hawaye Sumayya ta dinga yi tana cewa "Iyah yanzu dai da kike da shekaru talatin da biyu ai ya kamata ace kin fahimci ba abin da mace zata ri'ke a duniya sama da martabarta da 'kimarta. Domin kyau da arziki duk suna samun tawaya, amma idan mace ta ri'ke darajarta to ko da tsufa ya yi wa kyakkawar surarta tawaye wannan 'kimarta da ta ri'ke zata bata kariya. Kar ki bari matsananciyar soyayyar da kike yiwa Mukhtar tasa ki kasa gane a yanzu kinfi bu'katar ki yi daraja a maimakon samun son zuciyar ki.
Sa'adah da take jin magaganun Sumayya har cikin kanta ta dago ta kalleta, sai ta ji a yau tausayin Sumayya ne ya kamata saboda yadda take ganin rauni da wata irin fargaba a kwayar idanuwanta, tana kuma ganin wata irin soyayya da jini kawai ke samar da ita saboda tsananin karfinta da amincinta.
Ta matsa ta rungumeta cikin rawar murya ta ce "Na gode Anti! Ko yau Baffah da Inna suka barmu na san Zan yi kukan rashin ganinsu ne, da kuma adduionsu gare ni, Amma ba na rashin gata ko rashin samun wani abu ba, na tabbatar ubangiji ya zaba mini ke ki zame mini Yar uwa kuma garkuwa domin ya san idan ban samu irin wannan katangar ba zuciya ta tana iya tarwatsewa adalilin jarbawar rayuwata mai zafi ce, Ina tabbatar miki Anty ke ka'dai idan na kalle ki na ga tarin kaunar da kike mini fiye da ta ya'yan cikin sai na yi ta godewa ubangiji domin gatan da ya yi mini mai girma ne".
Suka dinga kuka tamkar anyi musu Rashi ne.
Da kyar suka rabu Sumaayya ta bita har hanyar waje tana fa'din ki rufe dukkan kofofin da kika san Mukhtar zai gan ki, idan kuma kaddara ta sake hada ku, to ki rufe dukkan kofofin da zai ji kayyawan kalmomin bakin ki domin shi din bai cancanta ba, bai dace da ke ba, shekaru bakwai da Kika yi, ba shi kika tsaya jira ya zo ya miki alfarmar mayar da aurenku ba. kin yi wadannan shekarun ne kawai dan gina Goben ki, da samarwa kai nutsuwa.
Sa'adah ta kasa bu'de baki ta yi magana domin kuka ne zai kwace mata mai karfi, saboda kalaman Sumayya tausayi su ke baata.
Tana tafe tana yiwa Sumayya addu'a da dukkan ahalinta tana fatan shakuwa da soyayyar da Jawad da Khairat suke yiwa juna ta bisu har girmansu dan su sake hada zuri'arsu ta zama dunkulalliya.
Tana isa kotun sai ta sake tarar da shari'ar da ta bata mamaki, mahifin Khalil hukumar ya'ki da yiwa kasa zagon kasa da ta'annati wato (E.F.C.C) ta gurfanar domin tuhumarsa da take yi da sama da fa'di da ma'kudan kudaden da ya wawure a lalitar gwamnati a laokcin da yake shugaban maaikatan gwamnati (Head of service).
Ido biyu suka yi da Khali cikin jerin mutanan da suke zaune suna dakon yadda shari'ar zata kaya. Rabon da ta su yi ido da ido idan har lissafinta dai dai ne, shekaru kusan goma sha hudu, tun ranar da suka je partin kammala sakandire a Hang out, ta tuno jidalin da Mk ya yi mata a lokacin. sai dai ta ganshi a hoto, sosai ya girma ya zama zabgegen saurayi na kece raini.
Wani irin abu ya dinga ta so musu dukkansu. Da sauri Sa'a ta wuce gaba inda tawagar lauyoyi suke zaune. Shi kuma ya bita da kallo yana fata iri iri akanta ya kasa daurewa a fili ya ce "Ba zai zama illah dan na auri age mate dina ba, domin har yau din nan da yake da yanmata daban daban yana jin son Gogel din sa, yana tuno moment dinsu kafin kutsen Mk Bichi cikin soyayyar su mai cike da kuruciya da Sanya nisha'di.
Sosai ta yi masa kyau, tafi Halima da ta ke budurwa komai da komai, domin ko a jiya sun hadu tunda basu da nisa . Hula da rigar lauyoyin nan ba karamin kyau da kwarjini suka kara mata ba, ga wani siririn farin glass a Idonta , kamshin ta na turaran Escada sentiment da ya santa da shi tun cikin kuruciya wadda a lokacin na Sumayya take daukowa bata san ma mai daraja bane, yauma kamshin ya shaka, tabbacin har yau da shi take tu'amalli.
A yanzu mahaifin Khalil Sanata ne mai ci, Dan haka yan adawa suka dinga rubuce rubuce akansa har sai da suka ja hankalin hukimar E.F.C.C ta damke shi, wata biyu ana ta dauki ba da'di tunda shi ya kafe ya'ki daukar lauya, ya kuma hana a daukar masa, da yake yana da kyakkawan alaka da gwamnatin jahar Kano sai ta bashi lauyoyi har guda biyar dan su tsaya masa, tunda mai girma gwamna da kansa ya gamsu Hon Ibrahim Hassan bai ci wannan kudaden da ake ambatonsu ba.
Manyan kwarrarun lauyoyi har guda uku masu mukamin (S.A.N.) sai guda biyu 'kananu amma hazi'kai, Bar Sa'adatu Bashir Gogel da Bar Mustafa Isa Gwaram.
"Allah ya rufa asiri" Baffa ya fa'da yana kallonta, ta amsa da "ameen a takaice.
"Ina tafe da albishir mai dadi wadda na tabbatar zai tsananta jikin nan naki saboda tsananin karfin farin-cikin da zai saukar Miki a zuciya da ma gangar jikin ki gaba'daya".
Ta gyara zama ta ce " Ai kuwa kana da Babban goro fari kal Baffan Iyah".
Da murmushi ya ce "Abin da muka Dade muna addu'a da fatan ya kasance ne zai tabbata bayan mun debe kauna da samunsa".
Zuciyar Innah ta sake takura amma sai ta shanye ta ce "Al'amarin ubangiji ya wuce hakan, yana zartar da komai a sadda ya nufa".
"Baffa ya ce "kwarai kuwa komai nufin Allah ne, bana dai kukanmu ya kare domin ubangiji ya nufa zaman Iyah yana daf da karewa a gabanmu, dazun nan Mutari ya zo mini da wannan albishir din, tun yamman na so na fa'da miki, ganin ki wani iri yasa na ce wannan maganar mai dadice bari na bari sai mun zauna".
Yana rufe baki ta fashe masa da kuka sosai fiye da wadda ta yi akan auren da Mk ya yi. Kuka sosai ta dinga yi, tana ambaton raini ne zaisa Mukhtar ya iya zuwa gabansa ya ce zai mayar da Iyah a yanzu, bayan ya gama wulakanta ta, ya gama cusa musu ba'kin ciki. Ba dan karfin imani ba da yanzu barin jikinta ba ya aiki saboda tsananin tozarcin da Muutar ya yiwa Iyah har da su, shine yanzu da aka samota da kyar zai dawo ya ce zai mayar da ita, saboda yana ganin komai ya ce maka haka zaka yi masa?"
Baffa ya yi shiru yana sauraronta, wannan ne karon farko tun aurensu da ta zauna take fa'da masa magana cikin kara'di da daga murya, kullum harshenta a kasa yake dan haka ya mata uzziri domin ba dabi'arta ba ce.
Ya zuba mata ido yana kallon yadda take kuka sosai tamkar yarinya karama.
Ya ce "Yanzu wannan kukan na menene Salamatu?"
Kai tsaye ta ce "Na ba'kin ciki ne, saboda wallahi na tsani duk abin da zai hada Iyah da Muutar, Jawad ne a tsakanin su ubangiji ya raya shi, amma ni kam na rufe babin wannan yaron mai kafirin ri'ko, da 'Kullaci da kuma rashin ragayya".
"To kuma idan ubangiji bai rufe babinsa da Iyah ba fa? Ya ya zaki yi ne?"
Kafin ta yi magana ya sake cewa na bashi dama ya nemi amincewarta, zan kuma ta ya shi neman yardarta".
Ta kuwa sake fasa kuka tamkar wata sa'ar Iyah.
Ya hassalo ya ce "lallai kin bani Babban goro fari kal Salamatu! na gode miki, amma abin da zan fa'da miki, 'daya ne, Ni ne na haifi Iyah kuma nine wakilinta, ko da shari'a ta bata damar ta zabi wadda ta aminta da shi, a matsayinta na bazawara, Nima kuma shari'ar bata ba ta bata damar yi mini kwangen biyayya ba, dan haka ba zance miki komai a yau ba, sai ta zo gidan nan a gaban ki zan tambayeta ra'ayinta. Da ra'ayin ta zaku ga matsayata".
Haka tsofaffin masoyan suka kwana zuciyoyinsu ba da'di amma Inna ta ta nan kan ba'kanta tana fatan ko zaman mota kar Allah ya sake hada su bare zaman aure, shekaru bakwai yarinya na zaune, sai yanzu tana shirin tsayar da miji zai lallabo ya watsa maneman, kai Muutar ya cika tabbataccen marar kunya, kuma marar mutunci, ta tabbatar zai iya aikata abin da ta gani a mafarkinta sai dai da ikon ubangiji ba da Iyanta ba.
A bangaren Sa'adah kuwa ta shanye murnar dawowar Mk, domin sai da suka zauna da Suamayyah ta sake gane ba 'karamin wauta ta yi ba da ta bari ta ji da'din dawowarsa cikin rayuwarta, domin washagari da zata fita zuwa kotu hawaye Sumayya ta dinga yi tana cewa "Iyah yanzu dai da kike da shekaru talatin da biyu ai ya kamata ace kin fahimci ba abin da mace zata ri'ke a duniya sama da martabarta da 'kimarta. Domin kyau da arziki duk suna samun tawaya, amma idan mace ta ri'ke darajarta to ko da tsufa ya yi wa kyakkawar surarta tawaye wannan 'kimarta da ta ri'ke zata bata kariya. Kar ki bari matsananciyar soyayyar da kike yiwa Mukhtar tasa ki kasa gane a yanzu kinfi bu'katar ki yi daraja a maimakon samun son zuciyar ki.
Sa'adah da take jin magaganun Sumayya har cikin kanta ta dago ta kalleta, sai ta ji a yau tausayin Sumayya ne ya kamata saboda yadda take ganin rauni da wata irin fargaba a kwayar idanuwanta, tana kuma ganin wata irin soyayya da jini kawai ke samar da ita saboda tsananin karfinta da amincinta.
Ta matsa ta rungumeta cikin rawar murya ta ce "Na gode Anti! Ko yau Baffah da Inna suka barmu na san Zan yi kukan rashin ganinsu ne, da kuma adduionsu gare ni, Amma ba na rashin gata ko rashin samun wani abu ba, na tabbatar ubangiji ya zaba mini ke ki zame mini Yar uwa kuma garkuwa domin ya san idan ban samu irin wannan katangar ba zuciya ta tana iya tarwatsewa adalilin jarbawar rayuwata mai zafi ce, Ina tabbatar miki Anty ke ka'dai idan na kalle ki na ga tarin kaunar da kike mini fiye da ta ya'yan cikin sai na yi ta godewa ubangiji domin gatan da ya yi mini mai girma ne".
Suka dinga kuka tamkar anyi musu Rashi ne.
Da kyar suka rabu Sumaayya ta bita har hanyar waje tana fa'din ki rufe dukkan kofofin da kika san Mukhtar zai gan ki, idan kuma kaddara ta sake hada ku, to ki rufe dukkan kofofin da zai ji kayyawan kalmomin bakin ki domin shi din bai cancanta ba, bai dace da ke ba, shekaru bakwai da Kika yi, ba shi kika tsaya jira ya zo ya miki alfarmar mayar da aurenku ba. kin yi wadannan shekarun ne kawai dan gina Goben ki, da samarwa kai nutsuwa.
Sa'adah ta kasa bu'de baki ta yi magana domin kuka ne zai kwace mata mai karfi, saboda kalaman Sumayya tausayi su ke baata.
Tana tafe tana yiwa Sumayya addu'a da dukkan ahalinta tana fatan shakuwa da soyayyar da Jawad da Khairat suke yiwa juna ta bisu har girmansu dan su sake hada zuri'arsu ta zama dunkulalliya.
Tana isa kotun sai ta sake tarar da shari'ar da ta bata mamaki, mahifin Khalil hukumar ya'ki da yiwa kasa zagon kasa da ta'annati wato (E.F.C.C) ta gurfanar domin tuhumarsa da take yi da sama da fa'di da ma'kudan kudaden da ya wawure a lalitar gwamnati a laokcin da yake shugaban maaikatan gwamnati (Head of service).
Ido biyu suka yi da Khali cikin jerin mutanan da suke zaune suna dakon yadda shari'ar zata kaya. Rabon da ta su yi ido da ido idan har lissafinta dai dai ne, shekaru kusan goma sha hudu, tun ranar da suka je partin kammala sakandire a Hang out, ta tuno jidalin da Mk ya yi mata a lokacin. sai dai ta ganshi a hoto, sosai ya girma ya zama zabgegen saurayi na kece raini.
Wani irin abu ya dinga ta so musu dukkansu. Da sauri Sa'a ta wuce gaba inda tawagar lauyoyi suke zaune. Shi kuma ya bita da kallo yana fata iri iri akanta ya kasa daurewa a fili ya ce "Ba zai zama illah dan na auri age mate dina ba, domin har yau din nan da yake da yanmata daban daban yana jin son Gogel din sa, yana tuno moment dinsu kafin kutsen Mk Bichi cikin soyayyar su mai cike da kuruciya da Sanya nisha'di.
Sosai ta yi masa kyau, tafi Halima da ta ke budurwa komai da komai, domin ko a jiya sun hadu tunda basu da nisa . Hula da rigar lauyoyin nan ba karamin kyau da kwarjini suka kara mata ba, ga wani siririn farin glass a Idonta , kamshin ta na turaran Escada sentiment da ya santa da shi tun cikin kuruciya wadda a lokacin na Sumayya take daukowa bata san ma mai daraja bane, yauma kamshin ya shaka, tabbacin har yau da shi take tu'amalli.
A yanzu mahaifin Khalil Sanata ne mai ci, Dan haka yan adawa suka dinga rubuce rubuce akansa har sai da suka ja hankalin hukimar E.F.C.C ta damke shi, wata biyu ana ta dauki ba da'di tunda shi ya kafe ya'ki daukar lauya, ya kuma hana a daukar masa, da yake yana da kyakkawan alaka da gwamnatin jahar Kano sai ta bashi lauyoyi har guda biyar dan su tsaya masa, tunda mai girma gwamna da kansa ya gamsu Hon Ibrahim Hassan bai ci wannan kudaden da ake ambatonsu ba.
Manyan kwarrarun lauyoyi har guda uku masu mukamin (S.A.N.) sai guda biyu 'kananu amma hazi'kai, Bar Sa'adatu Bashir Gogel da Bar Mustafa Isa Gwaram.