Sashe 10
Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Da sauri ta nufi Hajiyar tana fadin. Oyoyo -oyoyo ga Hajiyata ga Hajiyata".
"Ke tafi can Ashe duk abinda na fada Miki ta bayan kunnenki ya wuce Saida Kika fice Kika barmu da tashin hankali, jiya kukan da nayi rabona da yin irinsa tun rasuwar mijina. Amma Kika sakani maimaitwa Dan Allah ke kuwa 'yar Nan Ina Kika tafi jiya".
"Haba Hajiya Dan Allah haka mukayi da ke a gida kafin mu taho wato kin karya Alkawarin kenan? To a kazarki ta juma'a wallahi"
Ita dai Zahra borin kunya ta Fara "Allah ya Baki hakuri nifa na fada Miki kawai dai yawan mutane ya Hana ki gane waye yake Miki magana, Amma yaushe zanyi Miki haka Allah naji maganar ki kinga yanzu ma Zan Sha maganin fa".
Mahmud ne ya taso Yana fadin "Hajiyar mu ki shigo ciki ki fada min abinda ba'a so na sani Zan Baki abinda yafi kazar ma".
"Yauwa nasan kafi da haka, kanaji jiya ne wata daukakkiya ta tadawa yarinyar Nan hankali Wai kome gareta a mahaifa bansan dai sunansa ba da yaren Nasara Amma dai da hausa muna ce Masa tsiron mahaifa Wai sai tayi Mata tiyata,haka kawai ta ragewa zukekiyar 'yar Nan kwaliti yo an yanka mutum tun baiyi haihuwar fari ba Ina labari, shine nace baza'a yanka ta ba ga magani Nan Tasha na wata Daya in Sha Allah ze narke, ai sai daga baya Rakiya ke fada min ita waccan din ta Dade tana sonka tun Kuna turai koba haka bane? Ja'ira taga yarinya danya Sharab zata zauce tayi Mata illah to Banda abunka yaushe zaka ce buduwarka ta duba matarka ai wauta ce babba, wallahi kada a Kara kwatantawa, shine fa yarinyar nan tayi Mana batan dabo tun azzahar muka nemi 'yar Nan muka rasa nayi kuka kamar Zan yada idona to me zamu fada maka daga kawo yarinya ace ta Bata a gidana wallahi in takaice maka labari sai goma Sha biyun dare aka ganota ta Janbulo gidansu kawarta, itama uwar da yake ta kirki ce sai tayi tunani ta Nemo uwarta a waya take tambayarta duk da tana gurinta ta haka akasan guduwa tayi daga gurina cikin dare suka daukota to kaji yanda magana dai take".
Wani kallo ya yiwa Zahra Mai ma'anoni da yawa, sannan ya juya Yana kallon Sameer Wanda tunda Hajiyar makwarari ta Fara zuba ya sadda kansa kasa yayi Dana sanin kawota tafi cikin cikin masaki.
"To shike Nan in Sha Allah za'a kiyaye yanzu kiyi hakuri bata kyauta ba za'a duba korafin, nima ita ta tasoni na dawo ba Shiri wallahi hajiya yarinyar nan rikicinta yayi yawa".
"To ai tayi mini dai-dai ashe jikar tawa tasan kanta zo Nan Yar albarka".
Gurinta tazo ta zauna a kasa kusa da kafarata tana fadin "Hajiya Ina kwana?".
"Lafiya kalau ya jikin naki?"
"Nifa yanzu lafiya ta kalau ba damuwar komai".
Shima Muhmud Zama yayi kusa da ita da gani da shakuwa Mai yawa a tsakaninsu.
"Hajiyarmu kwana biyu Shiru ko nemana bakyayi ko?".
"Kaji kinibibi ta Ina Zan nemeka bayan kayi gudun hijira".
Dariya ya kamayi har ya bawa Zahra mamaki Daman Yana dariya haka.
Tashi tayi duk da Batasan Kan gurin ba Amma tana tunanin kitchen ne a cikin corridor din dake jikin dining area.
Babban tray ta dauko ta sako ruwa da lemo da Madara da plates ta dauko warmer din da aka zuba pepper soup din turkey din ta nufo parlourn ta dire cener table dake gaban Hajiyar tana fadin gashi Hajiyata ki Sha ruwa kafin nayi Miki girki yau fa a Nan Zaki wuni tunda oga ya dauke min Aunty Rukayya ko sallama bamuyi ba".
Inda Sameer din yake Hajiyar ta kalla "baka kyauta ba ai sai suyi sallama Mana kaga bataji Dadi ba".
"Ai zata dawo tunda zamuje Azare Nan da jibi".
Zahra na son taji ba'asin za'a tafi a barta Amma ba hali Dan tunda suka shigo ta kasa had'a Ido da Sameer da gaske ba karamar kunyarsa takeji ba.
Fita sukayi dare suka bar hajiya da zahrar.
Hira Hajiya ke Mata sosai tamkar sun shekara da sanin juna, taci Naman sosai Tasha madarar tana fadin "irinta muke Sha a makka laban kuke cewa ko tunda Sameer yace min mamarki balarabiyar Jordan ce ko?"
"Eh 'yar can ce".
"Ikon Allah ke Kuma Allah ya kaddaro naki mahaifin a wannan nashiya tamu, ai Sameer ya bani labarinki batun yanzu ba tun lokacin da mijinki ya kaini jidda akayi min aikin Ido da yaga wata yarinya diyar larabawa yake bani labarin ya ganki a jirgi keda wani mutum ko mahaifin ne ko Kuma dai mariki ne basu ba, Saida za'a daura Aurenki yazo yake dauko min tsohon zancen harna gane nace nasa a Ina suka laluboki yace min ikon Allah ne ya hada ku, daga Nan ban Kara ce masa komai ba, Fadima ki rik'e mijinki da kyau Yana sonki yanda Baki zato tun Baki San meye so ba yake Miki shi, kingan shi nan tun suna makarantar sakandire suke tare da Sameer Bai yadda shi ba, da Allah ya daukaka shi saiya Kara janyo shi jikin shi duk inda ya saka kafa Sameer yake aje tashi, duk abinda Sameer ya mallaka mijinki ne sila komu iyayensa da kakanni muna cikin cin arzikin".
Zahra abin jinsa take wani bai-bai me hakan yake nufi ne wai? Ana nufin Mahmud ne ubangidan Sameer ko me ake nufi? Lallai biri yayi kama da mutum duba da yanda suke rayuwa a Nan daga lokacin da sukazo garin zuwa yanzu kusan umarni ne oga Sameer yake karba kawai kasa hakuri tayi Saida ta tofa tata tambayar.
"Wai ni Hajiya waye Mai gidan nan ne? na Ya Sameer ne? ko kuma na wani abokin nasu ne? Naga ya sakar musu ragamar ko Ina na gidan Baya tsoron abinda zeje yazo,nifa tsoro ma yake bani kamar baza'a mutu ba gaskiya ya mayar Dani gida inda nafi wayo, anan mutum saiya shagala da duniya wallahi".
Baki Hajiyar ta rike tana yiwa zahra wani kallo.
"Amma yarinyar nan lamarin ki da sauran gyara, gidanwa ze daukoki ya kawo idan ba gidansa ba, yo wannan ai Bai kama kafar gidajensa na sokoto da Abuja ba, ni duk naje Kinga na Abujan,? ganin likita naje lokacin Ina ciwon kafa, na sokoton Kuma bikin kanwarsa wadda take a can Germany mukaje, wannan mutane da karamci suke, gashi kinyi sa'ar suruka Hajiya zainab Bata da damuwa ko kankani" .
Tsai Zahra tayi da ranta Kenan da gaske shi Dan Sokoto ne kamar yanda ya fada Mata sannan da gaske sunan Babar tasa zainab din Kennan lokacin da take fadar iya Abu yace ta daina fada gatsal sunan surukarta ne ta dauka Wasa yake Mata wallahi kenan duk abinda ya fada ba joking a ciki.
"To ai shike nan nayi zaton ko gidan na wani ne muka Mike kafa a cikinsa"..
'Ko alama ranar dasu Hajiya Inna sukazo ai nayi zaton fa a Nan zasu kwana gurinki sai Kuma suka juya surukar Taki ce Bata samu zuwa ba sai ita kakarsa da matar kanin mahaifinsa, ki yiwa Allah ki taushi zuciyarsa yayi hakuri ya koma gida tunda Naga alamar kece Zaki iya wannan jahadin, wani irin fushi yayi da kowa har Amminsa abin ya shafa ranar da nace Miki su Hajiya innar sunzo Saida Tasha kukanta a dakina, wallahi Banda idan na Fadi ga inda yake abin ze iya shafar tarensu da Sameer da saina fada musu kodan samun kwanciyar hankalin Ammin tasa tafi kwanan watanni Bata gidan ubansa saboda rikicin da akayi a gidan yanda mijinki ya fice yabar gidan itama ta fice ta bar musu gidan, abunfa Babu dadi kiyi wannan aikin ladan Dan Allah ko an samu kwanciyar hankali a zuri'ar su.
Ita dai zahra Banda gyada Kai babu abinda takeyi, Dan ji tayi abin yafi karfin dan karamin tunaninta.
[2/1, 6:08 PM] ASHMAR🤍: ✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH
Page 46.
_______Sun Jima a gurin suna hira da Hajiyar tana Kara Bata labarin taren Sameer da Mahmud, anan tasan mamansa 'yar Niger ce Kuma cewa shi din da gaske twins ne su kamar na Ammah mace da namiji.
Suna nan suna hira har aka Kira sallah, da sauri Zahra ta tashi tana fadar "Hajiya Kinga guri Yana neman kurewa ban Dora miki abinci ba ko".
"Kinga dawo ki kaini inda zanyi alwala nayi sallah Banda kinibibi ki wani ce Zaki dafa min abinci, to Wanda Rahane da wannan yarinyar Dana gani akace tare kuka taho da ita Wanda suke faman aikinsa kuma ayi iri dashi? Ina fada Miki ki nutsu mijinki yawa ke garesu Kuma duk cikinsu mijinki daban ne sai kin koyi kamewa da gaske sannan Zaki fuskanci yanayin kowa Ina ke Ina wani dorawa Baki abinci banqiba dai in mijinki Zaki ringa yiwa wannan ba laifi,amma ba kowanne karabiti ba kice Zaki wani kama rawar jikin yi Masa, mujeni ki nuna min nayi dahara kafin a shiga sallah".
'yar Jakarta ta hannu ta daukar Mata suka nufi bedroom din da suka kwana.
Saida ta rakata har cikin toilet din ta nuna Mata duk abinda ya kamata sannan ta fito, sallaya ta shimfida Mata sannan ta karasa gyaran gadon da Bata Ida ba dazu ta saka freshner ta Daki ta rage karfin A/C din dakin. Hajiyar ce ta fito tana fadin "Ina dalili komai ya Zama na tab'e tab'e sai mutum yasha wahala kafin ya tantance yanda za'ayi"
Dan murmushi Zahra tayi "Haba Hajiya me yake da wahala saboda Allah?"
"Babu Miko min gyalena nayi sallah naji kamar an tada sallar"
Hijabin ta Mika Mata tana fadin "Bari naje na dawo ta nufi kofa ta fice.
"Ke tafi can Ashe duk abinda na fada Miki ta bayan kunnenki ya wuce Saida Kika fice Kika barmu da tashin hankali, jiya kukan da nayi rabona da yin irinsa tun rasuwar mijina. Amma Kika sakani maimaitwa Dan Allah ke kuwa 'yar Nan Ina Kika tafi jiya".
"Haba Hajiya Dan Allah haka mukayi da ke a gida kafin mu taho wato kin karya Alkawarin kenan? To a kazarki ta juma'a wallahi"
Ita dai Zahra borin kunya ta Fara "Allah ya Baki hakuri nifa na fada Miki kawai dai yawan mutane ya Hana ki gane waye yake Miki magana, Amma yaushe zanyi Miki haka Allah naji maganar ki kinga yanzu ma Zan Sha maganin fa".
Mahmud ne ya taso Yana fadin "Hajiyar mu ki shigo ciki ki fada min abinda ba'a so na sani Zan Baki abinda yafi kazar ma".
"Yauwa nasan kafi da haka, kanaji jiya ne wata daukakkiya ta tadawa yarinyar Nan hankali Wai kome gareta a mahaifa bansan dai sunansa ba da yaren Nasara Amma dai da hausa muna ce Masa tsiron mahaifa Wai sai tayi Mata tiyata,haka kawai ta ragewa zukekiyar 'yar Nan kwaliti yo an yanka mutum tun baiyi haihuwar fari ba Ina labari, shine nace baza'a yanka ta ba ga magani Nan Tasha na wata Daya in Sha Allah ze narke, ai sai daga baya Rakiya ke fada min ita waccan din ta Dade tana sonka tun Kuna turai koba haka bane? Ja'ira taga yarinya danya Sharab zata zauce tayi Mata illah to Banda abunka yaushe zaka ce buduwarka ta duba matarka ai wauta ce babba, wallahi kada a Kara kwatantawa, shine fa yarinyar nan tayi Mana batan dabo tun azzahar muka nemi 'yar Nan muka rasa nayi kuka kamar Zan yada idona to me zamu fada maka daga kawo yarinya ace ta Bata a gidana wallahi in takaice maka labari sai goma Sha biyun dare aka ganota ta Janbulo gidansu kawarta, itama uwar da yake ta kirki ce sai tayi tunani ta Nemo uwarta a waya take tambayarta duk da tana gurinta ta haka akasan guduwa tayi daga gurina cikin dare suka daukota to kaji yanda magana dai take".
Wani kallo ya yiwa Zahra Mai ma'anoni da yawa, sannan ya juya Yana kallon Sameer Wanda tunda Hajiyar makwarari ta Fara zuba ya sadda kansa kasa yayi Dana sanin kawota tafi cikin cikin masaki.
"To shike Nan in Sha Allah za'a kiyaye yanzu kiyi hakuri bata kyauta ba za'a duba korafin, nima ita ta tasoni na dawo ba Shiri wallahi hajiya yarinyar nan rikicinta yayi yawa".
"To ai tayi mini dai-dai ashe jikar tawa tasan kanta zo Nan Yar albarka".
Gurinta tazo ta zauna a kasa kusa da kafarata tana fadin "Hajiya Ina kwana?".
"Lafiya kalau ya jikin naki?"
"Nifa yanzu lafiya ta kalau ba damuwar komai".
Shima Muhmud Zama yayi kusa da ita da gani da shakuwa Mai yawa a tsakaninsu.
"Hajiyarmu kwana biyu Shiru ko nemana bakyayi ko?".
"Kaji kinibibi ta Ina Zan nemeka bayan kayi gudun hijira".
Dariya ya kamayi har ya bawa Zahra mamaki Daman Yana dariya haka.
Tashi tayi duk da Batasan Kan gurin ba Amma tana tunanin kitchen ne a cikin corridor din dake jikin dining area.
Babban tray ta dauko ta sako ruwa da lemo da Madara da plates ta dauko warmer din da aka zuba pepper soup din turkey din ta nufo parlourn ta dire cener table dake gaban Hajiyar tana fadin gashi Hajiyata ki Sha ruwa kafin nayi Miki girki yau fa a Nan Zaki wuni tunda oga ya dauke min Aunty Rukayya ko sallama bamuyi ba".
Inda Sameer din yake Hajiyar ta kalla "baka kyauta ba ai sai suyi sallama Mana kaga bataji Dadi ba".
"Ai zata dawo tunda zamuje Azare Nan da jibi".
Zahra na son taji ba'asin za'a tafi a barta Amma ba hali Dan tunda suka shigo ta kasa had'a Ido da Sameer da gaske ba karamar kunyarsa takeji ba.
Fita sukayi dare suka bar hajiya da zahrar.
Hira Hajiya ke Mata sosai tamkar sun shekara da sanin juna, taci Naman sosai Tasha madarar tana fadin "irinta muke Sha a makka laban kuke cewa ko tunda Sameer yace min mamarki balarabiyar Jordan ce ko?"
"Eh 'yar can ce".
"Ikon Allah ke Kuma Allah ya kaddaro naki mahaifin a wannan nashiya tamu, ai Sameer ya bani labarinki batun yanzu ba tun lokacin da mijinki ya kaini jidda akayi min aikin Ido da yaga wata yarinya diyar larabawa yake bani labarin ya ganki a jirgi keda wani mutum ko mahaifin ne ko Kuma dai mariki ne basu ba, Saida za'a daura Aurenki yazo yake dauko min tsohon zancen harna gane nace nasa a Ina suka laluboki yace min ikon Allah ne ya hada ku, daga Nan ban Kara ce masa komai ba, Fadima ki rik'e mijinki da kyau Yana sonki yanda Baki zato tun Baki San meye so ba yake Miki shi, kingan shi nan tun suna makarantar sakandire suke tare da Sameer Bai yadda shi ba, da Allah ya daukaka shi saiya Kara janyo shi jikin shi duk inda ya saka kafa Sameer yake aje tashi, duk abinda Sameer ya mallaka mijinki ne sila komu iyayensa da kakanni muna cikin cin arzikin".
Zahra abin jinsa take wani bai-bai me hakan yake nufi ne wai? Ana nufin Mahmud ne ubangidan Sameer ko me ake nufi? Lallai biri yayi kama da mutum duba da yanda suke rayuwa a Nan daga lokacin da sukazo garin zuwa yanzu kusan umarni ne oga Sameer yake karba kawai kasa hakuri tayi Saida ta tofa tata tambayar.
"Wai ni Hajiya waye Mai gidan nan ne? na Ya Sameer ne? ko kuma na wani abokin nasu ne? Naga ya sakar musu ragamar ko Ina na gidan Baya tsoron abinda zeje yazo,nifa tsoro ma yake bani kamar baza'a mutu ba gaskiya ya mayar Dani gida inda nafi wayo, anan mutum saiya shagala da duniya wallahi".
Baki Hajiyar ta rike tana yiwa zahra wani kallo.
"Amma yarinyar nan lamarin ki da sauran gyara, gidanwa ze daukoki ya kawo idan ba gidansa ba, yo wannan ai Bai kama kafar gidajensa na sokoto da Abuja ba, ni duk naje Kinga na Abujan,? ganin likita naje lokacin Ina ciwon kafa, na sokoton Kuma bikin kanwarsa wadda take a can Germany mukaje, wannan mutane da karamci suke, gashi kinyi sa'ar suruka Hajiya zainab Bata da damuwa ko kankani" .
Tsai Zahra tayi da ranta Kenan da gaske shi Dan Sokoto ne kamar yanda ya fada Mata sannan da gaske sunan Babar tasa zainab din Kennan lokacin da take fadar iya Abu yace ta daina fada gatsal sunan surukarta ne ta dauka Wasa yake Mata wallahi kenan duk abinda ya fada ba joking a ciki.
"To ai shike nan nayi zaton ko gidan na wani ne muka Mike kafa a cikinsa"..
'Ko alama ranar dasu Hajiya Inna sukazo ai nayi zaton fa a Nan zasu kwana gurinki sai Kuma suka juya surukar Taki ce Bata samu zuwa ba sai ita kakarsa da matar kanin mahaifinsa, ki yiwa Allah ki taushi zuciyarsa yayi hakuri ya koma gida tunda Naga alamar kece Zaki iya wannan jahadin, wani irin fushi yayi da kowa har Amminsa abin ya shafa ranar da nace Miki su Hajiya innar sunzo Saida Tasha kukanta a dakina, wallahi Banda idan na Fadi ga inda yake abin ze iya shafar tarensu da Sameer da saina fada musu kodan samun kwanciyar hankalin Ammin tasa tafi kwanan watanni Bata gidan ubansa saboda rikicin da akayi a gidan yanda mijinki ya fice yabar gidan itama ta fice ta bar musu gidan, abunfa Babu dadi kiyi wannan aikin ladan Dan Allah ko an samu kwanciyar hankali a zuri'ar su.
Ita dai zahra Banda gyada Kai babu abinda takeyi, Dan ji tayi abin yafi karfin dan karamin tunaninta.
[2/1, 6:08 PM] ASHMAR🤍: ✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI.
MAMAN FATEEMAH
Page 46.
_______Sun Jima a gurin suna hira da Hajiyar tana Kara Bata labarin taren Sameer da Mahmud, anan tasan mamansa 'yar Niger ce Kuma cewa shi din da gaske twins ne su kamar na Ammah mace da namiji.
Suna nan suna hira har aka Kira sallah, da sauri Zahra ta tashi tana fadar "Hajiya Kinga guri Yana neman kurewa ban Dora miki abinci ba ko".
"Kinga dawo ki kaini inda zanyi alwala nayi sallah Banda kinibibi ki wani ce Zaki dafa min abinci, to Wanda Rahane da wannan yarinyar Dana gani akace tare kuka taho da ita Wanda suke faman aikinsa kuma ayi iri dashi? Ina fada Miki ki nutsu mijinki yawa ke garesu Kuma duk cikinsu mijinki daban ne sai kin koyi kamewa da gaske sannan Zaki fuskanci yanayin kowa Ina ke Ina wani dorawa Baki abinci banqiba dai in mijinki Zaki ringa yiwa wannan ba laifi,amma ba kowanne karabiti ba kice Zaki wani kama rawar jikin yi Masa, mujeni ki nuna min nayi dahara kafin a shiga sallah".
'yar Jakarta ta hannu ta daukar Mata suka nufi bedroom din da suka kwana.
Saida ta rakata har cikin toilet din ta nuna Mata duk abinda ya kamata sannan ta fito, sallaya ta shimfida Mata sannan ta karasa gyaran gadon da Bata Ida ba dazu ta saka freshner ta Daki ta rage karfin A/C din dakin. Hajiyar ce ta fito tana fadin "Ina dalili komai ya Zama na tab'e tab'e sai mutum yasha wahala kafin ya tantance yanda za'ayi"
Dan murmushi Zahra tayi "Haba Hajiya me yake da wahala saboda Allah?"
"Babu Miko min gyalena nayi sallah naji kamar an tada sallar"
Hijabin ta Mika Mata tana fadin "Bari naje na dawo ta nufi kofa ta fice.