← Book details Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 47

Sashe 24

Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

.............Sun koma asibitin sunga consultant g
Gynecology doctor sabuwar ce tazo daga federal medical center Birnin kudu, Dr Hajara yqrinya ce karama Amma tasan aikinta, so sai ta duba zahra ta turata ayi Mata special scanning saboda taga history na ciwonta a cikin file dinta.
Basu Dade a gurin scanning din ba suka dawo, tunda doctor din ta bude take jinjina Kai abun yayi matukar Bata mamaki, Saida ta aje result na scanning din sannan ta cire eye glasses din idonta.
"Dan Allah sister me ki kayi amfani dashi akan matsalarki ta fibroid? Ma'ana kin Sha wani magani na hausa Kona Islamic chemist haka akan matsalarki?".
Kai zahra ta gyada mata alamar eh.
"Pls my friend talk to me".
Ta fada tana murmushi.
"Eh nayi amfani da wani magani Amma Ina ganin black pepper ne kawai da kakata ta bani tace na ringa Sha da ruwan zafi Amma sai yayi twenty minutes Zan tace na Sha safe da yamma tace ze narke basai an yanka an cire ba, tace ma Yana maganin haihuwa Wanda baya haihuwa idan Yana amfani dashi eggs dinsa zeyi producing a samu haihuwa, tace min Yana magani sosai a bangaren ciwuwwukan Mata da suka shafi mahaifa, ko macen da bata haihuwa shima idan tana amfani dashi In Sha Allah zata Samu haihuwa, abinda ta fada min kenan".
Zahra ta fada tana kallon Dr din.
"Masha Allah, batayi karya ba Babu komai a cikin mahaifarki yayi dissolving ya wuce a cikin jinin da Kika zubar, Naga sun rubuta miscarriage irin haka ne yake kawo a batawa yarinya suna alhalin ba haka bane".
Ta fada tana kallon Aunty zilai.
"Kinga sister dina budurwa ce dal babu wata alaka data taba hadata da wani namiji na gani Dan haka ku bani number din Mama nayi Mata bayani nasan ba Karamin tashin hankali ta shiga ba a jiya nasan har yanzu Bata da nutsuwa da wata ce ma tana Nan tare damu ayi komai a gabanta".
Kallan kallo ake tsakanin Aunty zilai da zahra.
Me maganar likitan ke nufi da tace zahra budurwa ce? Tsatstsare Aunty zilai zahra tayi da Ido kafin ta juya ta kalli doctor Hajara kamar yanda ta gani a jikin Dan siririn freme a Kan table dinta.
"Nagode doctor Amma ba sai kin Kira Ammatah ba Bata kasar taje ganin likita tana da hawan jini ne Batasan ma bani da lafiya ba, ya pcv din Naga 48% ya Isa kenan?.
Murmushi tayi doctor din.
"Sister zahra ai yanzu haka sai ki bada jini,me 27% ma is ok basai an Kara masa jini ba sai dai a bashi maganin Karin jini".
"Ok tom shike Nan nagode kwarai sai an Jima" zahra ta fada tana tashi tsaye, har sun Kai Bakin kofar fita taji doctor din na fadin.
"Sister zahra bazaki bani number wayarki ba idan an tashi bikinki nazo Miki, bansan kowa ba a garin Nan daga Jigawa mukayi transfer nida mijina shima doctor ne pediatric banu Dade da Aure ba Ina son nayi kawa a nan".
Dawowa zahra tayi tana fadin.
"Ai kuwa na gode kwarai da gaske kawo na saka Miki number dina sai ki kirani Naga taki".
Ita dai Aunty zilai mamakin duniyar Nan ya cikata, har gurin mota doctor Hajara ta raka zahra saboda Bata da patient a ranar zata shiga ante-natal zasuyi awo.
Address din gidan Ammah ta bawa doctor din, sukayi sallama suka wuce, suna hanya mahmud ya Kara Kira yanda yaji muryar ta cikin nutsuwa yasan lamarin yayi kyau.
"I will call you later, we are on the way".
Ta fada Masa a hankali.
"Ok"
Kawai yace ya yanke Kiran.
Tunda suka shigo motar zahra ta hade gabas da yamma yanda Aunty zilai ma ba zatayi Mata wata magana ba, don taga yanda ta zaro Ido lokacin da doctor ke bayani.
Har kofar parlour zayyan ya kawo su ya sauke Yana fadin.
"Ranki shi dade Allah ya Kara lafiya".
"Allahumma Amin"
Zilai ta fada.
Ita ta bude kofar Zahra ta shiga, suna shiga ciki zahra ta juyo tana fuskantar zilan.
"Aunty zilai wannan maganar ta Zama sirri yarda da Aminci yasa nake yin abubuwana a gabanki tunda bamu taba samunki da wani abun ashsha ba, ko Ammah bana son taji labarin wannan abun Daya sameni Kinga dai ance babu ya wuce to zancen ya tsaya ya junan mu".
"In Sha Allah babu Mai ji uwar dakina, Amma wani hanzarin ba gudu ba, ko kuma dai a fadawa Ammah mijin naki bashi da lafiya sai a nemar Masa magani ai irin wannan ba'ayin shiru kada karamar matsala ta Zama Babba, yaro har yaro Amma babu lafiya".
Ta fada tana Jimamin abun.
Dariya maganganun ta suka bata ita bilhaqqi da gaske take maganar ta.
"Ki daina dariya wallahi ba abun dariya bane, yanzu saboda Allah kuja Baki kuyi shiru Dan yarinta, ai wannan ba Karamar matsala bace ba fa".
"Wai Aunty zilai waye yace Miki bashi da lafiya? Lafiyarsa kalau wallahi".
"Eh Daman lafiyar kalau Mana azahiri Amma a badini kuma ai Mai tsananin ciwo ne".
"Allah Ina fada Miki ba abinda ya sameshi fa".
Wani kallon Amma Baki da lissafi zilan tayi mata.
"Eh Naga lafiya a tare dashi tinda akace har yanzu kina nan a buduwarki Kinga kuwa ai lafiya ta tabbata a gare shi, yo ko waliyi ne aka aje Masa danyar yarinya kamar ki ya aje walittakar ya Raya sunna Amma shi yaro sharaf dashi ace ya Zuba Miki Ido tsawon watanni ai kinsan da matsala".
Ganin ba zata fahimce ta ba yasa Zahra fadin.
"Kinga Aunty zilai babu ruwan ki da shiga sangarsa ki Zuba Masa ido idan ma bashi da lafiyar ai ya sani ze nemarwa Kansa magani".
"Gaskiyarki Kuma fa babu ruwanw kada na dauko ruwan dafa kaina da kaina".
"Da dai yafi".
Bedroom Zahra ta wuce barci takeji sosai.

Tana shiga ta cire rigar jikinta wani wankan ta sake, fitowa tayi daure da towel sky blue a jikinta, jinta take wani iri Bata taba samun irin wannan bleeding din ba shi yasa duk ta takura.
Zama tayi tana shafa lotion na razac tana sonsa sosai, tana cikin shafawa taji ringing din wayarta a Kan bedside tashi tayi tsam ta nufi gurin sunansa ta gani Yana yawo Kan screen din, wallahi tausayi yake Bata ya kasa samun nutsuwa Kota sisin kwabo.
Video call ne, dauka tayi tana Masa sallama.
Tsura Mata Ido yayi yana tasbihi ga ubangijin da yayi wannan surar, wani yawu ya hadiye ba shiri, kashe mata Ido Daya yayi Yana dage girarsa ta hagu.
"Precious..,"
Ya kirawo sunanta in a deep voice, lumshe Ido tayi Dan sai taji yau sunan ya zamar Mata wani so special.
Gefen bed ta zauna ta Dan jingina da pillow a jikin gadon, sexy eyes dinta ta Zuba Masu kamar Zaiba a ciki kafin ta amsa Masa gently.
"Na'am.. meu Amor....".
Saida ya lashe lips dinsa saboda wani abu ya tsirga Masa cikin mararsa har Saida ya rufe Idanunsa, a hankali ya sauke su a kanta fal fitina Yana Mata wani kallon kasa-kasa.
"Kin tashi hankalina fa ba kadan ba, na rasa nutsuwa ta, hakurin zamanki nesa Dani ya Kare gaskiya bazan iya wannan jarumtar ba, gangar jina ke Nan Amma zuciyar tana Nan Kinga kuwa mutum ba zuciya ai babu mutum, ya jikin naki? Me suka fada da sukayi scanning din? naji zayyan na fada min wai sun ce miscarriage kikayi, nace a'a sai dai wani abun badai shi ba".
Gyara kwaciyarta tayi.
"Nima da farko haka suka fada Aunty zilai ma haka tace data gani, na fada musu bashi bane Amma Basu yarda ba, sai doctor din data dubani da safen Nan tace fibroid din ne yayi dissolving ya biyo period shine ya kawo heavy bleeding din, Kuma fa da har number din Ammah ta nemi na Bata Wai zatayi Mata bayanin abinda ya faru Dani tasan hankalinta ba a kwance yake ba ance 'yarta budurwa tana dauke da ciki tayi bari, gara ta fada Mata Babu wani Daya taba sanin yarta a matsayin mace lalura ce kawai, kasan muna dawowa Aunty zilai ta tsareni da maganar bamu da wayo Ashe baka da lafiya muke zaune bamu fadawa kowa ba ita zata fadawa Ammah a nemar maka magani tunda Amana ta turota gurina, da kyar fa na fashimtar da ita nace babu ruwanta ta barka ka nemi maganinka".
Dan cute pink lips din ta yake bi da kallo harta Gama bashi statement din.
Kankance Idanunsa yayi Yana Mata wani kallo.
"Gaskiya Kam maganar doctor gaskiya ce, Ni nasan har yanzu rainon a Bata nake yi koba haka bane? Kice da Auntyn ki ta Kira Mana Ruwa? da bazan Kara yarda mu hada ido da Ammah ba ai tonon sillil ne wannan shikenan na Zama ragon maza a idanunta".

Ai zahra Bata gane ta saki layi ba Sai daga baya, kunya taji ta rufeta.
"Nifa labari na baka ba Wai wani Abu ba".
"A'a gara na saka shimma kada a zaci da gaske ne, yanzu ita ta yarda bani da kuzari fa sai dai tayi ta kallona a haka koba haka bane?.

"Pls dan Allah mubar zancen Nan yafi karfina".

Murmushin nan nasa yayi mata yana fadin.
"Bayani zakiyi da yaren garinku yarinya gashi nan kin jamin ana min kallon wani lusari ko?".

Kira ne ya shigo Masa daga Asibiti, da sauri ya yanke Kiran Yana fadin.
"Bari na daga kirane daga Asibiti.

Yana sauka daga online tayi ajiyar zuciya Allah ya taimaketa, da Allah kadai yasan meze baro Mata taga alamar kamar hakurinsa Yana neman karewa, Dan wannan idanun nasa abinda suke fitarwa Yana Bata tsoro.

______

Maganar canza lokacin aiki sukayi masa saboda wasu dalilai da suka saka za'ayi Masa aikin gobe Dan haka suna iya shigowa sun fito da Baba Malam din daga investigation room din. Yana aje wayar Abubakar da Habib suka shigo, tashi yayi Yana fada musu su shirya zasu wuce Asibiti gurin baba Malam Wai sun canza ranar aikin gobe zasuyi Masa Ina ganin sun gano wani Abu daya zama dole aikin ya Zama emergency.
Chapter 24 · 0% Book details