← Book details Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 47

Sashe 34

Auren Huce Haushi Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Dan murmushi yayi duk da iyakarsa fuska.
"Babu komai kawai dai bana Jin dadin jikina ne".
Ya fada Yana karasawa kusa dashi ya gaishe shi ya Kara duba Jikin nasa, abinci ya dauko ya hada Masa yaci sosai sannan ya fada masa Yana son yaje Nigeria a yau in Sha Allah, addu'a yayi Masa sosai tare da Kara bashi Baki yayi hakuri ta koma ga iyayensa, sadda Kai kasa yayi kafin yace.
"A karayi Mana addu'a can na nufa idan Allah ya amince Mana".
"Kai! Masha Allah kazo min da abinda ya faranta min Raina mahmudu ubangiji yayi maka albarka ya Kara Kare ka daga dukkan sharri abin halitta Dan isar Manzon Allah s a w.w, kaje babu abinda ze faru da yardar ubangiji,Ina Kuma Fadimar ko ba tare zaku tafi ba?".
"Eh su sai jibi zasu taho da Hasanata wadda Dan uwana da mukazo dashi ya dawo ya kawota ta duba ka".
"Ikon Allah ai Bai min bayani ba yace dai ga iyalinsa tazo ta gaisheni, yanzu mahmudu daman takwayene Kai? Koda Wai ban taba sani ba, ko danma Kai ai saidai hamdala Amma me kake fada".
Murmushi yayi Yana Dan shafa sumar Kansa wadda Tasha gyara.
"Ayi hakuri yanayin ne yazo a haka".
"Babu komai hakan shine dai dai Allah yayi yagora ya Kara arziki Mai dorewa".
"Allahumma Amin".
Nurses ne Wanda suke bada maganj suka shigo, suka gaisa da malam Cikin harshen turanci sannan suka gaisa da mahmud da yarensu, magunguna suka bashi ya Sha sannan suka fice,Hira sukaci gaba dayi inda Baba malam ya dinga bawa mahmud Addu'oi masu karfi na tsarin jiki sanan ya Kara bashi wata yace ya dunga karantawa duk bayan sallar farilla in Sha Allah badai sihirin Dan mutum ba.
BISMILLAHI WA BILLAHI BISMILLAHI MASHA ALLAHU BISMILLAHI WALA HAULA WALAQUWWATA ILLABILLAH ÷ QALA MUSA MAJI'ITUM BIHISSIHIR INNALLAHA SAYUBDULUHU INNALLAHA LAYUSLUHU AMALAL MUBSIDIN FAWAQA'QAL HAQQU WA BADALA MA KANU YA'AMALUN FAGULIBU HUNALIKA WQNQALQBU AAGIRIN.
Godiya sosai mahmud ya yiwa Malam yace masa ze tafi Amma baze wuce sati daya ba ko biyu ze dawo tunda ya fadawa doctor kada a sallamar masa patient sai tafiyarsa ta nuna kukunna.
Yana fita ya Kira Mr salahuddeen yace su hadu a Airport ze dauko mota.
Karfe biyu da mintuna flights din su Mahmud ya dago Nigeria text kawai ya turawa Ya Abbas, itama Aishar ya tura Mata nata da bayanin komai.

Sayyid ya Jima a tsaye a parlour ko zaga ta inda Zahra zata bullo Amma yaga Shiru dole ya koma ya dauko coffee dinsa ya wuce dakinsa.
Bai Jima da barin parlourn ba Aunty Aishar ta sakko Cikin gayunta kitchen ta shiga ta Fara aiki tana tunanin irin yanda Hussein ya gindaya Mata dokoki akan matarsa tana ganin soyayya Amma sai take ganin Dan uwan nata yayi zurfi da yawa.
Tana Cikin aiki Sayyid ya shigo yayi Shirin fita school.
"Aunty Ina kwanq?" Ya fada Yana shigowa ciki.
"Lafiya kalau Sayyid har an fito yau da wuri haka? Gashi ko break ban Gama hadawa ba".
"No Aunty I am ok, Nasha coffee tun dazu, Wai Ni Aunty bakuwa kikayi a gidan Nan ne ko Kuma gamo nayi da safiyar Allah wata"Ala?".
Dariya tambayar ta bawa Aunty Aishar,duk yanda akayi yaga Zahra kenan, Amma sai tace masa.
"Meta faru Kuma kake wata magana irin haka?"
"Wallahi Aunty ba maganar jocking Naga yarinyar India ko larabawa a gidan Nan har fa Cikin kitchen din nan ta shigo muna had a Ido ta fice kamar walkiya ko dana fita ko Mai kama da ita bangani ba wallahi".
"Eh bakuwa ce nayi Baku San juna bane shi yasa ita ma Bata San da zamanka a gidan bane shi yasa inaga itama tsorata tayi gaskiya".
"Wow! Amma daga Ina Kika samo irin wannan Mai zafin haka? Gaskiya za'a da ita Dan Allah Ina kamu wallahi daga wannan Kuma kallo ya Kare ki Fara min campaign Dan Allah".
Ya fada Yana hade hannu irin ba 'yan kabilar Hindi na nan Indian din🙏🙏.
Anzo gurin tab Allah kiyaye da mijinta baya nan da a gabansa zeyi wannan kwabar da kuwa sun kwashi 'yan kallo.
"Wai kana nufi sonta jakeyi kenan?"
"Kwarai kuwa".
Ya fada da tabbatarwa.
"To ai matar Aure ce".
Dafe Kai yayi Yana fadin.
"Oh my God! Waye wannan Mai sa'ar da yayi min shigar sauri Dan Allah?".
"Wanda ya fika sonta ne ya dauke abarsa".
Langabar da Kai yayi Yana fadin.
"Shikenan na wuce school, Amma fa I really loved her".
"Matar Auren?"

Baice komai ba ya saka Kai ya fice daga kitchen din ransa babu Dadi. "Allah ya kyauta, wato mahmud ya yiwa Sayyid wani irin farin sani kenan, yasan matukar zeyi arba da ita sai an samu matsala gashi kuwa ya kasa ba marad'a kunya".
Sai da ta Gama komai ta dauko abincin data Zuba musu ita da zahrar a wani guri ta aje basket din ta koma ta dauko wani Abu kaman story mat da table mat ya shinfida sannan ta koma sama lokacin sweet heart din ya fito daga wanka, taimaka Masa tayi ya shirya tunda shi azumin litinin da alhamis yakeyi itama Aishar lalurar mu ta Mata ta hanata dauka, fita zeyi Yana da wasu ayyuka da Mahmud ya turo Masa Wanda zeyi masa su, tare suka gangaro Aishar ke fadar .
"Bari na kirawo Zahra ki gaisa tunda ba lallai yau ku hadu ba naji kace sai dare sosai zaka dawo aikin da yawa".
Dan janyota yayi jikinsa.
"Kyaleta ai Dan uwanki ya dasa Mana 'yar kunya a tsakaninmu tunda yayi mata irin wannan wawar rungumar a gabana kamar ze bude aiki kinji yanda jikinsa yake tsuma kuwa a lokacin?"

"Kai sweet heart Banda fa... Dan kaga baya kusa, shida abarsa har zakace Wai jikinsa Yana tsuma Kamar wani sabon shiga".
"Ni dai abinda naji nake fada Miki bawai Qage nayi masa ba, Kika sani ko farin shigar ne koma Bai shigan ba".
Ya fada yana dage Mata girar idonsa Daya.
"Wallahi Kai dai Yaya Babba ne, Banda irin haka da gani kasan ai Yana shanawa dubi fa yanda ya damu daga Dan turza shi da tayi yanzu ma kaji yanda yake jaddada min na kular masa da ita kamar wata jaririya".
"Ke dai mubar maganar lokaci ne ze nuna".
Har gurin mota tayi masa Rakiya tana fada Masa zasu fita fa.

Sama ta koma ta dauko Afnan wadda ta koma barci tun da akayi Mata wanka Dan kada ta tashi suna can bazajiyo kukanta ba.
Dakin Zahra ta Dan buga kadan tana fadin.
"Pls open the door" .
Jim muryar Aunty Aishar yasa Zahra tasowa da sauri ta bude kofar tana sakin murmushinta Mai kayatarwa.
"Ina kwana Aunty?"
Ta fada tana karbar Afnan dake barci, can tsakiyar gado Zahra ta kaita ta kwantar.
" Ki fito muyi break fast tun dazu na kawo na koma na sallami sweet heart ne shi yasa".
Tare suka jera zuwa gurin da tayi musu shinfida, abincin gargajiyar ba bahaushe tayi musu kunun tsamiya ne da kosai sai pepper soup din cow legs.
Suna gamawa Zahra ta kwashe kayan ta mayar kitchen ta wanke su ta aje komai a muhallinsa, taso ta yiwa Aunty Aishar magamar guy dai data gani sai wata Zuciyar ta kwabeta, Bata sani ba ko kaninta ne shaqiqi muharraminta.
A gurin ta dawo ta Sami Aunty Aishar tana amsa waya daga ganin yanda take amsawa kasan ba wayar sawa bace Mai wayar Yana da girma da kima a idanunta.
Zahra Bata zauna ba ciki ta shige tana shiga taga Afnan tana daddaga kafa tana Wasa ta tashi, daukarta tayi tana fadin.
"My Afee Babyyy.."
Yarinyar na ganinta ta Fara dariya shaidar ta ganeta kenan.

Saida Aunty Aishar ta Gama wayar ta shigo tana fadin.
"Au Kice mutuniyar ce ta tashi? Sai ki shirya fita zamuyi yanzu guri ya kure sosai kinsan Hussein shi komai nasa baya fada sai guri ya kure, sosai jibi fa zamu wuce Nigeria shine yace muje kasuwa kiyi tsaraba shi ya wuce Nigeria".
Da madaukakin mamaki Zahra ta dago ta kalli Aunty.
"Ya wuce Nigeria?"
Sai idonta yayi kwal-kwal ta tabbata abinda ya fada gaskiya ne, shikenan ita Kuma haka tata kaddarar take.
Girgiza Mata Kai Aunty Aishar tayi.
"Haba Banda shagwaba Mana, keda kike fushi dashi, yasan ko yazo bazaki saurarasa ba shi yasa ya tafi tunda baisan laifin da yayi Miki ba kike dafa shi da naki salon, Dan Allah a rangwanta Masa shi bako ne a cikin soyayya Bai taba yinta ba ke Kuma Naga taki da zafi ta kamashi batayi Masa da Wasa ba".
Da kyar ta iya mayar da hawayen, da suka so zubowa ta rasa dalili itama tata zuciyar Bata da wani karfi a Kan lamarinsa.
"Shike nan Aunty inda sabo na Saba yayi tafiyarsa Bai fada min ba".
Aunty Aishat ji tayi yarinyar ta Bata tausayi, kenan shima Yana gwada Mata halin miskilancin nasa, nata ne baya iya jurewa.
"Ki rabu dashi tafiyar ce tazo masa ba zato kiyi hakuri dole zamu zauna ya daina Miki irin haka tunda ke ba sanin halin yawonsa kikayi ba, inaga duk duniya Amminsa kadai yake bude Baki ya fada Mata duk inda zaya a cikin duniyar nan kafin yayi fushi kenan".
Chapter 34 · 0% Book details