Sashe 36
Halin Yau Part 3 Complete Hausa Novel · about 10 min read
Suka dinga sakin ajiyar zuciya! Ya dinga rada mata "Hold me tied please".
Amma Sa'a ta kasa yin komai, saboda rashin sukunin zuciya.
Tana jin yadda ya gyra kwanciyarsa ya fara laluben kirjinta da bakinsa, kan dole ta kyale shi ya zama tamkar sabon jariri saboda yadda yake tsotsar su.
Jikinta gaba'daya ya amsa, sai tsuma take yi, shi kuma rashin 'karfin jikinsa ya masa cikas din tafiya second round ko da ta 'karfi ne kuwa irin na daren jiya. A hakan da suke barci ya yi awon gaba da su.
9:18am dai dai Sa'a ta bude idonta, har lokacin kuma Mk barcinsa yake cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Fuskarsa na manne da kirjinta sai ka rantse baya samun iskar zukar numfashi.
A hankali ta zare jikinta, ta mayar masa da filo gurbinta, kamar yadda take yi masa a baya.
Bata tsaya a ko'ina ba sai a bayi, kai-tsaye ruwa mai zafi ta ha'da, ta yi wanka sosai, ta fito, ta shirya cikin matsakaiciyar kwalliya, ta zauna akan stool ta kasa daura dankwali saboda yadda take jin tsananin yunwa.
Bata son tashinsa, gashi kuma ji take tamkar ta ci babu saboda tsananin yadda cikinta yake yi mata karta.
Ta dauko hijabinta ta saka, ta dauko jakarta, ta nufi kofa da nufin fita ta nemi abinci.
Ta bude kofar kenan ya tashi, da azama ya ce "Ina zaki?"
Ta dawo da sauri ta ce "yunwa nake ji, tamkar an mini yasa a ciki".
Ya bata rai sosai ya ce "shine dalilin da zaki dauki hijab ki fita babu izni, alhalin kina kallona, Wai ke wanni irin raini kika mini ne? Ke ce zaki fita siyan abinci? Karatun naki abinda ya koya miki kenan?"
Ta yi shiru, ta kasa cewa komai. Idonta ya ciko da kwalla.
Ya ja tsaki ya mike ya shige bayi.
Bai wani jima ba ya fito, amma ita sai ta ga tamkar ya kusan awa guda.
Jallabiya ya zura ya dauko wallet din sa ya fice.
Mintina Kamar biyar, ya dawo dauke da ledoji a hannunsa.
Ya tarar da ita tana kan stool din mirror tana faman goge hawaye da tissue.
Ya ajiye ledar a gabanta ya ce "gashi sauko ki ci".
Ta yi tamkar ba ta ji shi ba, shikuma ya shige bayi, ya fara wanka.
Amma da yake yunwa ba kanwar uwa ba ce, sai ta sauko, ta hau duba ledar.
Leda daya dankalin turawa da kwai ne, 'dayar kuma doyace da aka soyata cikin kwai. Sai kuma leda mai dauke da daurin kunu biyu, na gyada da na tsamiya.
Doyar ta hau ci a yunwace, kafin ya fito ta cinye tass, sai ragowan kunun tsamiya a hannunta da take shirin zuke shi.
Sai da ya shirya, sannan ya zauna yana cewa "yanzu duk doyar nan kin cinye ke ka'dai, yaushe kika zama mai cin abinci haka? "
Takaici yasa ta cigaba da matso kwalla ta na gogewa, shikuma ya hau cin abincinsa hankali kwance, yana jin wani irin shau'ki. Bai san me yasa iskancin Sa'a ke tafiya da shi ba, ya lura a yanzu bata da burin kayayyakin 'kawa, ba ta harkar kawaye, cikin dabi'unta masu Muni kaifin harshe ne ya rage mata, shima kuma dole ta rage indai tana gabansa.
Amma sakalci, sai ya ga tamkar tana girma, yana sake bin jikinta ne. Ya tabbatar har kukanta yana jerin abubawan da yake kewarsu.
Sai da ya kammala ya dubeta ya ce " ke kam kin ji kunya wallahi! Ai bai kamata ki tisa ni gaba kina mini kukan shagwaba ba, tunda dai jiya ba irin ro'kon da ban miki akan ki taimake ni ki mini abin da zan samu nutsuwa, amma ki kika shafawa idonki toka. Sai dai kuma na nuna miki ba zanci gaba da zuba miki ido kina mini iyashege ba. Da ace kin ji rarrashin da na miki, da kin ga yadda zan tarairaye ki, na lallashe ki, amma yanzu ko bubburwa zaki yi ba ruwana da ke, bare na san kina sakalcin banza".
Da rawar murya irin tana gaf da fashewa da kuka ta ce "kin yarda da na yi da kai ya isa ka gane sonka ne ba na yi, haka karfin da ka gwada mini, da har yanzu nake Jin ciwo a inda ka bubbbga mini guiwar hannunka ya almata mini kaima sha'awa ta kawai kake yi, amma ba so ba".
"Eh bana son ki".
Ya bata amsa a ta'kaice.
Ba'kin ciki ya turniketa ta ce "Allah ya kawo zazzabi anjima zaka gane lalle nima bana sonka".
Ya ma'ke kafada ya ce "Ameen! Ciwo na kan kowa, nawa ya yi kyau ai. Kema kuma na ki na tafe, domin ciwo ai ba a fatansa, idan yau kaine, gobe na ga waninka. Idan ubangiji ya juya abin ya dawo kanki, a lokacin zaki gane tsiyar ki ka'dan ce".
Ya mike ya na cewa "To ni kam dama kwanaki uku iyalina ta san zan yi. Yau kam ko hayar direban da zai tuka ni zuwa Kano, zan yi, bare kuma Ina fatan ubangiji ya bani ikon tukin da kaina.
Don bana cikin mutane masu yiwa masoyansu 'karya ko butulci, ko danne musu hakkin su".
Zuciyarta ta buga da tsananin gaske, ta san shagube ya yi mata, sannan kai tsaye yake nuna mata yau gurin Farida zai kwana, domin kwana ukun da ta bashi ya cika.
Haka suka dawo Kano, ba wani jituwa a tsakanin su.
Ya sauketa a kofar gidansu ya ja motarsa ya yi gaba.
Tunda ya ajiyeta yake jin tamkar ya rusa ihu, shi dai ko zasu kwana suna Yar tsama yafi son ya ganta a kusa da shi, ko da ba zata kula shi ba, haka nan shima ko ba zai mata maganar ba, amma dai ya ganta kusa da shi shine samun nutsuwarsa, ko shareta da yake yi, Karfin hali kawai yake yi da son kwatar kansa a hannunta, tunda ya san halin iyashegenta.
*Bayan sati biyu*
Tunda Suka dawo kullum Mk sai ya Kira Sa'a a waya, sau tari bata dauka, ranar da ta yi niyya ta dauka, to kuwa zai ta yi mata magana ne, sai ta yi kamar bata ji shi ba.
Bai yi fishi ba, a hakan dai yake 'kiranta, zuwa ne dai ba ya yi. Wani lokacin ma zai je shagon Baffah su sha hirarsu, amma ba ya neman Sa'a.
Suna cikin haka tafiya ta same shi zuwa jahar Akwa-ibom. Zasu yi wani bincike a Jami'ar jahar na tsawon wata 'daya.
Ya gama lissafinsa ba zai yiwu ta tafi da Farida ba, domin aikinta ba irin wadda za'a yi masa shan ruwan tsuntsaye bane.
A zuciyarsa yafi dokin tafiya da Sa'a tunda dai har yau bata bashi dama ba, ko waccan ma, da tsiya tsiya aka yi, shikuma so yake, ayi da yardarta da amincewarta, ta yadda zata shayar da shi kalololin soyayyarta masu gigita shi.
Saura kwanaki biyu ya yi tafiyar ya iske Sa'adah a gidan Sumayya.
Suna zaune a falon mai gidan.
Ya sassauta murya ya ce "Tafiya ce ta same ni, zuwa south, shine nake son ki yi mini rakiya, zan jima domin zan shafe akallah wata guda".
Ta girgiza kai ta re da cewa "ba inda zani".
"Umarni fa na baki".
"Gaskiya ba zanje ba, tunda dai ban tare ba, umarninka baya kaina, ka je ka tafi da wadda idan ka yi tafiya baka wuce adadin kwanakin daka fa'da mata zaka yi, saboda sonta da isar da ta yi.
Ya numfasa tare da mikewa yana cewa "na gode sosai da wannan shawarar, ya ajiye mata kudi masu auki, ga su nan ko wani uzzirin zai taso miki, sai na dawo".
Har ya kai bakin kofa, sai kuma ya juyo, ya kalleta ya ce "zuwa yaushe kika shirya tarewar?"
Kai tsaye ta ce "idan abin da nake so ya samu nan da wattanni hudu".
Ba'kin ciki ya kama shi, amma sai ya yi nufin su raba bacin ran tare ya ce "To kawai a barshi a rabin shekara mana, wattanni shida kenan"!
"To kawai mu bar shi a shekarar kawai".
Ta fa'da a kufule sosai.
Ya yi tafiyarsa ba tare da ya sake cewa uffan ba".
Sai itace tana ganin fitarsa ta fashe da kuka sosai, tana gasgata da gaske ne yafi son Farida akanta.
Mk yana tuki amma a fili yake cewa " Ubangi ka mallaka mini zuciyar Sa'adatu da tunaninta, Allah ba zan iya ba, kaine mai sarrafa zukatan bayinka, Allah ka hore mini wannan yarinyar da take neman manna mini hauka, bayan hawan jinin da nake fama da shi adalilinta!
Kai ka jarrabi zuciyata akanta, ubangiji kar ka jarrabe ni a cikin hankalina da tunanina akan sha'aninta".
Haka ya tafi Uyo shi ka'dai tamkar ba mai mata biyu ba, amma a kullum yana ro'kon ubangiji akan a mallaka masa tunaninta tamkar yadda aka mallaka masa zuciyarta, hakanan duk sallar duniya sai ya roki Ubangiji akan a sassautawa Sa'adah kishin dake neman jefasu yanayin da yake tunanin sun yi bankwana da shi.
Satinsa biyu da tafiya Wanda ya yi dai dai da watansu daya da dawowa daga Sokoto.
Sa'a ta kasa gane kanta, bata ciwon komai, amma yini take tana zubar da miyau, da ta gaji sai take fama da alawowi ko cingum, ko kuma kaninfari.
Matu'kar kuwa ba komai a bakinta to kuwa miyau zai cika mata shi.
Ga 'dan karen barci. Da kanta ta yiwa kanta alkalanci tabbas ciki ne da ita, domin tana iya hakaito haka cikin Jawad ya yi mata.
Duk da yadda ta gamsu tana da ciki sai da ta yiwa kanta gwaji da P.T strip, sakamakon kuwa ya kasance positive.
Wani irin tashin hankali ya dinga ziyaryarta, ita kuwa da wanne ido zata kalli Innah da kuma Anty Sumayya?.
Da wanne irin harshen zata musu bayanin da zasu gamsu, sau 'daya tak wani abu ya gitta a tsakanin ta da Mk, shima kuma ba da sonta da yardarta ba, fin karfi ya gwada mata.
Mk ya shammaceta kwarai da gaske, gashi yanzu ya dawo da asalin halayyarsa ta bagarar da ita da lamarinta.
Ta nisa tana tunanin hanyar da zata bi ta boyewa Innah halin da take ciki. Ta shafa cikin tana Jin wata irin zazzafar soyyaarsa na huda dukkan sassan jikinta.
Cikin Jawad ta same shi cikin kuruciya, da kuma sa Rai za'a samu tunda tana ganin da anyi aure ake samun ciki a haihu.
Cikin kanwarsa kuma bai zo mata a sadda take so ba, asalima unwanted pregnancy ne, sai dai bayan ta haifeta ta dora ido akanta aka dora mata sonta fiye da tsammani, a yanzu da hankali ya shigeta ta tabbata tana jin son cikin jikinta kwatankwacin yadda take jin son Jawad. Shine kuma cikin da ta yi 'mararin samuwarsa duk da bai zo a lokacin da ya kamata ba.
Washagari ta nufi asibiti, aka yi mata gwaji na sosai, sakamakon dai 'dayane da wadda ta yi da kanta. Ta dawo gida tana ayyana lissafin zuwanta Sokoto, lissafin cikinta wanda yana shirin shiga sati na biyar.
A yanzu ba abin da take so irin ta tare tun kafin a ankara da halin da take ciki.
Ta dinga tunanin yadda zata sanarwa Mk tana son tariya da wuri, ta tuna ranar da ya sameta gidan Sumayya kafin ya yi tafiyar, da muradinsa na son su tafi tare, Amma ta kekasa kasa ta 'ki. Ta nisa tana sake tuno sadda suke yiwa juna gatse, inda ita ta ce a bari sai nan da shekara guda.
Zuciyarta ta harba idan kuwa hakane har sai ta haihu, da kusan wata hudu.
"Tirkashi" ta furta a fili, tun yanzu kunyar Innah take ji, gashi dai a gabansu ta yi ciki, sa'ar da aka yi, ba cikin gaba da fatiha bane kamar yadda Inna ta gani a mafarkinta.
Kwanaki uku da zuwan Sa'a asibiti ta kasa daurewa saboda yadda kullum take Samun sababbin alamomin da Za'a fahimci halin da take ciki.
Da daddare tana kwance a dakinta, ta kalli agogo, ta ga lokaci ya fara ja, amma hakan ta kasa hakuri ta 'kira layin Mk.
Amma Sa'a ta kasa yin komai, saboda rashin sukunin zuciya.
Tana jin yadda ya gyra kwanciyarsa ya fara laluben kirjinta da bakinsa, kan dole ta kyale shi ya zama tamkar sabon jariri saboda yadda yake tsotsar su.
Jikinta gaba'daya ya amsa, sai tsuma take yi, shi kuma rashin 'karfin jikinsa ya masa cikas din tafiya second round ko da ta 'karfi ne kuwa irin na daren jiya. A hakan da suke barci ya yi awon gaba da su.
9:18am dai dai Sa'a ta bude idonta, har lokacin kuma Mk barcinsa yake cikin nutsuwa da kwanciyar hankali. Fuskarsa na manne da kirjinta sai ka rantse baya samun iskar zukar numfashi.
A hankali ta zare jikinta, ta mayar masa da filo gurbinta, kamar yadda take yi masa a baya.
Bata tsaya a ko'ina ba sai a bayi, kai-tsaye ruwa mai zafi ta ha'da, ta yi wanka sosai, ta fito, ta shirya cikin matsakaiciyar kwalliya, ta zauna akan stool ta kasa daura dankwali saboda yadda take jin tsananin yunwa.
Bata son tashinsa, gashi kuma ji take tamkar ta ci babu saboda tsananin yadda cikinta yake yi mata karta.
Ta dauko hijabinta ta saka, ta dauko jakarta, ta nufi kofa da nufin fita ta nemi abinci.
Ta bude kofar kenan ya tashi, da azama ya ce "Ina zaki?"
Ta dawo da sauri ta ce "yunwa nake ji, tamkar an mini yasa a ciki".
Ya bata rai sosai ya ce "shine dalilin da zaki dauki hijab ki fita babu izni, alhalin kina kallona, Wai ke wanni irin raini kika mini ne? Ke ce zaki fita siyan abinci? Karatun naki abinda ya koya miki kenan?"
Ta yi shiru, ta kasa cewa komai. Idonta ya ciko da kwalla.
Ya ja tsaki ya mike ya shige bayi.
Bai wani jima ba ya fito, amma ita sai ta ga tamkar ya kusan awa guda.
Jallabiya ya zura ya dauko wallet din sa ya fice.
Mintina Kamar biyar, ya dawo dauke da ledoji a hannunsa.
Ya tarar da ita tana kan stool din mirror tana faman goge hawaye da tissue.
Ya ajiye ledar a gabanta ya ce "gashi sauko ki ci".
Ta yi tamkar ba ta ji shi ba, shikuma ya shige bayi, ya fara wanka.
Amma da yake yunwa ba kanwar uwa ba ce, sai ta sauko, ta hau duba ledar.
Leda daya dankalin turawa da kwai ne, 'dayar kuma doyace da aka soyata cikin kwai. Sai kuma leda mai dauke da daurin kunu biyu, na gyada da na tsamiya.
Doyar ta hau ci a yunwace, kafin ya fito ta cinye tass, sai ragowan kunun tsamiya a hannunta da take shirin zuke shi.
Sai da ya shirya, sannan ya zauna yana cewa "yanzu duk doyar nan kin cinye ke ka'dai, yaushe kika zama mai cin abinci haka? "
Takaici yasa ta cigaba da matso kwalla ta na gogewa, shikuma ya hau cin abincinsa hankali kwance, yana jin wani irin shau'ki. Bai san me yasa iskancin Sa'a ke tafiya da shi ba, ya lura a yanzu bata da burin kayayyakin 'kawa, ba ta harkar kawaye, cikin dabi'unta masu Muni kaifin harshe ne ya rage mata, shima kuma dole ta rage indai tana gabansa.
Amma sakalci, sai ya ga tamkar tana girma, yana sake bin jikinta ne. Ya tabbatar har kukanta yana jerin abubawan da yake kewarsu.
Sai da ya kammala ya dubeta ya ce " ke kam kin ji kunya wallahi! Ai bai kamata ki tisa ni gaba kina mini kukan shagwaba ba, tunda dai jiya ba irin ro'kon da ban miki akan ki taimake ni ki mini abin da zan samu nutsuwa, amma ki kika shafawa idonki toka. Sai dai kuma na nuna miki ba zanci gaba da zuba miki ido kina mini iyashege ba. Da ace kin ji rarrashin da na miki, da kin ga yadda zan tarairaye ki, na lallashe ki, amma yanzu ko bubburwa zaki yi ba ruwana da ke, bare na san kina sakalcin banza".
Da rawar murya irin tana gaf da fashewa da kuka ta ce "kin yarda da na yi da kai ya isa ka gane sonka ne ba na yi, haka karfin da ka gwada mini, da har yanzu nake Jin ciwo a inda ka bubbbga mini guiwar hannunka ya almata mini kaima sha'awa ta kawai kake yi, amma ba so ba".
"Eh bana son ki".
Ya bata amsa a ta'kaice.
Ba'kin ciki ya turniketa ta ce "Allah ya kawo zazzabi anjima zaka gane lalle nima bana sonka".
Ya ma'ke kafada ya ce "Ameen! Ciwo na kan kowa, nawa ya yi kyau ai. Kema kuma na ki na tafe, domin ciwo ai ba a fatansa, idan yau kaine, gobe na ga waninka. Idan ubangiji ya juya abin ya dawo kanki, a lokacin zaki gane tsiyar ki ka'dan ce".
Ya mike ya na cewa "To ni kam dama kwanaki uku iyalina ta san zan yi. Yau kam ko hayar direban da zai tuka ni zuwa Kano, zan yi, bare kuma Ina fatan ubangiji ya bani ikon tukin da kaina.
Don bana cikin mutane masu yiwa masoyansu 'karya ko butulci, ko danne musu hakkin su".
Zuciyarta ta buga da tsananin gaske, ta san shagube ya yi mata, sannan kai tsaye yake nuna mata yau gurin Farida zai kwana, domin kwana ukun da ta bashi ya cika.
Haka suka dawo Kano, ba wani jituwa a tsakanin su.
Ya sauketa a kofar gidansu ya ja motarsa ya yi gaba.
Tunda ya ajiyeta yake jin tamkar ya rusa ihu, shi dai ko zasu kwana suna Yar tsama yafi son ya ganta a kusa da shi, ko da ba zata kula shi ba, haka nan shima ko ba zai mata maganar ba, amma dai ya ganta kusa da shi shine samun nutsuwarsa, ko shareta da yake yi, Karfin hali kawai yake yi da son kwatar kansa a hannunta, tunda ya san halin iyashegenta.
*Bayan sati biyu*
Tunda Suka dawo kullum Mk sai ya Kira Sa'a a waya, sau tari bata dauka, ranar da ta yi niyya ta dauka, to kuwa zai ta yi mata magana ne, sai ta yi kamar bata ji shi ba.
Bai yi fishi ba, a hakan dai yake 'kiranta, zuwa ne dai ba ya yi. Wani lokacin ma zai je shagon Baffah su sha hirarsu, amma ba ya neman Sa'a.
Suna cikin haka tafiya ta same shi zuwa jahar Akwa-ibom. Zasu yi wani bincike a Jami'ar jahar na tsawon wata 'daya.
Ya gama lissafinsa ba zai yiwu ta tafi da Farida ba, domin aikinta ba irin wadda za'a yi masa shan ruwan tsuntsaye bane.
A zuciyarsa yafi dokin tafiya da Sa'a tunda dai har yau bata bashi dama ba, ko waccan ma, da tsiya tsiya aka yi, shikuma so yake, ayi da yardarta da amincewarta, ta yadda zata shayar da shi kalololin soyayyarta masu gigita shi.
Saura kwanaki biyu ya yi tafiyar ya iske Sa'adah a gidan Sumayya.
Suna zaune a falon mai gidan.
Ya sassauta murya ya ce "Tafiya ce ta same ni, zuwa south, shine nake son ki yi mini rakiya, zan jima domin zan shafe akallah wata guda".
Ta girgiza kai ta re da cewa "ba inda zani".
"Umarni fa na baki".
"Gaskiya ba zanje ba, tunda dai ban tare ba, umarninka baya kaina, ka je ka tafi da wadda idan ka yi tafiya baka wuce adadin kwanakin daka fa'da mata zaka yi, saboda sonta da isar da ta yi.
Ya numfasa tare da mikewa yana cewa "na gode sosai da wannan shawarar, ya ajiye mata kudi masu auki, ga su nan ko wani uzzirin zai taso miki, sai na dawo".
Har ya kai bakin kofa, sai kuma ya juyo, ya kalleta ya ce "zuwa yaushe kika shirya tarewar?"
Kai tsaye ta ce "idan abin da nake so ya samu nan da wattanni hudu".
Ba'kin ciki ya kama shi, amma sai ya yi nufin su raba bacin ran tare ya ce "To kawai a barshi a rabin shekara mana, wattanni shida kenan"!
"To kawai mu bar shi a shekarar kawai".
Ta fa'da a kufule sosai.
Ya yi tafiyarsa ba tare da ya sake cewa uffan ba".
Sai itace tana ganin fitarsa ta fashe da kuka sosai, tana gasgata da gaske ne yafi son Farida akanta.
Mk yana tuki amma a fili yake cewa " Ubangi ka mallaka mini zuciyar Sa'adatu da tunaninta, Allah ba zan iya ba, kaine mai sarrafa zukatan bayinka, Allah ka hore mini wannan yarinyar da take neman manna mini hauka, bayan hawan jinin da nake fama da shi adalilinta!
Kai ka jarrabi zuciyata akanta, ubangiji kar ka jarrabe ni a cikin hankalina da tunanina akan sha'aninta".
Haka ya tafi Uyo shi ka'dai tamkar ba mai mata biyu ba, amma a kullum yana ro'kon ubangiji akan a mallaka masa tunaninta tamkar yadda aka mallaka masa zuciyarta, hakanan duk sallar duniya sai ya roki Ubangiji akan a sassautawa Sa'adah kishin dake neman jefasu yanayin da yake tunanin sun yi bankwana da shi.
Satinsa biyu da tafiya Wanda ya yi dai dai da watansu daya da dawowa daga Sokoto.
Sa'a ta kasa gane kanta, bata ciwon komai, amma yini take tana zubar da miyau, da ta gaji sai take fama da alawowi ko cingum, ko kuma kaninfari.
Matu'kar kuwa ba komai a bakinta to kuwa miyau zai cika mata shi.
Ga 'dan karen barci. Da kanta ta yiwa kanta alkalanci tabbas ciki ne da ita, domin tana iya hakaito haka cikin Jawad ya yi mata.
Duk da yadda ta gamsu tana da ciki sai da ta yiwa kanta gwaji da P.T strip, sakamakon kuwa ya kasance positive.
Wani irin tashin hankali ya dinga ziyaryarta, ita kuwa da wanne ido zata kalli Innah da kuma Anty Sumayya?.
Da wanne irin harshen zata musu bayanin da zasu gamsu, sau 'daya tak wani abu ya gitta a tsakanin ta da Mk, shima kuma ba da sonta da yardarta ba, fin karfi ya gwada mata.
Mk ya shammaceta kwarai da gaske, gashi yanzu ya dawo da asalin halayyarsa ta bagarar da ita da lamarinta.
Ta nisa tana tunanin hanyar da zata bi ta boyewa Innah halin da take ciki. Ta shafa cikin tana Jin wata irin zazzafar soyyaarsa na huda dukkan sassan jikinta.
Cikin Jawad ta same shi cikin kuruciya, da kuma sa Rai za'a samu tunda tana ganin da anyi aure ake samun ciki a haihu.
Cikin kanwarsa kuma bai zo mata a sadda take so ba, asalima unwanted pregnancy ne, sai dai bayan ta haifeta ta dora ido akanta aka dora mata sonta fiye da tsammani, a yanzu da hankali ya shigeta ta tabbata tana jin son cikin jikinta kwatankwacin yadda take jin son Jawad. Shine kuma cikin da ta yi 'mararin samuwarsa duk da bai zo a lokacin da ya kamata ba.
Washagari ta nufi asibiti, aka yi mata gwaji na sosai, sakamakon dai 'dayane da wadda ta yi da kanta. Ta dawo gida tana ayyana lissafin zuwanta Sokoto, lissafin cikinta wanda yana shirin shiga sati na biyar.
A yanzu ba abin da take so irin ta tare tun kafin a ankara da halin da take ciki.
Ta dinga tunanin yadda zata sanarwa Mk tana son tariya da wuri, ta tuna ranar da ya sameta gidan Sumayya kafin ya yi tafiyar, da muradinsa na son su tafi tare, Amma ta kekasa kasa ta 'ki. Ta nisa tana sake tuno sadda suke yiwa juna gatse, inda ita ta ce a bari sai nan da shekara guda.
Zuciyarta ta harba idan kuwa hakane har sai ta haihu, da kusan wata hudu.
"Tirkashi" ta furta a fili, tun yanzu kunyar Innah take ji, gashi dai a gabansu ta yi ciki, sa'ar da aka yi, ba cikin gaba da fatiha bane kamar yadda Inna ta gani a mafarkinta.
Kwanaki uku da zuwan Sa'a asibiti ta kasa daurewa saboda yadda kullum take Samun sababbin alamomin da Za'a fahimci halin da take ciki.
Da daddare tana kwance a dakinta, ta kalli agogo, ta ga lokaci ya fara ja, amma hakan ta kasa hakuri ta 'kira layin Mk.