← Book details Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 47

Sashe 28

Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

****
Zaune suke Yana cin abinci ita Kuma tana duba sakonni whatApps har zata wuce salon Faisal saita dawo saboda Basu fi minti goma da Gama ways dashi ba Yana Mata magiyar ta turo da kudi suyi sarin Kaya, ta nuna masa ya jirata zasu shigo ganin jikin Abban nasu sai ayi abinda ya kamata, sai Kuma wata zuciyar ta kwabeta akan ta duba ita me majiyyaci ai share sako ba nata bane.
Ta maimaita karanta sakon ya Kai sau biyar tana ganin kamar ba gaskiya bane.
Dialing din number Faisal Aunty Surayya tayi, Yana dauka Bata jira komai ba ta jefa Masa tambaya.
"Shin text din daka turo min gaskiya ne".
"Eh wallahi Aunty ko jiya ma yazo gurin Abba mantawa nayi na fada Miki bakiga yanda yake kula da Abba ba kinsan har daki ya canza Mana mantawa nayi na fada Miki ayi Mana godiya gurin Auncle Mustapha".
"Ok shi kenan ina zuwa".
Ta fada tana yanke Kiran.
Auncle Mustapha ta juya tana kallo Wanda Shima ita ya zubawa idanu, batace Masa komai ba sakon ta bude ta Mika Masa.
Yana Gama karantawa ya dago da sauri yana neman Karin bayani.
"Nima shine na Kira Faisal din ya bani tabbacin haka ne, Wai ya Kai wani Babansa ne".
Spoon din ya aje ya mike ya zari hularsa da key din mota ya fice, Surayya na Masa magana hannu kawai ya daga Mata yayi gaba.

Duk yanda Aishat taso mahmud ya Bata hadin Kai suyi magana ya Kiya yace ta Bari sai dare zasu zauna suyi magana sosai.
Abincin ta shirya a table ta nufi dakin da zahra take, samu tayi barci ya dauketa a saman sallar da tayi sallah, Bata tasheta ba dawowa tayi tana fada Masa tayi barci da alama ta gaji.
Shida Abulkhairi sukaci abincin, yayin da Aishat ta dauki Afnan Wadda tayi barci ta haya da ita sama.
Kamar jira ake ta shiga bedroom dinta Kiran sweet heart ya shigo.
Tana dauka ya Fara fadin.
"Sweetie Ina Mahmud din yake Dan Allah?"
Saida taja fasali sannan tace Masa.
"Yana down stairs, wallahi sweet heart kamar Almara nake ganin abin duk na rude Dan Allah kazo kada ya Kara tafiya... Yace matukar na fadawa Abbie ko Ammi Bazan Kara ganinsa ba".
Ta fada tana share hawaye.
"Cool down your temper my sweetie Babu inda zaya, ban tsoro ne kawai yake miki yasan idan yayi Miki haka bazaki fadawa kowa ba, ki jirani zuwa gobe da safe in Sha Allah, ki daina yi min asarar hawayenki a banza, a gurina suna da mahimmanci , ki kyaleni dashi yanzu basai an Jima ba zanyi informing din Abbie gara ayita ta Kare tunda shi Abu baya wucewa a gurinsa".

"Gaskiya dai Kam ki shiga cikin Lamarin kuyi Masa taron dangi, kasan da wata yarinya yazo Wai 'yar gidan uban gidansa ce ya kawota Asibiti, nifa I doubt much akan yarinyar Nan kasan dai halinsa baya sabga da macen daba muharramarsa ba ya kake ganin ze dauko yarinya mace kamar wanna ka ganta kuwa? Allah Ina Jin ta hada iri da Larabawa Dan she is very young and beautiful".
"Just ka bishi a yanda yake so idan na shigo zamu Yara da yaren garinmu rabu dashi".
Basu wani Dade ba yayi Mata sallama Yana Kara kwantar Mata da hankali akan tunda ya kawo kafarsa har gida in Sha Allah komai yazo karshe.

A mota uncle Mustaphan ta karaso gidan duk da babu nisa Amma sai yaga idan yace ze tako a kafa kamar baze zo ba.
Directly part din Ammah ya nufa Don baya son maganar ta fita tun kafin su tabbatar da abunda aka fada, very lucky ya samu yayan nasa general a part din.
Batool ya bude Masa kofa ya shigo tana gaishe shi.
Ya amsa Yana fadin.
"Ina Abbie Amminku take?".
"Tana part din Abbie na cikin nan".
Ok, Bari na kira shi"
Ringing Daya ya dauka Yana fadin.
"Ko Ina kake Mustapha maza kazo Ina son ganinka ina kokarin kiranka naka Kiran ya shigo".
I
"To ai gani a part din Ammi Nima neman ka nakeyi".
Ya fada yana nufar kofar baya yabi corridorn da ze sada shi da part din General din".
Yana shiga da sallama a bakinsa yayi turus ganin Ammi tana shafe hawaye, a sanyaye ya karasa cikin parlourn.
"Lafiya! meya faru?".
"Zauna Mustapha yanzu ne Abbas ya kirani daga Jamaica inda yaje aikin da nake fada maka, wai Aishat ta kiwo shi ga Dan uwansa yazo Yana tare da ita".
Neman guri uncle Mustaphan yayi Yana tabbatar da gaskiyar maganar Faisal.
"To ai Nima abinda ya tasoni kenan na taho, kasan Alhajin su Surayya Yana can Indian an sake Masa gyaran kafa shine suka hadu da mahmud din yaketa dawainiya dasu shine ya fadawa surayyar tayi min godiya kasan ba kowa ne yasan case din da ya faru ba kawai dai an wayi gari ba'a ganinsa duk da zancen duniya baya buya nasar Surayya Bata fada musu komai ba gaskiya, Ammin Yara ki daina kuka ko lokacin da ake cikin tashin hankali ba Wanda yaga hawayenki sai yanzu da asking ya I gaban gashi".
Share hawayen tayi tana fadin "
dole nayi kuka ni kadai nasan dacin Dana ci a lokutan baya da dararen Dana Raya akan ubangijina ya dubi Lamarin yaron nan ya juyo min da hankalinsa gida".
"To godiya ya kamata ki yiwa Allah Daya amshi addu'ar ki ba kuka ba".
Wani murmushi general yayi yana duban Mustapha.
"Ni bansan lokacin data aje karar 'ya'yan fari ba da ko me zakayi musu Bata daga Kai ta dubeka amma yanzu dibi yanda take Kora bayani Kamar ba ita na".
"Kan barta tayi Yaya ai taking jarunta ma ba uwa duka ba, yanzu Yaya kenan za'ayi? Da nida madam zamuje next week amma dole mu raba tafiyar a yau Zan shiga neman visa ko nawa Zan bayar saina samu nan da jibi in Sha Allah Zan tafi Indian Zan kadi shi mu taho gida da izinin Allah. Amma dan Allah kada a fadawa Hajiya Inna wallahi idan taji cewa zatayi kafarta kafa ta".
"Kaje kayi shiri zanyi magana akan visar taka, ka Zama cikin shiri kawai".
Tashi Ammi tayi ta shiga ciki ta barsu suna tattaunawa akan Lamarin.

*****
Saida zahta tayi barci Mai isarta sannan ta tashi, wanka ta shiga tana fitowa lokacin magariba ta kusa kawo jiki, tayi mamakin dogon barcin da tayi.
Lotion kawai ta shafa sai roll-on da tasa sure sai body midt da normal turaruka da take amfani dasu designers na kamfanin Alharamaini, rigar atamfa ta saka simple style A shape ta yafa Karamin gyale sai tayi wani sansanyan kyau, a hankali ta bude kofar ta fito tana takunta gentle ta shigo parlourn Aishat ta gani a zaune da Abulkhairi a gefenta tana koya masa homework, kafin tayi sallama har sansanyan kqmshinta ya jewa Aishat.
Dago Kai tayi tana amsa sallamar da Zahra tayi.
"Masha Allah!"
Abinda Aishat ta fada kenan Dan babu karya yarinyar ta hadu ta ko Ina macece ga asalin kyau Dan gaske, murmushinta Mai kayatarwa zahra tayi Mata tana fadin.
"Sannu da hutawa Aunty".
Hannu Hanan ke dagowa Zahra tana zillo daga cinyar mamanta.
Daukarta tayi tana Zama daga dayan gefe Kan wata kujerar.
"Yauwa sannu, Zahra ko?"
Kaita gyada Mata alamar eh.
"Kinsha barcin gajiya, ga abincinki can Kan table muje kici kin kwanta da yunwa, bro yace na fada Miki yaje Asibiti sai dare ze dawo".
"Ok, nagode kiyk zamanki Bari muje da 'yar gidana Aunty ki bani ita Dan Allah Ina sonta".
Dan murmushi tayi idan mijin da Zaki aura ya amince ki dauka Ni tawa Mai sauki ne na Baki".
Gaba tayi tana dariya kasa-kasa ta nufi dining din save da Afnan.
Chapter 28 · 0% Book details