Sashe 44
Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
***
Su zahra basu fi minti ashirin da tafiya ba Part din Ammi ya fara karbar Baki matar Aliyu Halimatu ita ta fara zuwa Ammi batayi mamaki ba tasan karshen maganar kenan duk wanda ya samu labarin mahmud ya dawo zaiyi kokarin zuwa ya gani da idonsa ballantana tasan maganar zahra zata karade dangi shi yasa tayi wannan Kandagarkin ta turata gida duk masifar mutum da iya gulmarsa Saida ya koma da gwiwa a sage Dan Mai Kama da itama baze gani ba, kafin azzuhur part din ya dinke da jama'a 'yan taya murna, na gida Wanda suka Isa sai yan leke-leke sukeyi basa sama basa kasa, irinsu Habiba matar uncle saminu har gidan Hajiya Inna sukaje ita da Matar Ya Abdallah first born din Abbie, tasu tazo Daya da Habiba itama 'yar adawar mahmud ce ta gaske sai dai ita ta iya takunta ba lallai ne lokaci Daya ka ganeta ba,haka suka dawo ba wani labari sai Kuma suka shiga kokonton gaskiyar maganar yarinyar da aka fada yazo da ita.
Aishat na kwance Kiran Aunty Surayya ya shigo.
"Wai kina Ina ne tun Dan hantsi nake gidan Nan sai yaran nake gani Amma ke ko duriyarki Babu".
Yunkurawa tayi ta tashi zaune tana fadin.
"Ina masaukina a kasa bana Jin Dadi ne shi yasa, Aunty Ina wuni".
Dariya Ammi tayi saboda wayar a speaker take, tana ayyana kina min dacin Rai dai na tura muku Mata gida,Baku San nemar muku daraja nake yi ba duk wannan taruruwar murnar da ake zuwa ba domin Allah ake yinta ba saboda aga yarinyar da aka Kai musu labarin ta.
" Lafiya kalau, kizo sama yanzu Ina bedroom din Ammi".
Ta kashe wayar, saukowa Aishar tayi ta zura takalma ta fice tana hawan strains taji Kira ya shigo Mata tana dubawa Sameer ne.
Ta daga da sallama suka gaisa sannna ya Dora da fadin.
"Dake da waye zakuzo gidan oga na arkilla zaku duba wani Abu kuga Koda abinda za'a gyara".
"Ok Bari na fadawa Aunty Surayya sai muzo tare".
Ta fada tana tura handle din kofar bedroom din Ammin.
A zaune ta samesu su Aunty Surayya nata faman rubutu a Cikin wata jotter.
Da sallama a bakinta ta shiga ta gaishe dasu Ammin ta nemi guri ta zauna, Saida Aunty Surayya ta Gama rubutun ta dago tana kallon Aishat din.
"Ungo duba kin gani Koda gyaran da za'ayi".
Jotter ta karba ai Bata San lokacin da tayi super ta Haye jikin Ammin su ba.
"Allah ya Kara sutura Ammi, ya jikan mahaifi yanda Kika faranta Mana Allah ya haskaka qabarin Alhaji Haroona ya yalwata Masa, mun gode Amminmu sai yanzu na samu kwanciyar hankali wallahi".
Murmushi Ammin tayi.
"Allahumma Amin, da kin dauki fushi Dani Dan Ina nemar muku daraja da kima kinsa yau har sama Hajiya Babba ta hauro saboda taga kwakwaf tunda nasan yayan ki Ibrahim ya fada Mata komai har dakun Nan ta shiga Wai sau Daya ta taba shigarsu Ina jinta dasu Batool Suma da Taya bera Bari har kciki suke shiga Kuma jikin ba kwari ta sauka da kyar fa take taka kafar Amma gulma ta hauro da ita saman Ina jiyo wash wash dinta tana sauka".
"Allah ya kyauta ai ba Karamin Basu kafa mikayi ba Ammi sai yanzu na gane plan dinki na gaggawar ficewa da zahrar daga gidan Kinga kin kashe bakin tsanya babu batun mutum ya bugi kirji yace ya ganta da idanunsa, yanzu Sameer ya kirawo ni yace muje gidan bros na Arkilla muga wani Abu ko da abunda za'a gyara".
"To Kuma da boutique dina zakuje a hado lefen da za'a Kai musu can nasan ba wani abun azo a gani akayi Mata ba duba da yanda abun ya faru kinsan halin kayanki Kuma".
"To Bari mu Fara zuwa Arkillar in yaso sai mu wuce can din ko Aunty Surayya?".
A gidan suka Sami mahmud da wasu abokansa biyu sai sameer.
Suka gaishe da Aunty Surayya har tana zolayar mahmud.
Sameer ne ya shiga ya bude musu inda kayan da suka zo dasu daga Dubai da Kuma akwatunan.
"Auntyn mu gasu Nan ku duba idan da abinda babu ko za'a canza ko karawa sai a fada"..
Ya ja musu kofar, kayan suka Fara dubawa ba karya komai yayi harda abinda ma ba'a sakawa an saka sunyi santin kayan kamar me Dan naira da taci gidansu a gurin ba Bata lokaci suka shiga zubawa a Cikin akwatunan abinda ya daukesu kusan awa hudu suna Abu Daya.
Saida suka Gama komai sannan Aunty Surayya ta Kira Ammi video call lokacin Ammin tana gurin Hajiya Inna Dan ana shiga magariba ta fice ita da suhailat wadda ke driving dinsu suka nufi mabera gidan Hajiya Inna taje ta fada Mata komai ake ciki ta Kuma Bata hakurin yanke hukuncin da tayi ba tare da ta nemi Shawarar ta ba,nuna Mata Hajiyar tayi ba komai idan akace sai an tsaya ciccira maganar abin baze Zama sirrin ba hakan da tayi shine dai dai.
To Kuma saiga Kiran WhatsApp tunda duk gidajensu da wifi suke amfani.
Akwatunan Ammi ta Fara gani gasu Nan birjik sai da suka Kai karshe sannan Aunty Surayyar ta dago da wayar tana fadin .
"Ammi kin gani? To Dana ya Gama aikinsa Kaiwa kadai ya rage ba'a bukatar komai Ina za'a kawo Kayan? Can ko kuma a barsu a nan kawai?".
"Masha Allah, Kice kun hutar dani? Ki fada musu su kawosu gidan Hajiya kawai sai a fadawa Wanda ya kamata suzo su gani a Nan kawai".
Sukayi sallama Hajiyar ke tambayar.
"Me za'a kawo Mini Nan kuma?".
A kunyace Ammi ta fada mata".
"A'a kirawo su azo a kaini Arkillar na gani yaushe za'a wani kawo min Kaya da wani kiran jama'a su ringa dodon gani Abu guri yana neman kurewa ga Azumi Yana karatowa gara ayi a Mika Masa matarsa ai yayi rawar gani ma wallahi a 'ya 'yan zamani ba kowa ne zeyi abinda dan Albarkar Nan yayi ba, shi yasa yaki zuwa gidan kenan yayi min zaune a Nan yake min wasu maganganun a bai-bai".
Ita dai Ammi Dan murmushi kawai takeyi.
Daga Arkilla gidan Ammi su Sameer da Tajuddeen suka nufa da lefen har lokacin Su Habiba suna nan Wai suna neman Ammi suyi Mata sallama da momin kano Maman su Faruq wadda ta dawo da gefin magariba daga Dubai inda takeyo oder din Kaya, tana zuwa yaran ta suka fada Mata dawowar Ya mahmud din shine bayan tayi sallah ta shigo sai Kuma Bata Sami Ammin ba sun dauka ko tana part din Abbie ne.
Suna zaune aka Fara shigowa da akwatuna ana ajewa Saida aka shigo dasu gaba daya Nan kallo ya koma sama suna mamakin daga Ina kuma wannan su Aunty surayya ne suk shigo daga karshe Nan suke fada musu lefen mahmud ne, Akayi caaaa kowa na fadar Albarkacin bakinssa aka Fara daddagawa, ana wannan rarumar Ammi ta wuce ciki.
****
Saida su Aunty Badi'a sukayi salllolinsu Alawiyya da zilai wadda tayi suf ta baro sahura ta shigo, dazu Sarai ta gane zahra ta gwasale sahurar ne Dan kada tayi halin nata na kinibibi tunda Bata San menene dalilin zuwan ba ga Kuma Bakin fuska suna tare tana gani zata shiga gurin Mama ta Kai tsegumu Dan ma kwanan nan ta rasa me yake damun Mamar duk ta fada sai idanu gashi ta rage wannan izzar da wulakancin nan na ganin kowa a banza.
Sai da suka Gama suka kimtsa wannan Ammah ta shiga suka gaisa sosai tayi musu sannu da zuwa.
Aunty Badi'a ce ta Fara Kora bayanin dangantakarsu da Ammi sannan ta Dora da fadin dalilin zuwansu duk da Ammi ta yiwa Ammah a takaice.
"Hajiya ga yarinyar mu Nan mun kawo ta badon mun Raina iyawarku ba a'a bisa wasu dalilai na abinda ya faru da yaron muke son azo a daukar Masa matarsa a Cikin mutuncinta da kimarta kamar ko wace yarinya budurwa da ake aurarwa a gaban iyayenta,kinsan ko wane family akwai tasu matsalar da fatan bamu Bata muku ba".
"Kai haba wannan ai gyara kayanka ne kuma kun nuna Mana yanda kuke kaunar zahra da gaskiya mun gode sosai, ku huta kafin Abban nasu ya shigo ku gaisa".
Har Ammah taje baking kofa ta dawo tana fadin.
"Na shafa'a ga waya Hajiya zainab zata Kira tace min layinku baya shiga a nan kasar".
"Wallahi kuwa haka ake fama idan Suma suka shiga sai dai su sayi sabon sim na can wallahi".
Tunda zahra ta shige Bata ko leko waje ba, kwanciya tayi duk abun duniya ya taru yayi Mata yawa, ga Ammah ma bata ko leko ta ba tana ta bakinta shima meu amor shiru Bai nemeta ba haka Aunty Aishar itama shiru Sai taji Zuciyarta ta tsinke tasan shikenan sai yanda Hali yayi tunda har zuwa lokacin Bai kirata ba tasan Amminsa Bata sonta gashi harda mutane ta hadota a bawa iyayenta hakuri.
Aunty zilai ce ta shigo taga zahra ta rabsa uban tagumi ko daga inda take Bata tashi ba, ga abincin da aka kawo mata ko taba shi batayi ba.
Matsowa tayi tana fadin.
"Haba uwar dakina tagumi ai ba naki bane, wane gata ne Ubangiji baiyi Miki ba ai ke sai hamdala ta kamace ki".
Dago aexy eyes dinta tayi ta watsasu akan Aunty zilan tana fadin.
"Kayya Aunty zilai idan ana cin baure ba'a tona cikinsa Kuma daudar gora ciki ka shata, gida fa Ammimsa tace a rakoni a bawa Ammah hakuri Kinga abinda ma ta bani da zamu taho tace min sai wata rana".
Sai kukan da take rikewa ya kubce Mata.
Hakuri Aunty zilan ta Riga bata, tana Cikin kukan ne wayarta ta dauki Kira harta tsinke Bata daga ba da gaske abin yayi Mata ciwo da tasan karshen abun haka ze Zama da Bata yarda tayi irin wannan sabon dashi ba.
Wani Kiran ne ya shigo Aunty zilai ce ta dauka da sallama muryar yallaban taji duk sai ta daburce ta rasa abun fada, Cikin in Ina ta furta."yal..labai Ina wuni".
"Lafiya". Ya amsa mata in short.
"Ina zahrar take ne?".
Da sauri tace "gata Nan yallabai bansan meye ya sameta ba sai kuka takeyi"
"What! Kuka kuma?".
Su zahra basu fi minti ashirin da tafiya ba Part din Ammi ya fara karbar Baki matar Aliyu Halimatu ita ta fara zuwa Ammi batayi mamaki ba tasan karshen maganar kenan duk wanda ya samu labarin mahmud ya dawo zaiyi kokarin zuwa ya gani da idonsa ballantana tasan maganar zahra zata karade dangi shi yasa tayi wannan Kandagarkin ta turata gida duk masifar mutum da iya gulmarsa Saida ya koma da gwiwa a sage Dan Mai Kama da itama baze gani ba, kafin azzuhur part din ya dinke da jama'a 'yan taya murna, na gida Wanda suka Isa sai yan leke-leke sukeyi basa sama basa kasa, irinsu Habiba matar uncle saminu har gidan Hajiya Inna sukaje ita da Matar Ya Abdallah first born din Abbie, tasu tazo Daya da Habiba itama 'yar adawar mahmud ce ta gaske sai dai ita ta iya takunta ba lallai ne lokaci Daya ka ganeta ba,haka suka dawo ba wani labari sai Kuma suka shiga kokonton gaskiyar maganar yarinyar da aka fada yazo da ita.
Aishat na kwance Kiran Aunty Surayya ya shigo.
"Wai kina Ina ne tun Dan hantsi nake gidan Nan sai yaran nake gani Amma ke ko duriyarki Babu".
Yunkurawa tayi ta tashi zaune tana fadin.
"Ina masaukina a kasa bana Jin Dadi ne shi yasa, Aunty Ina wuni".
Dariya Ammi tayi saboda wayar a speaker take, tana ayyana kina min dacin Rai dai na tura muku Mata gida,Baku San nemar muku daraja nake yi ba duk wannan taruruwar murnar da ake zuwa ba domin Allah ake yinta ba saboda aga yarinyar da aka Kai musu labarin ta.
" Lafiya kalau, kizo sama yanzu Ina bedroom din Ammi".
Ta kashe wayar, saukowa Aishar tayi ta zura takalma ta fice tana hawan strains taji Kira ya shigo Mata tana dubawa Sameer ne.
Ta daga da sallama suka gaisa sannna ya Dora da fadin.
"Dake da waye zakuzo gidan oga na arkilla zaku duba wani Abu kuga Koda abinda za'a gyara".
"Ok Bari na fadawa Aunty Surayya sai muzo tare".
Ta fada tana tura handle din kofar bedroom din Ammin.
A zaune ta samesu su Aunty Surayya nata faman rubutu a Cikin wata jotter.
Da sallama a bakinta ta shiga ta gaishe dasu Ammin ta nemi guri ta zauna, Saida Aunty Surayya ta Gama rubutun ta dago tana kallon Aishat din.
"Ungo duba kin gani Koda gyaran da za'ayi".
Jotter ta karba ai Bata San lokacin da tayi super ta Haye jikin Ammin su ba.
"Allah ya Kara sutura Ammi, ya jikan mahaifi yanda Kika faranta Mana Allah ya haskaka qabarin Alhaji Haroona ya yalwata Masa, mun gode Amminmu sai yanzu na samu kwanciyar hankali wallahi".
Murmushi Ammin tayi.
"Allahumma Amin, da kin dauki fushi Dani Dan Ina nemar muku daraja da kima kinsa yau har sama Hajiya Babba ta hauro saboda taga kwakwaf tunda nasan yayan ki Ibrahim ya fada Mata komai har dakun Nan ta shiga Wai sau Daya ta taba shigarsu Ina jinta dasu Batool Suma da Taya bera Bari har kciki suke shiga Kuma jikin ba kwari ta sauka da kyar fa take taka kafar Amma gulma ta hauro da ita saman Ina jiyo wash wash dinta tana sauka".
"Allah ya kyauta ai ba Karamin Basu kafa mikayi ba Ammi sai yanzu na gane plan dinki na gaggawar ficewa da zahrar daga gidan Kinga kin kashe bakin tsanya babu batun mutum ya bugi kirji yace ya ganta da idanunsa, yanzu Sameer ya kirawo ni yace muje gidan bros na Arkilla muga wani Abu ko da abunda za'a gyara".
"To Kuma da boutique dina zakuje a hado lefen da za'a Kai musu can nasan ba wani abun azo a gani akayi Mata ba duba da yanda abun ya faru kinsan halin kayanki Kuma".
"To Bari mu Fara zuwa Arkillar in yaso sai mu wuce can din ko Aunty Surayya?".
A gidan suka Sami mahmud da wasu abokansa biyu sai sameer.
Suka gaishe da Aunty Surayya har tana zolayar mahmud.
Sameer ne ya shiga ya bude musu inda kayan da suka zo dasu daga Dubai da Kuma akwatunan.
"Auntyn mu gasu Nan ku duba idan da abinda babu ko za'a canza ko karawa sai a fada"..
Ya ja musu kofar, kayan suka Fara dubawa ba karya komai yayi harda abinda ma ba'a sakawa an saka sunyi santin kayan kamar me Dan naira da taci gidansu a gurin ba Bata lokaci suka shiga zubawa a Cikin akwatunan abinda ya daukesu kusan awa hudu suna Abu Daya.
Saida suka Gama komai sannan Aunty Surayya ta Kira Ammi video call lokacin Ammin tana gurin Hajiya Inna Dan ana shiga magariba ta fice ita da suhailat wadda ke driving dinsu suka nufi mabera gidan Hajiya Inna taje ta fada Mata komai ake ciki ta Kuma Bata hakurin yanke hukuncin da tayi ba tare da ta nemi Shawarar ta ba,nuna Mata Hajiyar tayi ba komai idan akace sai an tsaya ciccira maganar abin baze Zama sirrin ba hakan da tayi shine dai dai.
To Kuma saiga Kiran WhatsApp tunda duk gidajensu da wifi suke amfani.
Akwatunan Ammi ta Fara gani gasu Nan birjik sai da suka Kai karshe sannan Aunty Surayyar ta dago da wayar tana fadin .
"Ammi kin gani? To Dana ya Gama aikinsa Kaiwa kadai ya rage ba'a bukatar komai Ina za'a kawo Kayan? Can ko kuma a barsu a nan kawai?".
"Masha Allah, Kice kun hutar dani? Ki fada musu su kawosu gidan Hajiya kawai sai a fadawa Wanda ya kamata suzo su gani a Nan kawai".
Sukayi sallama Hajiyar ke tambayar.
"Me za'a kawo Mini Nan kuma?".
A kunyace Ammi ta fada mata".
"A'a kirawo su azo a kaini Arkillar na gani yaushe za'a wani kawo min Kaya da wani kiran jama'a su ringa dodon gani Abu guri yana neman kurewa ga Azumi Yana karatowa gara ayi a Mika Masa matarsa ai yayi rawar gani ma wallahi a 'ya 'yan zamani ba kowa ne zeyi abinda dan Albarkar Nan yayi ba, shi yasa yaki zuwa gidan kenan yayi min zaune a Nan yake min wasu maganganun a bai-bai".
Ita dai Ammi Dan murmushi kawai takeyi.
Daga Arkilla gidan Ammi su Sameer da Tajuddeen suka nufa da lefen har lokacin Su Habiba suna nan Wai suna neman Ammi suyi Mata sallama da momin kano Maman su Faruq wadda ta dawo da gefin magariba daga Dubai inda takeyo oder din Kaya, tana zuwa yaran ta suka fada Mata dawowar Ya mahmud din shine bayan tayi sallah ta shigo sai Kuma Bata Sami Ammin ba sun dauka ko tana part din Abbie ne.
Suna zaune aka Fara shigowa da akwatuna ana ajewa Saida aka shigo dasu gaba daya Nan kallo ya koma sama suna mamakin daga Ina kuma wannan su Aunty surayya ne suk shigo daga karshe Nan suke fada musu lefen mahmud ne, Akayi caaaa kowa na fadar Albarkacin bakinssa aka Fara daddagawa, ana wannan rarumar Ammi ta wuce ciki.
****
Saida su Aunty Badi'a sukayi salllolinsu Alawiyya da zilai wadda tayi suf ta baro sahura ta shigo, dazu Sarai ta gane zahra ta gwasale sahurar ne Dan kada tayi halin nata na kinibibi tunda Bata San menene dalilin zuwan ba ga Kuma Bakin fuska suna tare tana gani zata shiga gurin Mama ta Kai tsegumu Dan ma kwanan nan ta rasa me yake damun Mamar duk ta fada sai idanu gashi ta rage wannan izzar da wulakancin nan na ganin kowa a banza.
Sai da suka Gama suka kimtsa wannan Ammah ta shiga suka gaisa sosai tayi musu sannu da zuwa.
Aunty Badi'a ce ta Fara Kora bayanin dangantakarsu da Ammi sannan ta Dora da fadin dalilin zuwansu duk da Ammi ta yiwa Ammah a takaice.
"Hajiya ga yarinyar mu Nan mun kawo ta badon mun Raina iyawarku ba a'a bisa wasu dalilai na abinda ya faru da yaron muke son azo a daukar Masa matarsa a Cikin mutuncinta da kimarta kamar ko wace yarinya budurwa da ake aurarwa a gaban iyayenta,kinsan ko wane family akwai tasu matsalar da fatan bamu Bata muku ba".
"Kai haba wannan ai gyara kayanka ne kuma kun nuna Mana yanda kuke kaunar zahra da gaskiya mun gode sosai, ku huta kafin Abban nasu ya shigo ku gaisa".
Har Ammah taje baking kofa ta dawo tana fadin.
"Na shafa'a ga waya Hajiya zainab zata Kira tace min layinku baya shiga a nan kasar".
"Wallahi kuwa haka ake fama idan Suma suka shiga sai dai su sayi sabon sim na can wallahi".
Tunda zahra ta shige Bata ko leko waje ba, kwanciya tayi duk abun duniya ya taru yayi Mata yawa, ga Ammah ma bata ko leko ta ba tana ta bakinta shima meu amor shiru Bai nemeta ba haka Aunty Aishar itama shiru Sai taji Zuciyarta ta tsinke tasan shikenan sai yanda Hali yayi tunda har zuwa lokacin Bai kirata ba tasan Amminsa Bata sonta gashi harda mutane ta hadota a bawa iyayenta hakuri.
Aunty zilai ce ta shigo taga zahra ta rabsa uban tagumi ko daga inda take Bata tashi ba, ga abincin da aka kawo mata ko taba shi batayi ba.
Matsowa tayi tana fadin.
"Haba uwar dakina tagumi ai ba naki bane, wane gata ne Ubangiji baiyi Miki ba ai ke sai hamdala ta kamace ki".
Dago aexy eyes dinta tayi ta watsasu akan Aunty zilan tana fadin.
"Kayya Aunty zilai idan ana cin baure ba'a tona cikinsa Kuma daudar gora ciki ka shata, gida fa Ammimsa tace a rakoni a bawa Ammah hakuri Kinga abinda ma ta bani da zamu taho tace min sai wata rana".
Sai kukan da take rikewa ya kubce Mata.
Hakuri Aunty zilan ta Riga bata, tana Cikin kukan ne wayarta ta dauki Kira harta tsinke Bata daga ba da gaske abin yayi Mata ciwo da tasan karshen abun haka ze Zama da Bata yarda tayi irin wannan sabon dashi ba.
Wani Kiran ne ya shigo Aunty zilai ce ta dauka da sallama muryar yallaban taji duk sai ta daburce ta rasa abun fada, Cikin in Ina ta furta."yal..labai Ina wuni".
"Lafiya". Ya amsa mata in short.
"Ina zahrar take ne?".
Da sauri tace "gata Nan yallabai bansan meye ya sameta ba sai kuka takeyi"
"What! Kuka kuma?".