Sashe 21
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jawad ya kalle shi da mamaki! ya ga seriousness a fuskar Baban nasa ya kasa gasggatawa ya ce " please Malam are you serious, are u sure?"
Da sauri Mk ya kada kai ya ce very sure Babana! Yanzu zamu je gida kaa ci abin da Anti ta shirya maka, daga nan sai mu zo ka gaida Hajiya, sai mu koma ka kwana tare da mu, tomorrow morning da kaina zan kaika gidan Baffah ko gidan Anty Sumayya ko ina kake so nan zaka je".
Ya dinga murmushi irin murmushin Sa'adah, wurshiryar da ya samu daga gareta ya sake kawata murmushin nasa".
Da farin ciki sosai Mk ya ce "kyaun ka na bayyana idan kana smiling my boy".
Jawad ya sa hannunsa ya rufe fuskarsa wai shi kunya.
Da murna sosai Farida ta karbi Jawad ta dinga ina ka saka da shi, karshe ya shige dakinsa da komai na ciki blue ne, irin kayan alatun da aka shirya masa duk dan a hilace shi ya daina gudun gidan basu yi tasiri ba.
Wanka ya yi, ya shirya ya fito ya tarar da kayayyakin da aka tanada dan shi kala kala.
Farida ta dinga rawar jikin kyautata masa adalilin taga sassauci a tare da shi fiye da wattannin baya da ko kallon inda take ba kaunar ya yi. Ta ji farin-cikin sauyin da ta gani a tare da yaron.
Sai yamma lis suka fice da Babansa.
Basu dawo gidan ba sai dare sosai domin har sai da Jawad ya yi barci a dakin Hajiya.
Da ya zo yana tashinsa Hajiya ta ce
"Barshi mana tunda ya yi barci".
Da sauri ya ce " A a Hajiya bari kawai mu tafi lalla'ba shi nake yi ya daina gudun Farida, ta dora hankalinta akansa, amma yana gudunta tamkar kunama, yau dai na ga ya fara saukowa, gobe zan kai shi wurin uwarsa dan hankalinsa ya kwanta".
Hajiya ta ce "dan hankalinsa ya kwanta, ko dan ka samu dalilin ganin uwarsa babu hijabi?"
Mk ya ce "haba Hajiya"
"Haba Hajiya ko dai haba gaskiya?"
Washagari kuwa ya kai shi gidan da tarin tsaraba Niki niki tamkar wadda zai shekara, har da cake dinsa na murnar dawowar sa gida, bai ci ba, Mk ya ce ya taho da abinsa. har cikin gidan Mk ya shiga ya tarar da Innah na yin wainar shinkafa irin ta garin su Shafa'atun Bauchi ko da yake itama Innar ai daga Gamawa take kenan Inna Yar Bauchi ce. Sa'a na kicin na hada miyar cin masar.
Ya dinga tuno yadda Sa'adah take yi masa waina da miyar ganye da yake santi, haka nan ya yi kewar dambunta, ya yi kewar farfesu mai daddawa, ya yi kewar kunun danyar gyada da shinkafa, da alkubus. Traditional dishes da ya yi kewar su ba za su lissafu ba, hatta shinkafa da wake har yau bai sake cin mai gardin ta Sa'adah ba. Haka nan kwa'don zogale da Rama. Yana matu'kar jinjinawa Inna yadda ta horar da Sa'adah nau'in abinci kala, kala masu dan karen 'dan'dano da kashe kowacce irin yunwa, ga kara lafiya.
Sa'a tana jinsu ta rakube, ko kwakkwaran motsi ta ki yi dan kar a hangota.
Baffa ya fito yana marabatarsu, yayin da hankalin uba da 'da ya karkata a son ganin Iyah.
Lura da hakan da Baffah ya yi yasa ya kirata, ta fito sanye da doguwar riga ta atamfa, dinkin free ne amma ya matu'kar yin kyau.
Da sauri Jawad ya ruga ya rungumeta yana fa'din "Daure ki gwada daga ni sama Mami".
Baffah ya yi saurin cewa "wannan shine gangan Jawad, a gabana ka ke son ka kayar mini da uwa?"
Mk ya murmusa ba tare da ya ce komai ba, bagarar da shi da Inna ta tsiri yi masa na matu'kar damunsa.
Duk yadda Inna take jin haushin Mk bai hana ta zuba masa waina ba, ta zuba masa masar a ledar ta sake kara wata ledar, ta mike ta dauko flask ta shiga kicin ta zubo miya, ta kawo ta ajiye masa a gabansa, a hankali ta ce ga waina, ta koma ta cigaba da aikinta.
Baffah kuwa fa'di yake "wannan tafiya zai yi da shi zubo masa wadda zai ci yanzu"
Da sauri Mk ya ce "Na riga da na karya, na gode, a ransa kuma fa'di yake yaushe zan iya cin abinci a gaban ku?"
Idon Baffa ya sa Sa'adah cewa Mk "Ina kwana".
Ya amsa da sauri, cike da walwala.
Ta shige dakinta Jawad ya bita, ya kwanta a shimfidarta, yana cewa "I miss your scent, I missed everything about you my Iyah".
Ta ce "Ashe ban hanaka fa'dar Iyan nan ba?"
Ya turo baki irin yadda ta ke yi ya ce "Iyah means mother, means uwa, Mami da Iyah all the same".
Ta ce "To dai ban son sunan a bakinka barwa Baffa da Innah kawai".
Mk suka fita tare da Baffah! Jawad ya fito da sauri ya bisu, daga kofar gida Baffa ya wuce inda za shi, yayin da su kuma suka tsallaka zuwa shagon Mk .
Jawad ya yi mamakin yadda aka sake kawata shagon, komai na wurin na zamani ne, ya zauna yana cewa " Azo a wanke mini kafata".
Harara Mk ya galla masa ya ce " Saminu ba ya nan, ina fatan ba Uncle Akil kake nufi ya wanke maka kafar ba?".
Jawad ya yi shiru! Yayin da Mk ya zarce da fa'din, kullum ana idar da Sallar la'asar ka tabbatar ka zo nan kana koyon aiki, zan fa'dawa Akil duk ranar da baka zo ba, ya yi dealing dinka well well, kasan dai shi no nonsense ne baya wasa da yara, ba kamar Uncle Abbas bane da yake yi muku yadda kuke so".
Jawad ya nisa ya ce"Malam ni bazan iya yiwa mutum aski ko wanke kafa ba, zan bata jikina ne kawai".
Mk ya zuba masa ido yana kare masa kallo, a zahiri dai yaron kamarsa ya yi, amma dabi'unsa sak na uwarsa ne, gayu da pride dinsa na Sa'adah ne.
Ya daure fuska sosai ya ce "Jawad ai baka kai a baka yin aski ko wankin kafa bama tukun, share wurin zaka dinga yi, kana wanke towels din da aka yi amfani da su, sannan ka dinga ganin yadda ake gudanar da aikin".
Ya shagwabe fuska ya ce"Haba mana Malam a shagonka zan dinga irin wannan wahalar?"
Mamaki ya kama Mk amma da yake yasan a iya shekarun Jawad da iya tunaninsa shi hakan abin kunya ne, a gurinsa.
Sai ya sassauta ya ce, "Jawad Ni dai a tarihin Nigeria ban taba ganin wadda ya yi karatu mai zurfi ya mallaki jirgin sama ba, Amma na san yan kasuwa da suka fara da kananun business, a hankali business din y tunbatsa har suka sayi jirgin sama. Na san kai kuma burinka ka samu damar siyan jirgi, fa'da mini idan ba ka koyi business ba, how ur dreams will be reality one day?"
"To zan dinga zuwa, amma plz Malam! tell Uncle Akil to be gentle, I really dislike his hershness"
Mk ya sake daure fuska sosai ya kafe shi da Ido, har sai da Jawad ya dinga jin wani irin abu na ratsa shi, ya sunkuyar da idonsa kasa ya ce " very sorry Malam".
Mk ya nisa ya ce "Akil din ka ke fa'din haka akansa? Kanina, kanina Jawad? ashe kuwa nima na shirya, domin Ni da shi ai daya ne a gunka! Ko Ahamad da yake karamin mu ban za ci zaka iya fa'dar wani abu da bai maka a tare da shi ba".
Ya ru'ko hannun Mk ya ce "ba zan sake ba Malam! Plz forgive and forgot".
Ya na fada yana leka waje, yana fatan Akil din bai iso ya ji me ya ce ba".
Mk ya ce daina ma wani lekawa dan kuwa zan fada masa.
Nan da nan kuwa ya fara kuka yana fa'din sorry Malam, ya tsorata sosai, domin Akil mala'ikan Yara ne, baya musu ta Dadi shine discipline master a family din nasu.
"Ok stop crying! Ba zan fa'da ba, amma idan ka sake, ko idan ka zo ka ga baya shago ka ce zaka dinga yiwa su Saminu rudeness to ka tabbatar zai ji komai".
Ya goge fuskar sa yana fa'din " Thank you! Komai suka ce na yi, yi kawai zan yi".
Mk ya ru'ko shi yana fa'din "good boy! Sannan islamiyar nan ta safe zaka dinga zuwa. 9 ake faraawa, a tashi 1pm.
*A samarwa Yara lokacin da zasu dinga zuwa wurin koyon sana'a domin hakan zaisa su taso da burin tsayuwa akan kafafuwansu, zai rage musu burin su kammala digirin farko su zauna zaman jiran gwamnati ta basu abin yi, lokaci ya yi da zamu daina yaudarar kanmu cewa gwamnati zata iya WADATAR da kowa*.
Haka kwanaki suka dinga shudewa, har shari'ar mahaifin Khalil ta zagayo, aka yi ta cakudawa bisa taimakon lauyoyinsa mussaman Sa'adah suka samu kotu ta bada belinsa, bayan sun kawo wadda kotu ta bu'kata a matsayin sharudda.
Kotu ta sake zabar ranar 28/08 a matsayin ranar yanke hukunci na karshe.
Wannan shari'a ta matu'kar Jan hankalin yan siya domin gaba'daya al'amarin siyasa ne, belin da ya samu ya matu'kar daga darajar lauyoyinsa mussaman Sa'adah da ta kasance mace tilo, duka shafin jaridun kasar nan shafin farko sai ka tsinci hoton Sanata Ibrahim Hassan da lauyoyinsa.
Mk da ya tsinci hoton Sa'adah a tsakanin manyan lauyoyi gefe kuma ga mahaifin Khalil sai ya ji tamkar ya shide dan tsananin takaici.
Da sauri Mk ya kada kai ya ce very sure Babana! Yanzu zamu je gida kaa ci abin da Anti ta shirya maka, daga nan sai mu zo ka gaida Hajiya, sai mu koma ka kwana tare da mu, tomorrow morning da kaina zan kaika gidan Baffah ko gidan Anty Sumayya ko ina kake so nan zaka je".
Ya dinga murmushi irin murmushin Sa'adah, wurshiryar da ya samu daga gareta ya sake kawata murmushin nasa".
Da farin ciki sosai Mk ya ce "kyaun ka na bayyana idan kana smiling my boy".
Jawad ya sa hannunsa ya rufe fuskarsa wai shi kunya.
Da murna sosai Farida ta karbi Jawad ta dinga ina ka saka da shi, karshe ya shige dakinsa da komai na ciki blue ne, irin kayan alatun da aka shirya masa duk dan a hilace shi ya daina gudun gidan basu yi tasiri ba.
Wanka ya yi, ya shirya ya fito ya tarar da kayayyakin da aka tanada dan shi kala kala.
Farida ta dinga rawar jikin kyautata masa adalilin taga sassauci a tare da shi fiye da wattannin baya da ko kallon inda take ba kaunar ya yi. Ta ji farin-cikin sauyin da ta gani a tare da yaron.
Sai yamma lis suka fice da Babansa.
Basu dawo gidan ba sai dare sosai domin har sai da Jawad ya yi barci a dakin Hajiya.
Da ya zo yana tashinsa Hajiya ta ce
"Barshi mana tunda ya yi barci".
Da sauri ya ce " A a Hajiya bari kawai mu tafi lalla'ba shi nake yi ya daina gudun Farida, ta dora hankalinta akansa, amma yana gudunta tamkar kunama, yau dai na ga ya fara saukowa, gobe zan kai shi wurin uwarsa dan hankalinsa ya kwanta".
Hajiya ta ce "dan hankalinsa ya kwanta, ko dan ka samu dalilin ganin uwarsa babu hijabi?"
Mk ya ce "haba Hajiya"
"Haba Hajiya ko dai haba gaskiya?"
Washagari kuwa ya kai shi gidan da tarin tsaraba Niki niki tamkar wadda zai shekara, har da cake dinsa na murnar dawowar sa gida, bai ci ba, Mk ya ce ya taho da abinsa. har cikin gidan Mk ya shiga ya tarar da Innah na yin wainar shinkafa irin ta garin su Shafa'atun Bauchi ko da yake itama Innar ai daga Gamawa take kenan Inna Yar Bauchi ce. Sa'a na kicin na hada miyar cin masar.
Ya dinga tuno yadda Sa'adah take yi masa waina da miyar ganye da yake santi, haka nan ya yi kewar dambunta, ya yi kewar farfesu mai daddawa, ya yi kewar kunun danyar gyada da shinkafa, da alkubus. Traditional dishes da ya yi kewar su ba za su lissafu ba, hatta shinkafa da wake har yau bai sake cin mai gardin ta Sa'adah ba. Haka nan kwa'don zogale da Rama. Yana matu'kar jinjinawa Inna yadda ta horar da Sa'adah nau'in abinci kala, kala masu dan karen 'dan'dano da kashe kowacce irin yunwa, ga kara lafiya.
Sa'a tana jinsu ta rakube, ko kwakkwaran motsi ta ki yi dan kar a hangota.
Baffa ya fito yana marabatarsu, yayin da hankalin uba da 'da ya karkata a son ganin Iyah.
Lura da hakan da Baffah ya yi yasa ya kirata, ta fito sanye da doguwar riga ta atamfa, dinkin free ne amma ya matu'kar yin kyau.
Da sauri Jawad ya ruga ya rungumeta yana fa'din "Daure ki gwada daga ni sama Mami".
Baffah ya yi saurin cewa "wannan shine gangan Jawad, a gabana ka ke son ka kayar mini da uwa?"
Mk ya murmusa ba tare da ya ce komai ba, bagarar da shi da Inna ta tsiri yi masa na matu'kar damunsa.
Duk yadda Inna take jin haushin Mk bai hana ta zuba masa waina ba, ta zuba masa masar a ledar ta sake kara wata ledar, ta mike ta dauko flask ta shiga kicin ta zubo miya, ta kawo ta ajiye masa a gabansa, a hankali ta ce ga waina, ta koma ta cigaba da aikinta.
Baffah kuwa fa'di yake "wannan tafiya zai yi da shi zubo masa wadda zai ci yanzu"
Da sauri Mk ya ce "Na riga da na karya, na gode, a ransa kuma fa'di yake yaushe zan iya cin abinci a gaban ku?"
Idon Baffa ya sa Sa'adah cewa Mk "Ina kwana".
Ya amsa da sauri, cike da walwala.
Ta shige dakinta Jawad ya bita, ya kwanta a shimfidarta, yana cewa "I miss your scent, I missed everything about you my Iyah".
Ta ce "Ashe ban hanaka fa'dar Iyan nan ba?"
Ya turo baki irin yadda ta ke yi ya ce "Iyah means mother, means uwa, Mami da Iyah all the same".
Ta ce "To dai ban son sunan a bakinka barwa Baffa da Innah kawai".
Mk suka fita tare da Baffah! Jawad ya fito da sauri ya bisu, daga kofar gida Baffa ya wuce inda za shi, yayin da su kuma suka tsallaka zuwa shagon Mk .
Jawad ya yi mamakin yadda aka sake kawata shagon, komai na wurin na zamani ne, ya zauna yana cewa " Azo a wanke mini kafata".
Harara Mk ya galla masa ya ce " Saminu ba ya nan, ina fatan ba Uncle Akil kake nufi ya wanke maka kafar ba?".
Jawad ya yi shiru! Yayin da Mk ya zarce da fa'din, kullum ana idar da Sallar la'asar ka tabbatar ka zo nan kana koyon aiki, zan fa'dawa Akil duk ranar da baka zo ba, ya yi dealing dinka well well, kasan dai shi no nonsense ne baya wasa da yara, ba kamar Uncle Abbas bane da yake yi muku yadda kuke so".
Jawad ya nisa ya ce"Malam ni bazan iya yiwa mutum aski ko wanke kafa ba, zan bata jikina ne kawai".
Mk ya zuba masa ido yana kare masa kallo, a zahiri dai yaron kamarsa ya yi, amma dabi'unsa sak na uwarsa ne, gayu da pride dinsa na Sa'adah ne.
Ya daure fuska sosai ya ce "Jawad ai baka kai a baka yin aski ko wankin kafa bama tukun, share wurin zaka dinga yi, kana wanke towels din da aka yi amfani da su, sannan ka dinga ganin yadda ake gudanar da aikin".
Ya shagwabe fuska ya ce"Haba mana Malam a shagonka zan dinga irin wannan wahalar?"
Mamaki ya kama Mk amma da yake yasan a iya shekarun Jawad da iya tunaninsa shi hakan abin kunya ne, a gurinsa.
Sai ya sassauta ya ce, "Jawad Ni dai a tarihin Nigeria ban taba ganin wadda ya yi karatu mai zurfi ya mallaki jirgin sama ba, Amma na san yan kasuwa da suka fara da kananun business, a hankali business din y tunbatsa har suka sayi jirgin sama. Na san kai kuma burinka ka samu damar siyan jirgi, fa'da mini idan ba ka koyi business ba, how ur dreams will be reality one day?"
"To zan dinga zuwa, amma plz Malam! tell Uncle Akil to be gentle, I really dislike his hershness"
Mk ya sake daure fuska sosai ya kafe shi da Ido, har sai da Jawad ya dinga jin wani irin abu na ratsa shi, ya sunkuyar da idonsa kasa ya ce " very sorry Malam".
Mk ya nisa ya ce "Akil din ka ke fa'din haka akansa? Kanina, kanina Jawad? ashe kuwa nima na shirya, domin Ni da shi ai daya ne a gunka! Ko Ahamad da yake karamin mu ban za ci zaka iya fa'dar wani abu da bai maka a tare da shi ba".
Ya ru'ko hannun Mk ya ce "ba zan sake ba Malam! Plz forgive and forgot".
Ya na fada yana leka waje, yana fatan Akil din bai iso ya ji me ya ce ba".
Mk ya ce daina ma wani lekawa dan kuwa zan fada masa.
Nan da nan kuwa ya fara kuka yana fa'din sorry Malam, ya tsorata sosai, domin Akil mala'ikan Yara ne, baya musu ta Dadi shine discipline master a family din nasu.
"Ok stop crying! Ba zan fa'da ba, amma idan ka sake, ko idan ka zo ka ga baya shago ka ce zaka dinga yiwa su Saminu rudeness to ka tabbatar zai ji komai".
Ya goge fuskar sa yana fa'din " Thank you! Komai suka ce na yi, yi kawai zan yi".
Mk ya ru'ko shi yana fa'din "good boy! Sannan islamiyar nan ta safe zaka dinga zuwa. 9 ake faraawa, a tashi 1pm.
*A samarwa Yara lokacin da zasu dinga zuwa wurin koyon sana'a domin hakan zaisa su taso da burin tsayuwa akan kafafuwansu, zai rage musu burin su kammala digirin farko su zauna zaman jiran gwamnati ta basu abin yi, lokaci ya yi da zamu daina yaudarar kanmu cewa gwamnati zata iya WADATAR da kowa*.
Haka kwanaki suka dinga shudewa, har shari'ar mahaifin Khalil ta zagayo, aka yi ta cakudawa bisa taimakon lauyoyinsa mussaman Sa'adah suka samu kotu ta bada belinsa, bayan sun kawo wadda kotu ta bu'kata a matsayin sharudda.
Kotu ta sake zabar ranar 28/08 a matsayin ranar yanke hukunci na karshe.
Wannan shari'a ta matu'kar Jan hankalin yan siya domin gaba'daya al'amarin siyasa ne, belin da ya samu ya matu'kar daga darajar lauyoyinsa mussaman Sa'adah da ta kasance mace tilo, duka shafin jaridun kasar nan shafin farko sai ka tsinci hoton Sanata Ibrahim Hassan da lauyoyinsa.
Mk da ya tsinci hoton Sa'adah a tsakanin manyan lauyoyi gefe kuma ga mahaifin Khalil sai ya ji tamkar ya shide dan tsananin takaici.