← Book details Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 19 OF 47

Sashe 19

Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Itama zahra Bata kwanta ba sai kusan biyu da rabi bayan ta gama karatun Alqur'ani ta Fara nafifili sannan ta kwanta, harta gama addu'ar kwanciyar barci sai Kuma ta canza Shawara ta tashi ta dauko Jakarta tana fadin "Bari na kunna wayar nan ba turawa Ammah text na ban hakuri tayi breakfast dashi sai Kuma da Dan hantsi na kirata nasan zata huce ta saurareni lokacin, sannan na Kira bestie musha hurar yau she gamo".
Jakar ta dauko ta koma saman gadon Tana gyara Zama, duk iya binciken ta tayi Babu duk wani Abu Mai mahimmanci data saka a ciki, zazzage jakar tayi wayam kamar ba'a taba ajewa a cikinta ba.
Tagumi ta buga tana tunanin, to a Ina suka zube wadannan kayan? Kuma me yasa sauran Basu zube ba? ko jiya lokacin da suka fito daga gidan mommy komai Yana ciki Kuma ai ko daga motar Bata fito ba lokacin da sukaje sahad din.
Jiki ba kwari ta matsa tsakiyar gadon ta kwanta ita duk lamarin ya tsinke Mata wa zata tambaya Ina kayanta na jaka suke da wannan tunanin barci yayi gaba da ita.
Hudu da rabi Mahmud ya tashi as usual, duk da Daren da suka raba da Faruq besa shi ya makara ba, nafila yayi sannan yayi raka'atanul fajri ya fito Jin an Fara Kiran sallar na biyu, harya nufi Hanyar fita daga corridorn sai ya dawo baya ya tura kofar dakin da take, a kwace ya ganta tsakiyar gadon hular data saka ta cire gefe guda Ribom din shima yayi nasa gurin blanket din ya sauka har saman cikinta ga rigar ita da Babu duk Daya, a hankali yake shigowa cikin dakin kamar Mai tsoron kada ya tasheta, Yana Kare Mata kallo yanda tayi wani mahaukacin kyau a cikin dinligh din dakin, har ze tasheta saiya tuna condition din da take ciki ya juya ta fice daga dakin, yaso ya gyara Mata gashin Amma yasan matukar ya tabata sai ya sake alwalasa, a waya ya Kira Faruq ya fito su wuce masallaci.

A cikin barci taji kamar an bude kofa dakin, fargigit ta tashi tana addu'ar tashi daga barci, kamshin turarensa da taji ya hade dakin shiya tabbatar Mata daya shigo cikin dakin. A gurguje ta nufi toilet jin har an Fara sallah a masallatai, fatan ta Allah yasa har ta Idar Bai dawo daga masallacin ba Dan ita fa wallahi tsoronsa takeji Bata shuryawa abinda yake muradi ba...
[2/1, 6:08 PM] ASHMAR🤍: AUREN HUCE HAUSHI.

MAMAN FATEEMAH.

Page 50.

_______Tun idar da sallar Zahra ta shiga kakkabe gadon Tana dubawa ko Allah zesa tayi arba da tarkacen ta na cikin jaka amma ko alamarsu Babu dole ta hakura ta linke sallayar da hijabin Adana saboda tsaro.
Bata koma barci ba gyara dakin tayi duk da ba wani datti Dan da gani sabon guri ne da alama ma kamar a jiyan aka Fara amfani dashi Dan ko toilet din shima haka ne, Bata dauki dogon lokaci ba ta gama komai ta bazawa dakin kamshi Dan ga Room freshners Nan kamar anyi gorinsu, wanka ta shige, ta Jima tana gasa jikinta da ruwan dumi sannan tayi wanka ta fito haka nan taji tana son tayi kwalliya Sosai.
Zama tayi ta tsara light makeup tabi jikinta ta Sanya turaren gabobi Dana bayan kunne duk ta saka tunda gasu nan kamar ba da kudi ake sayensu ba, ita dai ta zubawa sarautar Allah Ido taga inda wasan ze Kare, clothset din ta nufa ta bude dayan bangaren, English wears ta saka riga da siket blue black masu ratsin fari a jikin coat din,rolling tayi da farin veil ta fito Shar da ita gefe gadon ta zauna tana karanta addu'ar Azkar din safe.
Su Mahmud Basu shigo gidan ba sai wurin bakwai tun bayan idar da sallar sukayi zaman karatun alqur'ani da Azkar din Suma a masallacin. Faruq yaso ya wuce gida amma Mahmud ya Hana shi yace yayi zamansa a Nan ze fiye Masa shi yau ze koma Nasarawa Daman akwai abinda yazo yi Nan din zuwa anjima Idan ya gama zasu wuce Kuma ma Basu gaisa da madam ba, part din Daya kwana ya wuce shi kumq Mahmud ya nufi sabon part din har ya Fara hawan steps din ya dawo Yana Kiran Faruq.
Shima gangarowa yayi Yana nufo Mahmud din Saida ya Karaso yace masa.
"Ina key din waccen car din akwai Kaya a baya za'a fito dasu".
"Oh! Sorry, wallahi na manta Yana ciki trouser din Dana sake jiya, harna na fito dashi na manta ban baka ba, daman ni ka barwa ita Naga tayi maka kadan motar five millions ai sai mu Kuma ma motar Mata ce"
"Nima ba tawa bace ta madam ce idan kana so ka tafi da ita kawai".
Baki ya rike alamar mamaki Yana 'yar dariya.
"Haba dai yaushe za'ayi haka da Wasa nake gani nayi dai tayi kankanta a gurinka harma ita din gaskiya".
"To Yaya kake son ayi kenan?kaga dai bani na Bata ita ba Babanta ya saya Mata Kuma saina ce batayi ba, Ina laifi da ake bani aro da ita fa nazo airport lokacin da zanyi tafiya,Kuma anan na aje ta harna dawo sannan na dauko Mata abarta, Kuma kawai saina ce Mata tayi kadan to ina wadda tafitan da Zan bata?".
Ya fada Yana kallonsa, shima kallon nasa yake yi, shi wani zance yake masa me Kama da zaurance me yake nufi da hakan Yana nufin a baibai ya ninketa kenan kome?.
"Pls jeka dauko min we will discuss later". Da sauri ya nufi ciki ya dauko key din suka nufi gurin da motar take.
Kayan ciki suka dauko, da gudu malam ya taho ya karbe kayan hannun Mahmud Yana fadin "Haba yallabai meye amfanin na a gidan da har zaka dauki kaya". Ya karba yayi gaba da sauri Faruq ba biye dashi suka nufi parlourn kowa da dauke da ledojin a hannau.
Har gurin dining table ya Kai kayan ya Dora kayan Faruq ma a Nan ya dora na hannunsa, Malam musa ne ya koma ya dauko sauran da suka rage a cikin motar.
Maimakon Mahmud ya shigo saiya Koma dayan part din bai jima ba ya fito rike da laptop da wayoyi tablet guda biyu.
A parlourn ya iske Faruq Yana tsaye kusa da wani freme Mai hoton wani tsibiri a tsakiyar teku gurin yayi matukar kyau sosai.
Jin shigowar Mahmud yasa ya baro gurin Yana fadin "gaskiya tsarin gurin Nan yayi kyau sosai banyi zaton ze kai haka ba kafin a gama".
Wani kallo Mahmud din yayi masa Yana aje abubuwan dake hannuwansa.
"Amma Faruq ka fiye gulma, Ina cewa Kaine ka zana ginin Nan da hannunka zakazo kana wani zance daban a Kai Kuma, ni zonan ka shigar min da wasu sakonni cikin laptop din nan jiya naso yin aikin ka hanani".
Ya fada Yana kokarin kunna wayoyin dake hannuwansa.
Saida ya nuna masa komai sannan ya nufi upstairs.

Tunda ya doso saman yaji wani kanshin Dadi Wanda ya kasa tantance Kona menene, direct dakin Daya kwana ya shige Yana son ya sake wanka yana son ya fita wasu sabgogin nasa wanda yaken son yayi da Kansa.
Ya shiga ciki ba dadewa Zahra ta fito ta nufi kasa tana ayyana bari ta duba Koda kayan amfanin kitchen Dana abinci tasan abinda ya kamata tayi kada ta Zama sakarya wadda ta rako Mata. Plat shoes ta saka fari tas dashi ta nufo down stairs din cikin takunta mai daukar hankali, Bata ankara da mutum a zaune ba Saida ta ahigo tsakiyar falon taja ta tsaya tana rarraba idanu tana son tantance ya fasalin ginin yake da inda ya Kamata ta dosa,.
Carab suka hada Ido dashi ya aje abinda yakeyi ya Zuba Mata idanu irin kallon Nan na wuce shari'a Yana tsarkake ubangijin da ya yi wannan halittar da take gabansa.
Dan zabura zahrar tayi ganin mutum ba zato ba tsammani.
Aje abinda yakeyi yayi ya taso har lokacin Yana kallonta Dan ja baya tayi ganin ya nufo ta.
"Ina Zaki Kuma nida na taso na gaishe da Aunty na".
Ya fada Yana murmushi, saida ya matso ta Dan gane shi, shine jiya ya rungume Mahmud a kofar store din da yayi sayayya.
Sai lokacin ta Dan nutsu amma da tana tunanin ta Ina zata fece ta Koma saman tasan ko banza tana da mafaka a can.
Dan murmushi tayi itama tana fadin "Yaya sunan bakon da babu sallama? Kawai na wayi gari da ganin mutun ai dole na rasana".
Dariya yayi Yana fadin "Good morning Aunty".
"Morning".
Ta amsa masa a dan darare din nan ba wani sakewa, tana kallonsa.
"I am Faruq Dange".
Ya fada Yana juyawa zuwa inda yake aikinsa.
A hankali ta bude bakinta tace Masa.
"Sunana Fatima Zahra Muhammad Sani, Ina maka.barka da zuwa".
Tana Gama fada ta wuce can inda ta hango Kaya akan dining table.
Sakato yayi Yana kallonta Bai taba tunanin tana Jin yaren ba, Kai kawai ya girgiza Yana dan murmushi Yana fadin "wato Ya Mahmud sai a barshi kawai sannin inda ya dosa sai Allah, shi yasa kenan duk yayi d'iban Karan mahaukaciya da matan daketa rashin hankali a Kansa yayi tafiyarsa ya kyale kowa da nata salon rashin hankalin".
Chapter 19 · 0% Book details