Sashe 11
Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gaba Daya ta fice daga part din, ta cikin barandar Nan tabi ta shiga babban part din, ko Ina tadal sai sanyi da sansanyan kamshi ke tashi Nan ma wani bangaren ne daban da gyar ta gano inda ta kwana saboda duk gurin shine parlourn da yafi kankanta Amma yafi sauran tsaruwa, a hankali ta bude dakin ta shiga yana nan yanda tabar Shi direct bedside din ta janyo wayar na Nan yanda ta ajeta Saida kudin America dollars data gani a ciki shiya Bata mamaki Daman dasu a ciki ta saka ko Kuma daga baya aka aje Dan tab'e Baki tayi tunda ba matsalarta bace, gurin mirror taje ta dauko kayan da Aunty Rukayya ta saya Mata ta dauko luggage dinta ta zuba kayan ta duka ta fito daga ciki, a nan parlourn ta aje luggage din ta wuce ta ratsa duk parlours din Shiru ba motsin kowa, ta nufi inda su Aunty zilai suke Nan ma shiru, ta dawo kitchen Nan ma shiru abin ya Bata mamaki to suna Ina ne? Hanyar fita ta nufa sai Kara jinjina maganganun da sukayi da Hajiya takeyi abin yayi matukar daure Mata Kai shin abinda Hajiyar makwarari ta fada haka yake ko Kuma rudun tsufa ne kawai.
Cikin sa'a tana fitowa ta hango iya Rahane ta bullo ta bayan wani gini da wani babban basket a hannunta, ganin zahra yasa ya tsaya tana fadin "ai Daga can nake nayi zaton ko tare kuka fita Maida Hajiyar makwarari da shiga naji Shiru a gurin naku".
"A'a Iya Ina nan Hajiyar ma tana nan sallah takeyi Ina wuni? Wallahi tun dazu naso fitowa to saiga Hajiya ita ta zaunar dani sai data shiga sallah na fito".
'yar dariya Iya Rahanen tayi "Lafiya kalau ya jikin naki? Sai Kuma ga Uban gidan mu yayi Mana zuwan bazata ko? Masha Allah, ai Hajiyar sai ku kai almuru Bata gaji ba kin Sha labari dai Kam".
"Lallai kam nasha hira, Wai Kuna Ina ne? Na duba banganku ba a can".
Rike Baki tayi kamar yarinya " ke! 'yar Nan ki rufa Mana asiri, Banda dalilin wadalilatan Ina mu Ina kwana a bangaren yallabai, tun sassafe muka dawo nan kafin Rukayya ta tafi, Bari na yiwa zilan magana ko?".
"A'a mu shiga kawai".
Tare suka karasa shiga cikin bangaren. Masha Allah guri ne Mai kyau tamkar gidansu na Azare abinda ya banbanta su kalilan ne tunda wancan Renovation ne,wannan Kuma haka aka tsara shi sai banbancin furnitures kawai, nan ma question mark tayiwa abun.
Jin sallamar zahra yasa zilai fitowa daga kitchen din tana fadin "Masha Allah, wallahi jiya ban samu kwanciyar hankali ba Saida Rukayya ta shigo tace min kin wuce Daki kin kwanta har Ammah na Kira na fada Mata Baku dawo ba, tace min na kwantar da hankalina ba komai tunda bake kadai Kika fita ba, Kuma sai muka wayi gari da zuwan yallabai? Ai ya shigo shida oga Sameer mun gaisa".
"Eh wallahi muna cikin gari gidan Hajiyar makwarari kakar oga har dare, kunyi waya da Ammah kuwa yau?"
Saita share zancen Mahmud din.
"Eh mun gaisa tun wurin karfe shida na safe har take tambayar ya jikin naki tunda wayarki Bata shiga, nace mata da sauki amma dai kun wuni a Asibiti Dan sai wurin Sha biyun dare kuka dawo".
"Ok.ba damuwa Bari na bude wayar na kirata sai yanzu na dauko wayar, Bari na koma na baro Hajiya tana sallah inaga yanzu ta Gama kada ta jini Shiru amma dai Zaki zo can din ko?".
Ta fada tana mik'ewa tsaye.
Zaro Ido tayi Kamar wadda taga abin tsoro.
"A'a wannan fa Daya ai jiya ba yau ba, sai dai In da abinda za'ayi Miki ki fada min ta waya sai nazo nayi Miki".
Sallama ta yiwa Iya Rahane suka fito tare da Zilan, Saida sukayi nisa sannan zahra ta tsaya itama Zilan tsayawa tayi.
"Aunty zilai me Kika fashimta daga lokacin da mukazo zuwa yanzu?"
Zahra ta jefa Mata tambaya.
"To abin ne da yawa gaskiya, Dan ni lissafina ya kwance gaba daya wallahi na rasa tudun dafawa Amma dai komai rintsin mijinki shine ke Jan ragamar gidan nan Dan dazu lokacin da oga Sameer ya kawo Hajiya naji suna magana da wasu ma'aikatan gidan Nan akan oga yayi zuwan bazata, sai Kuma lokacin Daya fito a can gurin Naga ya Tara su yana magana dasu oga Sameer Yana gefe harya gama oga Sameer ya rarraba musu kudi muma har ya aiki wani Wanda Naga ya shigo da waccen babbar motar ya kawo Mana dubu ashirin ashirin nida iya Rahane".
Ajiyar zuciya zahra tayi tana duban bangaren motocin hango motarta tayi a cikin parking lot din, kenan a Nan ya ajeta ko kuma jiyan yazo da ita Nan Dan kamar Bata ganta ba jiya, rausayar da Kai tayi tana wani tunani kafin tace.
"Muje kawai Aunty zilai mu zuba idanu a hankali gaskiya zatayi halinta, nifa duk hankalina ya koma gida Amma naji yana fadin zasuje Azare jibi za'a dawo min da Aunty Rukayya, Kinga ba zancen komawar mu kenan, ni Kuma abinda bazan yarda ba kenan ya ajeni a wannan gjdan da bansan asalinsa ba gashi Nan Kashi-kashi kamar gidan marasa gaskiya".
"A'a kada kiyi haka ki Bari kiga iya gudun ruwansa Mana nasan dai baze cutar dake ba, to kiyi Masa biyayya a duk abina ze umarceki matukar Bai sabawa shari'a ba,kiyi hakuri wata rana ma garinsu ze koma sai kice bazaki bishi ba? ai shi aure ba inda baya Kai mace, ki duba Maman Akwanga kin taba cewa tayi rayuwar Azare".
Haka zilai ta dunga tausar zahra har suka shiga part din da suka zauna Zahra ta dauki luggage dinta Zilan ta karba suka shiga ta ciki suka fito barandar nan zilai sai mamakin abin take Bata taba tunanin da wani ginin a bayan wannan ba, Bata Gama sarewa da lamarin ba Saida suka shiga ciki, a parlourn farko suka tarar da Hajiya ta rabsa uban tagumi ta zubawa kofa idon suna shigowa ta sauke ajiyar zuciya tana fadin "Haba 'yar Nan daga Bari na dawo Kika nemi gurin Zama Kika manta Dani saboda Allah kin kyauta min kenan? duk sanyi ya game min jiki har attishawa na Fara nasan mura Kuma sai abinda hali yayi kawai".
Da sauri zahra ta karasa kusa da Hajiyar tana fadin "Ayya wallahi nayi tunanin ko zakiyi nafilfili ne fa shi yasa na fita dauko wayata da kayana Dana Bari a wancen dakin, taso muje kici abinci kinji Hajiyarmu insha Allah bazakiyi mura ba, Aunty zilai Naga da kaji a can bangaren inda muka fito kiyi Mata irin pepper soup din da Naga kin yiwa Inna maimuna lokacin tana mura, ko a soya Mata ta tafi gida dashi".
"To in Sha Allah Bari naje ai kayan dazu wani mutum ya debesu ya mayar kitchen din part din da muka koma harma an karo wasu kayan masu yawa mun shafa'a mu nuna Miki su".
Ta fada tana mik'ewa ta nufi kofa ita Kuma zahra ta nufi dining ta daukowa Hajiyar abinci.
*** *** ***
Tunda garin Allah ya waye Mama ke faman Kai kawo a cikin Daki ta Kai gwaro ta Kai mari, tun bayan wayar da sukayi da Aunty larai hankalinta Bai kwanta ba sai yarfe gumi takeyi baji ba gani, ta Kira wayar Asabe yafi Shurin masaki amsar Daya ce switch off.
Wannan wane irin Abu ne Kullum tana tubkar gaba baya na warwarewa, Wai ita wannan Matar meta taka ne, duk abinda takeyi ya tashi a banza Kenan?
Tun bayan kaiwa Mai gadi sakon Nan Basu Kara samun damar shiga gidan Nan ba ko kofar ma tafi karfin zuwansu gashi yanzu Kuma aunty larai tazo Mata da wani Abun d'aga hankalin ga sako Amma isar dashi shine aiki ga wayar Asabe Bata shiga da sai ta Kai ko ta bayan gidan ne ta jefa abin bukatar dai ya shiga gidan ga sakon ya taho daga Jos din Kuma ance ba'a son ya kwana ba'a aiwatar dashi ba, akwai matsala Dan ze iya warware duk ayyukan baya, kuma wani aikin ze iya yin kome a Kanta ko 'ya'yan ta shine ta tada hankalin ta, tunda tasan idan tayi sake kwabarta ce zatayi ruwa, tayi tunanin ko sahura zata aika Tasha ta karbo sakon idan yaso sai tayi Mata bayanin yanda zatayi da sakon idan ta Kai can gidan zahrar, tayi tunanin ko zilai zata Kira tace Mata ta fadawa Zahra sahura zata je tayi musu share-share kafin su dawo, Nan ma taga abun ba lallai ya yuwu ba. Kara Kiran Asaben ta gwada still dai a rufe, dangwarar da wayar tayi duk abin duniya ya taru yayi Mata yawa.
Duk iya tunanin ta ya Kare ta rasa Ina ne mafita dole ta tashi ta fice daga dakin tana tunanin dole ta tura sahura taje ta Kirawo Mata Asaben in ba haka ba tasan watan Jin kunya ne yake neman Kama Mata.
Wannan kenan.
Tunda Ammah ta fita daga bangaren Abban take kokarin neman zahra Amma Shiru har bayan Azzahar inda taji Dadi da zilai tace Mata zahrar a gidan ta kwana Kuma Mai gidan ma yazo, tasan kome ne ne zezo da sauki. Banda kada yaron Nan Sameer yaga Kamar ta raina abinda yakeyi da yanzu ta tsufa a Kano, sakon text ta turawa zahrar ta tashi ya nufi bedroom dinta.
**** **** ****
Cikin sa'a tana fitowa ta hango iya Rahane ta bullo ta bayan wani gini da wani babban basket a hannunta, ganin zahra yasa ya tsaya tana fadin "ai Daga can nake nayi zaton ko tare kuka fita Maida Hajiyar makwarari da shiga naji Shiru a gurin naku".
"A'a Iya Ina nan Hajiyar ma tana nan sallah takeyi Ina wuni? Wallahi tun dazu naso fitowa to saiga Hajiya ita ta zaunar dani sai data shiga sallah na fito".
'yar dariya Iya Rahanen tayi "Lafiya kalau ya jikin naki? Sai Kuma ga Uban gidan mu yayi Mana zuwan bazata ko? Masha Allah, ai Hajiyar sai ku kai almuru Bata gaji ba kin Sha labari dai Kam".
"Lallai kam nasha hira, Wai Kuna Ina ne? Na duba banganku ba a can".
Rike Baki tayi kamar yarinya " ke! 'yar Nan ki rufa Mana asiri, Banda dalilin wadalilatan Ina mu Ina kwana a bangaren yallabai, tun sassafe muka dawo nan kafin Rukayya ta tafi, Bari na yiwa zilan magana ko?".
"A'a mu shiga kawai".
Tare suka karasa shiga cikin bangaren. Masha Allah guri ne Mai kyau tamkar gidansu na Azare abinda ya banbanta su kalilan ne tunda wancan Renovation ne,wannan Kuma haka aka tsara shi sai banbancin furnitures kawai, nan ma question mark tayiwa abun.
Jin sallamar zahra yasa zilai fitowa daga kitchen din tana fadin "Masha Allah, wallahi jiya ban samu kwanciyar hankali ba Saida Rukayya ta shigo tace min kin wuce Daki kin kwanta har Ammah na Kira na fada Mata Baku dawo ba, tace min na kwantar da hankalina ba komai tunda bake kadai Kika fita ba, Kuma sai muka wayi gari da zuwan yallabai? Ai ya shigo shida oga Sameer mun gaisa".
"Eh wallahi muna cikin gari gidan Hajiyar makwarari kakar oga har dare, kunyi waya da Ammah kuwa yau?"
Saita share zancen Mahmud din.
"Eh mun gaisa tun wurin karfe shida na safe har take tambayar ya jikin naki tunda wayarki Bata shiga, nace mata da sauki amma dai kun wuni a Asibiti Dan sai wurin Sha biyun dare kuka dawo".
"Ok.ba damuwa Bari na bude wayar na kirata sai yanzu na dauko wayar, Bari na koma na baro Hajiya tana sallah inaga yanzu ta Gama kada ta jini Shiru amma dai Zaki zo can din ko?".
Ta fada tana mik'ewa tsaye.
Zaro Ido tayi Kamar wadda taga abin tsoro.
"A'a wannan fa Daya ai jiya ba yau ba, sai dai In da abinda za'ayi Miki ki fada min ta waya sai nazo nayi Miki".
Sallama ta yiwa Iya Rahane suka fito tare da Zilan, Saida sukayi nisa sannan zahra ta tsaya itama Zilan tsayawa tayi.
"Aunty zilai me Kika fashimta daga lokacin da mukazo zuwa yanzu?"
Zahra ta jefa Mata tambaya.
"To abin ne da yawa gaskiya, Dan ni lissafina ya kwance gaba daya wallahi na rasa tudun dafawa Amma dai komai rintsin mijinki shine ke Jan ragamar gidan nan Dan dazu lokacin da oga Sameer ya kawo Hajiya naji suna magana da wasu ma'aikatan gidan Nan akan oga yayi zuwan bazata, sai Kuma lokacin Daya fito a can gurin Naga ya Tara su yana magana dasu oga Sameer Yana gefe harya gama oga Sameer ya rarraba musu kudi muma har ya aiki wani Wanda Naga ya shigo da waccen babbar motar ya kawo Mana dubu ashirin ashirin nida iya Rahane".
Ajiyar zuciya zahra tayi tana duban bangaren motocin hango motarta tayi a cikin parking lot din, kenan a Nan ya ajeta ko kuma jiyan yazo da ita Nan Dan kamar Bata ganta ba jiya, rausayar da Kai tayi tana wani tunani kafin tace.
"Muje kawai Aunty zilai mu zuba idanu a hankali gaskiya zatayi halinta, nifa duk hankalina ya koma gida Amma naji yana fadin zasuje Azare jibi za'a dawo min da Aunty Rukayya, Kinga ba zancen komawar mu kenan, ni Kuma abinda bazan yarda ba kenan ya ajeni a wannan gjdan da bansan asalinsa ba gashi Nan Kashi-kashi kamar gidan marasa gaskiya".
"A'a kada kiyi haka ki Bari kiga iya gudun ruwansa Mana nasan dai baze cutar dake ba, to kiyi Masa biyayya a duk abina ze umarceki matukar Bai sabawa shari'a ba,kiyi hakuri wata rana ma garinsu ze koma sai kice bazaki bishi ba? ai shi aure ba inda baya Kai mace, ki duba Maman Akwanga kin taba cewa tayi rayuwar Azare".
Haka zilai ta dunga tausar zahra har suka shiga part din da suka zauna Zahra ta dauki luggage dinta Zilan ta karba suka shiga ta ciki suka fito barandar nan zilai sai mamakin abin take Bata taba tunanin da wani ginin a bayan wannan ba, Bata Gama sarewa da lamarin ba Saida suka shiga ciki, a parlourn farko suka tarar da Hajiya ta rabsa uban tagumi ta zubawa kofa idon suna shigowa ta sauke ajiyar zuciya tana fadin "Haba 'yar Nan daga Bari na dawo Kika nemi gurin Zama Kika manta Dani saboda Allah kin kyauta min kenan? duk sanyi ya game min jiki har attishawa na Fara nasan mura Kuma sai abinda hali yayi kawai".
Da sauri zahra ta karasa kusa da Hajiyar tana fadin "Ayya wallahi nayi tunanin ko zakiyi nafilfili ne fa shi yasa na fita dauko wayata da kayana Dana Bari a wancen dakin, taso muje kici abinci kinji Hajiyarmu insha Allah bazakiyi mura ba, Aunty zilai Naga da kaji a can bangaren inda muka fito kiyi Mata irin pepper soup din da Naga kin yiwa Inna maimuna lokacin tana mura, ko a soya Mata ta tafi gida dashi".
"To in Sha Allah Bari naje ai kayan dazu wani mutum ya debesu ya mayar kitchen din part din da muka koma harma an karo wasu kayan masu yawa mun shafa'a mu nuna Miki su".
Ta fada tana mik'ewa ta nufi kofa ita Kuma zahra ta nufi dining ta daukowa Hajiyar abinci.
*** *** ***
Tunda garin Allah ya waye Mama ke faman Kai kawo a cikin Daki ta Kai gwaro ta Kai mari, tun bayan wayar da sukayi da Aunty larai hankalinta Bai kwanta ba sai yarfe gumi takeyi baji ba gani, ta Kira wayar Asabe yafi Shurin masaki amsar Daya ce switch off.
Wannan wane irin Abu ne Kullum tana tubkar gaba baya na warwarewa, Wai ita wannan Matar meta taka ne, duk abinda takeyi ya tashi a banza Kenan?
Tun bayan kaiwa Mai gadi sakon Nan Basu Kara samun damar shiga gidan Nan ba ko kofar ma tafi karfin zuwansu gashi yanzu Kuma aunty larai tazo Mata da wani Abun d'aga hankalin ga sako Amma isar dashi shine aiki ga wayar Asabe Bata shiga da sai ta Kai ko ta bayan gidan ne ta jefa abin bukatar dai ya shiga gidan ga sakon ya taho daga Jos din Kuma ance ba'a son ya kwana ba'a aiwatar dashi ba, akwai matsala Dan ze iya warware duk ayyukan baya, kuma wani aikin ze iya yin kome a Kanta ko 'ya'yan ta shine ta tada hankalin ta, tunda tasan idan tayi sake kwabarta ce zatayi ruwa, tayi tunanin ko sahura zata aika Tasha ta karbo sakon idan yaso sai tayi Mata bayanin yanda zatayi da sakon idan ta Kai can gidan zahrar, tayi tunanin ko zilai zata Kira tace Mata ta fadawa Zahra sahura zata je tayi musu share-share kafin su dawo, Nan ma taga abun ba lallai ya yuwu ba. Kara Kiran Asaben ta gwada still dai a rufe, dangwarar da wayar tayi duk abin duniya ya taru yayi Mata yawa.
Duk iya tunanin ta ya Kare ta rasa Ina ne mafita dole ta tashi ta fice daga dakin tana tunanin dole ta tura sahura taje ta Kirawo Mata Asaben in ba haka ba tasan watan Jin kunya ne yake neman Kama Mata.
Wannan kenan.
Tunda Ammah ta fita daga bangaren Abban take kokarin neman zahra Amma Shiru har bayan Azzahar inda taji Dadi da zilai tace Mata zahrar a gidan ta kwana Kuma Mai gidan ma yazo, tasan kome ne ne zezo da sauki. Banda kada yaron Nan Sameer yaga Kamar ta raina abinda yakeyi da yanzu ta tsufa a Kano, sakon text ta turawa zahrar ta tashi ya nufi bedroom dinta.
**** **** ****