Sashe 12
Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tun bayan fitar zilai zahra ta wuce bedroom tabar Hajiya nacin abincin ta, a gurguje ta sake wanka ta gyara jikinta Bata wani Bata lokaci ba ta shirya cikin wata doguwar Rigar lace cotton Mai kalar blue black, anyi touching dinsa da silver ash yayi Mata kyau sosai.Bata daura dankwalin ba rolling tayi da ash din gyalen ta feshe jikinta da turenta ita abin har mamaki yake bata, ta rasa yanda akayi duk inda take sai taga turaren da take amfani dashi a gurin. Dan watsa hannu tayi irin baka gane Abu ba din nan.
Parlourn ta koma gurin Hajiya dai dai lokacin da su Sameer da Mahmud suka shigo.
"Bakin Hajiya ne yaki rufuwa data hango zahra ta nufo ta Fadi take "Masha Allah! Haka ake so wwnnan 'ya naga alama bazakiyi saken da za'a karbe miki miji ba, ki Kama abinki ki rike wallahi sonsa akeyi kamar goron hannun sarki ki matse kayanki tunda Allah kadai yasan gwagwarmayar da yasha kafin ki shigo hannunsa..."
Sameer ne ta katse Mata hanzarin zancen data dauko ya Fara fadin "ki tashi na mayar dake gida garin Zan Bari yanzu Banda kina Nan da nayi nisa a Hanya".
Shi kuwa Mahmud Banda kallon zahra ba abinda yakeyi gani yayi ta Kare Masa wani sanyin kyau a idanunsa, Kuma fir Taki yarda su hada Ido dasu duk kowa da kalar kunyar da takeji tasa.
"Hajiyarmu ya zaman guri Daya nasan kin gaji sosai ko".
"Mahmud din ta kalla Wanda ya nufo ta.
"A'a ban gaji ba ai wannan yarinyar da Abun gari take, jiya ma dai an Bata Mata Rai ne yasa na ganta Kamar marar wayo Amma yau ai ka gani sai Ina taka saka Dani takeyi".
"Dan Allah ki taso bana son nayi dare a hanya ke Kuma kin tsaya sai maimaita zance kikeyi, abinda ya wuce ai ya wuce".
Da sauri Zahra ta juya ta koma ciki ta barsu Sameer nata yiwa Hajiyar Dan zance, turarika da sabulai ta daukowa Hajiyar ta fito, lokacin Hajiyar na gyara lullubin gyalenta tana fadin "ai Zan dawo ne tunda ban karbo Mata dawa'in Dana saka ayi Mata ba a sanka, Kasan duk wannan jidaliyar ta jiya Bata Hana da almuru Saida Tofeek ya kaini Sanka naje na fadawa Malam karami ya taimawa jikata da maganin tsarin jiki Dana Baki, yo anyi sake Baki ya Kamata dubi fa yanda take tubarkalla, yo tunda ya fito da ita Nan ai magana kuma ta gare haka ze dunga reto da ita,to kasan wani idon da bakin ba masu kyau bane, shi yasa gara a dafata daga Nan" shi dai mahmud ban kunshe dariya ba abinda yakeyi yasan kadan da aikin Hajjaju ne hakan, shi Kuwa Sameer ya cika yayi fam shi yayi Dana sanin kawota gidan nan Dan Allah kadai yasan abinda ta fada Mata tunda kanwa Bata jiqa a bakinta.
"Wallahi Zan tafi na barki a gidan nan haba saboda Allah kin kama zance kamar an saka Miki batir".
Dakuwa tayi Masa ungo Nan. Dan nema kake wani zaro min Ido to tsoron ka zanji kome? wato gaskiyar ce baza'a fada ba".
Juyawa yayi ya nufi kofa da hanzari Hajiyar tabi bayansa itama zahrar da sauri tabi bayan Hajiyar, ji tayi an riko ledar da hannunta gaba daya ya dawo da ita jikinsa.
"Precious ba irin huge din Nan na welcome saiki wani shareni"
Ya fada Yana Dan goga Mata sajensa a gefen kumatunta cikin wani irin low voice.
Wani yar taji a jikinta.
Cikin shagwaba tace "Dan Allah ya Bari na rakata kada su tafi ban Bata komai ba, Kuma na saka Aunty zilai ta dafa Mata nama".
Juyota yayi suna facing din juna. "Baze tafi ba kawai ya gaji da surutun Hajiya ne itafa Bata gajiya da magana, kawo na gani dame-dame za'a bawa kakar tamu?"
Ya fada Yana duba cikin ledar.
"Inye ashe dai da wayonki irin wannan Abu haka? jazakumullahu khairan. Bari na Kara gyara Miki kudi ya Ciro daga aljihun wandonsa ya saka a ledar Yana fadin sai kice ta sayi man shafawa ko kice ta sayi goro, bari mu dawo ki bani abida ya samu, Kuma idan anjima Zaki rakani gidan su Sameer na gaishe da mommy sannan muje muga Mai sunana"
.
Bai saki hannun nata ba, a haka suka nufi kofar fita.
Taso ta zame hannunsa daga cikin nata tasan ba Karamin aikinsa bane su fita harabar a haka, kuma taga alama gidan da mutane da yawa ga kuma Hqjiya da Sameer.
Ganin kada ya Bata kunya yasa ya saki hannun ya rike ledar kawai kafin taje gurin motar ta shiga gurin su Aunty zilai ta gani ko angama.
Cikin ikon Allah ta samu an Gama soya Mata cikin roba, Ashe Daman tun safe suka dafa aka saka a fridge yanzu soyawa kawai sukayi, a ciki babban warmer aka zuba zilai ce ta dauko suka fito suka nufi gurin da suke tsaye suna jiran zuwansu.
Saida Motar tabar harabar gidan sannan suka juya suka koma, Saida suka wuce idanun jama'a ya janyota jikinsa Yana shagar kamshin jikinta, a haka suka shige ciki zame jikinta tayi tana Dan dubansa. "ga abinci Nan na kawo maka nan ko can table Amuje".
Dan bakinta ya shafa kadan ka Yana kwaikwayon maganarta..
"Bari nayi wanka sai muzo muci abincin nasan kema bakici ba ko?".
"Kai ta gyada masa.
Gurin da Hajiyar taci abincin ta gyara sannan ta dauko wata table mat da shimfida a kasa ta jera abincin, gurin kayan kallo taje da gani ko hadasu ba'ayi ba, ta tsuguna tana hadawa ya shigo, yayi wanka ya saka Riga armless da wando three quarter blue black na kamfanin Adidas sai fitar da wannan kanshin nashi yakeyi wanda har ya Zama constant a jikinsa, direct inda take ya nufa dago ta yayi "oya taso kibar wannan ba aikin ki bane akwai Wanda zaya hadasu".
Kai ta gyada masa ta bishi suka koma, abincin ta zuba musu sukaci Saida suka koshi, sannan ta tattara gurin ta dauke komai ta dawo ta zauna a gefensa.
Jikinta ya Dan kwanto Yana Dan matsa kafadar ta.
"Precious".
Ya Kira sunan sunanta.
"Na'am".
"Fada min me Haseenar ta fada Miki Kika yi yaji Zaki Kira min Ruwa? Banda Allah yasa Ammah tana yina da kin tayar min da zaune tsaye, ni na taho Ina mararin ki ke kuma kina gudun Zama dani ko?".
Sakin kafadar yayi ya kwantar da ita a cinyarsa suna facing na juna.
"Nifa na fada maka ba guduwa nayi ba to a cikinsu ai ba Wanda yayi min laifin da zanyi yaji? Kuma Dan lalacewa na tsaya Ina yiwa wannan Mai saffar mazan yaji,kawai dai Naga bazan iya tolerating na nonsense dinta ba,wato zatayi amfani da damarta tayi min illah tunda Nina hanata cikar muradinta ki? Ai naji ance tare kukayi karatu ba a UK? Dan Allah ka fada min waye Kai wallahi zuciyarta taki samun nutsuwa, abubuwan da nake gani a Nan sun girmewa tunanina, pls tell me, Me amor".
Tsuru yayi da Ido Yana kallonta Dan kalmar ta bashi mamaki data fito daga bakinta.
"A ina Kika iya yaren Portuguese?".
Ai Yana fadar haka ta bude Baki alamar mamaki da sauri ta yunkura zata fece ya mayar da ita jikinsa.
"Ya haka Zaki gudu daga tambaya".
"Nima bansan ko wane yare bane na fada sunan ne naji yayi min Dadi shi yasa na fada maka Ni ko ma'anarsa ban sani ba".
Ta fada tana Kara sunne Kai a kirjinsa.
"A'a idan ba Rami meya kawo zancen Rami? Meye na Jin kunya tinda kince Baki San ma'nar sunan ba duk da haka yau ranar Nan special ce a gurina badan da dutse tsakanin mu ba da Saina bada special gift Nima".
.
[2/1, 6:08 PM] ASHMAR🤍: ✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI.
✨✨✨
MAMAN FATEEMAH.
Page. 47
📖🖋️
________Duk yanda Mahmud yaso zahra ta bashi amsa abun yaci tura da gaske take kunyarsa Bata taba zaton Yana Jin yaren ba, shima kyaleta yayi dan bashi da amsar tambayarta a yanzu dai sai hakan yayi Masa dadi, wata hirar ya dauko Mata ta tafiyar da yayi da ire-iren cigaban da yake ganin makarantun mu zasu samu, har aka Kira sallar la'asar suna gurin tashi yayi suka shiga ciki yayi Shirin masallaci.
Misalin karfe takwas da kwata suka fito zuwa unguwar da zata raka shi, sunyi wata irin dacewa dole idan ka kallesu ka Kara, Dan kallonsa tayi "Zan leka na yiwa su Aunty zilai sallama".
Daka ya amsa Mata saboda Yana amsa waya.
A parlour ta iskesu suna Hira, a gurguje suka gaisa ta fada musu zasu fita, a dawo lafiya sukayi Mata ta juya ta nufi kofa har ta kusa fita ta ji maganar Aunty zilai bayanta.
"Uwar dakina Ammah tace a fada Miki ki bude wayarki tana son magana dake, yanzu ba dadewa ta kirani tace na Kai Miki tawa, na fada Mata Mai gidan Yana Nan shine tace to idan kin fito na fada Miki lallai ki bude zakuyi magana".
Dan rausayar da Kai zahra tayi da alamun damuwa a fuskarta.
"Ni wallahi na kasa bude wayar ne laifi nayi Mata fa".
"Laifi Kuma kina Nan tana can akayi laifin?"
Kai ta gyada Mata alamar Eh.
"Dan Allah ki bude wayar kuyi magana ko hankalinta ya kwanta,Allah a cikin damuwa take".
"To shikenan sai mun dawo din".
Ta fice tana amsa a dawo lafiyar Aunty zilan.
Motarta daya kawo ta gani, Wanda ya Kira da safwan dazu ya fito daga ciki da alamar shiya kawota nan seat din kusa da driver Mahmud ya budewa Zahra Yana fadin "Bismillah"
Saida ta zauna sannan ya nufo gurin safwan din yayi Masa magana sannan ya shigo ya tayar da motar suka nufi gate din fita, a dawo lafiya masu gadin sakayi musu Dan ba mutum Daya zahra ta gani ba.
Sunyi tafiya Mai Dan nisa kafin ya riko hannunta Bai kalleta ba gabansa yake kallo yace.
"Kina tambaya ta wannan gidan na wanene ko?"
Ya Dan juyo Yana kallonta.
"Eh" ta fada a takaice.
Parlourn ta koma gurin Hajiya dai dai lokacin da su Sameer da Mahmud suka shigo.
"Bakin Hajiya ne yaki rufuwa data hango zahra ta nufo ta Fadi take "Masha Allah! Haka ake so wwnnan 'ya naga alama bazakiyi saken da za'a karbe miki miji ba, ki Kama abinki ki rike wallahi sonsa akeyi kamar goron hannun sarki ki matse kayanki tunda Allah kadai yasan gwagwarmayar da yasha kafin ki shigo hannunsa..."
Sameer ne ta katse Mata hanzarin zancen data dauko ya Fara fadin "ki tashi na mayar dake gida garin Zan Bari yanzu Banda kina Nan da nayi nisa a Hanya".
Shi kuwa Mahmud Banda kallon zahra ba abinda yakeyi gani yayi ta Kare Masa wani sanyin kyau a idanunsa, Kuma fir Taki yarda su hada Ido dasu duk kowa da kalar kunyar da takeji tasa.
"Hajiyarmu ya zaman guri Daya nasan kin gaji sosai ko".
"Mahmud din ta kalla Wanda ya nufo ta.
"A'a ban gaji ba ai wannan yarinyar da Abun gari take, jiya ma dai an Bata Mata Rai ne yasa na ganta Kamar marar wayo Amma yau ai ka gani sai Ina taka saka Dani takeyi".
"Dan Allah ki taso bana son nayi dare a hanya ke Kuma kin tsaya sai maimaita zance kikeyi, abinda ya wuce ai ya wuce".
Da sauri Zahra ta juya ta koma ciki ta barsu Sameer nata yiwa Hajiyar Dan zance, turarika da sabulai ta daukowa Hajiyar ta fito, lokacin Hajiyar na gyara lullubin gyalenta tana fadin "ai Zan dawo ne tunda ban karbo Mata dawa'in Dana saka ayi Mata ba a sanka, Kasan duk wannan jidaliyar ta jiya Bata Hana da almuru Saida Tofeek ya kaini Sanka naje na fadawa Malam karami ya taimawa jikata da maganin tsarin jiki Dana Baki, yo anyi sake Baki ya Kamata dubi fa yanda take tubarkalla, yo tunda ya fito da ita Nan ai magana kuma ta gare haka ze dunga reto da ita,to kasan wani idon da bakin ba masu kyau bane, shi yasa gara a dafata daga Nan" shi dai mahmud ban kunshe dariya ba abinda yakeyi yasan kadan da aikin Hajjaju ne hakan, shi Kuwa Sameer ya cika yayi fam shi yayi Dana sanin kawota gidan nan Dan Allah kadai yasan abinda ta fada Mata tunda kanwa Bata jiqa a bakinta.
"Wallahi Zan tafi na barki a gidan nan haba saboda Allah kin kama zance kamar an saka Miki batir".
Dakuwa tayi Masa ungo Nan. Dan nema kake wani zaro min Ido to tsoron ka zanji kome? wato gaskiyar ce baza'a fada ba".
Juyawa yayi ya nufi kofa da hanzari Hajiyar tabi bayansa itama zahrar da sauri tabi bayan Hajiyar, ji tayi an riko ledar da hannunta gaba daya ya dawo da ita jikinsa.
"Precious ba irin huge din Nan na welcome saiki wani shareni"
Ya fada Yana Dan goga Mata sajensa a gefen kumatunta cikin wani irin low voice.
Wani yar taji a jikinta.
Cikin shagwaba tace "Dan Allah ya Bari na rakata kada su tafi ban Bata komai ba, Kuma na saka Aunty zilai ta dafa Mata nama".
Juyota yayi suna facing din juna. "Baze tafi ba kawai ya gaji da surutun Hajiya ne itafa Bata gajiya da magana, kawo na gani dame-dame za'a bawa kakar tamu?"
Ya fada Yana duba cikin ledar.
"Inye ashe dai da wayonki irin wannan Abu haka? jazakumullahu khairan. Bari na Kara gyara Miki kudi ya Ciro daga aljihun wandonsa ya saka a ledar Yana fadin sai kice ta sayi man shafawa ko kice ta sayi goro, bari mu dawo ki bani abida ya samu, Kuma idan anjima Zaki rakani gidan su Sameer na gaishe da mommy sannan muje muga Mai sunana"
.
Bai saki hannun nata ba, a haka suka nufi kofar fita.
Taso ta zame hannunsa daga cikin nata tasan ba Karamin aikinsa bane su fita harabar a haka, kuma taga alama gidan da mutane da yawa ga kuma Hqjiya da Sameer.
Ganin kada ya Bata kunya yasa ya saki hannun ya rike ledar kawai kafin taje gurin motar ta shiga gurin su Aunty zilai ta gani ko angama.
Cikin ikon Allah ta samu an Gama soya Mata cikin roba, Ashe Daman tun safe suka dafa aka saka a fridge yanzu soyawa kawai sukayi, a ciki babban warmer aka zuba zilai ce ta dauko suka fito suka nufi gurin da suke tsaye suna jiran zuwansu.
Saida Motar tabar harabar gidan sannan suka juya suka koma, Saida suka wuce idanun jama'a ya janyota jikinsa Yana shagar kamshin jikinta, a haka suka shige ciki zame jikinta tayi tana Dan dubansa. "ga abinci Nan na kawo maka nan ko can table Amuje".
Dan bakinta ya shafa kadan ka Yana kwaikwayon maganarta..
"Bari nayi wanka sai muzo muci abincin nasan kema bakici ba ko?".
"Kai ta gyada masa.
Gurin da Hajiyar taci abincin ta gyara sannan ta dauko wata table mat da shimfida a kasa ta jera abincin, gurin kayan kallo taje da gani ko hadasu ba'ayi ba, ta tsuguna tana hadawa ya shigo, yayi wanka ya saka Riga armless da wando three quarter blue black na kamfanin Adidas sai fitar da wannan kanshin nashi yakeyi wanda har ya Zama constant a jikinsa, direct inda take ya nufa dago ta yayi "oya taso kibar wannan ba aikin ki bane akwai Wanda zaya hadasu".
Kai ta gyada masa ta bishi suka koma, abincin ta zuba musu sukaci Saida suka koshi, sannan ta tattara gurin ta dauke komai ta dawo ta zauna a gefensa.
Jikinta ya Dan kwanto Yana Dan matsa kafadar ta.
"Precious".
Ya Kira sunan sunanta.
"Na'am".
"Fada min me Haseenar ta fada Miki Kika yi yaji Zaki Kira min Ruwa? Banda Allah yasa Ammah tana yina da kin tayar min da zaune tsaye, ni na taho Ina mararin ki ke kuma kina gudun Zama dani ko?".
Sakin kafadar yayi ya kwantar da ita a cinyarsa suna facing na juna.
"Nifa na fada maka ba guduwa nayi ba to a cikinsu ai ba Wanda yayi min laifin da zanyi yaji? Kuma Dan lalacewa na tsaya Ina yiwa wannan Mai saffar mazan yaji,kawai dai Naga bazan iya tolerating na nonsense dinta ba,wato zatayi amfani da damarta tayi min illah tunda Nina hanata cikar muradinta ki? Ai naji ance tare kukayi karatu ba a UK? Dan Allah ka fada min waye Kai wallahi zuciyarta taki samun nutsuwa, abubuwan da nake gani a Nan sun girmewa tunanina, pls tell me, Me amor".
Tsuru yayi da Ido Yana kallonta Dan kalmar ta bashi mamaki data fito daga bakinta.
"A ina Kika iya yaren Portuguese?".
Ai Yana fadar haka ta bude Baki alamar mamaki da sauri ta yunkura zata fece ya mayar da ita jikinsa.
"Ya haka Zaki gudu daga tambaya".
"Nima bansan ko wane yare bane na fada sunan ne naji yayi min Dadi shi yasa na fada maka Ni ko ma'anarsa ban sani ba".
Ta fada tana Kara sunne Kai a kirjinsa.
"A'a idan ba Rami meya kawo zancen Rami? Meye na Jin kunya tinda kince Baki San ma'nar sunan ba duk da haka yau ranar Nan special ce a gurina badan da dutse tsakanin mu ba da Saina bada special gift Nima".
.
[2/1, 6:08 PM] ASHMAR🤍: ✨✨✨
AUREN HUCE HAUSHI.
✨✨✨
MAMAN FATEEMAH.
Page. 47
📖🖋️
________Duk yanda Mahmud yaso zahra ta bashi amsa abun yaci tura da gaske take kunyarsa Bata taba zaton Yana Jin yaren ba, shima kyaleta yayi dan bashi da amsar tambayarta a yanzu dai sai hakan yayi Masa dadi, wata hirar ya dauko Mata ta tafiyar da yayi da ire-iren cigaban da yake ganin makarantun mu zasu samu, har aka Kira sallar la'asar suna gurin tashi yayi suka shiga ciki yayi Shirin masallaci.
Misalin karfe takwas da kwata suka fito zuwa unguwar da zata raka shi, sunyi wata irin dacewa dole idan ka kallesu ka Kara, Dan kallonsa tayi "Zan leka na yiwa su Aunty zilai sallama".
Daka ya amsa Mata saboda Yana amsa waya.
A parlour ta iskesu suna Hira, a gurguje suka gaisa ta fada musu zasu fita, a dawo lafiya sukayi Mata ta juya ta nufi kofa har ta kusa fita ta ji maganar Aunty zilai bayanta.
"Uwar dakina Ammah tace a fada Miki ki bude wayarki tana son magana dake, yanzu ba dadewa ta kirani tace na Kai Miki tawa, na fada Mata Mai gidan Yana Nan shine tace to idan kin fito na fada Miki lallai ki bude zakuyi magana".
Dan rausayar da Kai zahra tayi da alamun damuwa a fuskarta.
"Ni wallahi na kasa bude wayar ne laifi nayi Mata fa".
"Laifi Kuma kina Nan tana can akayi laifin?"
Kai ta gyada Mata alamar Eh.
"Dan Allah ki bude wayar kuyi magana ko hankalinta ya kwanta,Allah a cikin damuwa take".
"To shikenan sai mun dawo din".
Ta fice tana amsa a dawo lafiyar Aunty zilan.
Motarta daya kawo ta gani, Wanda ya Kira da safwan dazu ya fito daga ciki da alamar shiya kawota nan seat din kusa da driver Mahmud ya budewa Zahra Yana fadin "Bismillah"
Saida ta zauna sannan ya nufo gurin safwan din yayi Masa magana sannan ya shigo ya tayar da motar suka nufi gate din fita, a dawo lafiya masu gadin sakayi musu Dan ba mutum Daya zahra ta gani ba.
Sunyi tafiya Mai Dan nisa kafin ya riko hannunta Bai kalleta ba gabansa yake kallo yace.
"Kina tambaya ta wannan gidan na wanene ko?"
Ya Dan juyo Yana kallonta.
"Eh" ta fada a takaice.