← Book details Al'ajabin So Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 36

Sashe 22

Al'ajabin So Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Kana lafiya kuwa?"
Ajiyar zuciya ya sake sauƙewa kan ya ɗan girgiza kai sai kuma ya gyaɗa kawai.
Rita tayi saurin cewa
"Ko dai Maaminka ce ke pressurizing ɗin ka? Matar abin da take yi bata kyautawa, kaman babu zuciya a ƙirjinta? Anya ita ta haif..."
"Shut uppp! U are very stupid mahaifiyata kike kokarin jefa da kalaman raini? I won't take that wlh kika sake ko da ambatan sunanta ne sai kin sha mamaki na.."
Yana kai nan ya ture ta ya fice daga wurin kujerun ya koma gaban table da masu kula da wurin ke ta sarrafa barasarsu ana cigaba da bawa masu siye wasu har da ƙanƙara ciki.

"Wadda ya fi kowanne ƙarfi"
Abinda ya faɗawa bar attendant ɗin kenan, shi kuwa ya san waye mukhy ya soma haɗa mishi kaman yadda ya buƙata ya gama ya tura mishi, cup ɗin ya zubawa idanu ya jima yana kallo kan ya kai hannu ya ɗauka yana ɗan jujjuya shi a hannunshi da alama dae contemplating yake ya sha ne ko kar ya sha, bakinshi ya kai da nufin sha sai yaji kaman muryan Baba na ce mishi
"Duk wadda ya dawwama yana shan giya har ya mutu Allah ya haramta masa aljanna, ko ƙamshinta ba zai ji ba bare ya shige ta"
Jifa yayi da kofin ta tarwatse ya miƙe ya nufi waje kaman kumurcin maciji, motanshi ya buɗe zai shiga yaji an riƙe shi

"mukhy Meke damun ka ne haka? Is something wrong?"
Juyowa yayi sai ya kallesu har su uku ne, Pepe, smart da Nawwaz ne, Smart da yayi maganan ya maida hankali kanshi yace
"I don't really know wlh smart, bana jin daaÉ—in komai i feel lonely, tired nd lost"
Pepe yace
"ko dai ka gaji da Rita kana son chanza Babe? Though na san Dukda kana tare da ritan kayi Ƴan mata dayawa."

"Ko sha'awar jin sunansu bana yi bare har in raɓesu, I hate everything wallahi tun jiya ko runtse idanuna na kasa da sunan bacci"
Shiru suka É—an yi kan Nawwaz yace
"maybe you need space for Little bit ka É—an huta, da dai zaka iya da mun koma ka zama high sai ka fi samun natsuwa da bacci yadda ya kamata"
Kai ya girgiza ya juya zai shiga mota smart ya riƙe hannunshi
"ba zamu barka kake driving kai kaÉ—ai cikin wannan hali ba, zamu dinga kasancewa tare da kai har ka dawo daidai ko ya kuka ce?"
Ya tambayi saura suka ce hakane a tare suka shishiga motar, Smart ya ja suka fice daga harabar wurin.

****

Hawayenta ta share tare da ɗaga kai ta kalli saman ɗakin mutane are very wicked a wannan zamani namu, su kan manta cewa duniyar kwata-kwatarta bata da wani girma kuma aron rai aka bamu muke zama cikinta, bata san me zata kira iyalan Hassan dala dashi ba, menene suke dashi against waennan bayin Allahn? Ko rantsuwa tayi bazata yi kaffara ba akwai tsantsar son zuciya, hassada da baƙar kyashi a tare dasu waenda duk mugayen ciyuka ne masu zaftare imani ya ɗaiɗaita natsuwa da farin ciki, godiya ta cigaba da yiwa Allah da ya sa umar na gari da bata san yadda zata fuskanci Alayah ba idan ta farka, dole hankalinta ya tashi ta shiga damuwa saboda uwa ai wata giɓi ce da rasa ta rayuwa babban asara ce wadda mai da irin ita babu har Abadan Abada.

Banko kofan da aka yi ne yasa ta buÉ—e idanunta tana kallon Alhj hammad da ya shigo har huci yake sbd fushin da bata san a ina ya kwaso ba yake shirin zuwa kanta ya juye mata kwandunansu.

"Lafiya kuwa Alhj? Ya zaka bangaje kofan asibiti haka kuma babu sallama ka s...."

"Shut uppp!! Ki dakata min Fatima, uban wa ya baki izinin kutse cikin ahalin Hassan dala? Menene naki da rayuwar gidanshi? Ina ruwanki da komai na gidan?"

Ranta ta haÉ—e tace
"ban gane ba, saboda na ceci ran da yake gangaren mutuwa a hannun waenchan azzaluman laifi ne? Na san abokinka ne Dukda abotarku be taɓa burgeni ba hasali ma na tsani alakarku saboda Hassan zuciyarshi babu Allah cikinta na daɗe da fahimtar hakan to ba zan zuba idanu a cigaba da zaluntar bayin Allah nan ba ko me zaka ce sai dae ka ce"

"kin san me kike kokarin aikatawa? Kin fa san siyasata idan ba Hassan kaman babu ita ne, taya zaki yi kokarin yi min asarar mutum irin shi a gab sa'ar da burin raina ke gab da cika? Har ki aiki wanchan banzan É—an n..."
Da sauri ta katse shi
"Umar ba banza bane Muhammad, kuma ba zai taɓa zama banza ba, ina zuciyar imaninka ya shiga ne? Cikin fa najasar kashi da fitsari, ɗauke da zazzafar stroke da hawan jini ya haddassa wanda ya assassawa matar chan shiga cikin come ya fiddo ta, shin wannan be zama abin alfahari ba? Menene laifin umar da ka ɗaura mai karan tsana saboda kawai ya saka idanu kan al'amuranka ya kuma tsaya tsayin daka wurin hana ka aikata mummunan laifin illata rayuwar matasa a cikin al'umma? Kar ka zama Hassan din mana! Kar zuciyarka ta yaudare ka wurin auren duniyar nan mana Abban Mukhtar.."
Ta ƙarasa da karyayyen hawaye.

"Ina ruwanku? In ma abinda ya fi fitsari da kashi ne ko comar banza ne duk babu ruwanki, ina ce nine na ɗauki yarinyar nan na aurawa Mukhtar? Toh zan saka shi ya sake ta ki tattara ta da ita da uwar da kuka jajibo ku watsar don wallahi zaki fuskanci mummunan ɓacin raina idan kuka yi sanadiyar lalacewar siyasa ta"
Ya ƙarasa kaman zai kifa da ƙasa don masifa, har ya juya ya nufi kofa yaji Maami na cewa
"ko menene zaka yi yanzu kam sai dae kayi Abban Mukhtar yanzu case É—in ba tsakanina da Hassan bane tsakanin Umar da Hassan ne, shi zaka ja wa kunne amma ba ni ba"

Juyowa yayi ya watsa mata wani irin kallo kan ya juya ya fice yana sake buga kofar, kanta ta maida ƙasa ta sake silalar da hawaye kan ta share ta juya ta fice don duba Ummi dake ICU tun jiya ko motsi bata yi ba kaman yadda Alayar ma take ta bacci tun a jiyan don daga ta tashi za'a sake mata allura ta koma tana bukatar cikakken hutu.

Maami na fita ta buɗe idanunta tare da kurawa kofan, hawaye ne taji yana cika mata ido wato in ka hangi Maami daga waje zaka rantse da Allah cewa ta gama samun komai a rayuwa tana cikin daula da hutu ga kuɗi masu maganin matsaloli amma ba hakan ba ce mai ɗaki shi ya san inda yake mishi yoyo, ashe bayan jarrabawar Mukhtar tsakanin ɗaya ɗan ta da mahaifinshi babu zaman lafiya? Amma kaman maganan ummi ake? Sai yanzu kalaman ya ɗaukota cikin najasar kashi da fitsari da stroke wanda hawan jini ya haifar sanadiyar hakan tana cikin coma da wani irin hanzari ta miƙe zaune tare da fisge ruwan ba tare da ta damu da jinin da ya cigaba da bin tsintsiyar hannunta ba tayi saurin saka takalmi tayi waje.

Bayan Maami kawai ta hanga hakan yasa ta haÉ—a da gudu tana kiran sunanta, da sauri Maami ta juyo tana ganinta ta nufeta tana salati
"Menene haka Alaya? Meyasa zaki fusge ruwa daga jikinki haka? Dubi fa jinin dake zuba?"

"Maami Ummi na ce? Ummi ce kuke maganar Shiga coma? Me ya sameta ummi? Garin yaya? Taya hakan zata kasance.....innalillahi wainna ilaihi rajiun..""
GabaÉ—aya ta ma ruÉ—e ta gigice
"Ki natsu Alayah tana cikin salama in shaa Allah Adu'a kawai take buƙata a halin yanzu daga gareki ba wannan kukan da ɗaga hankalin ba, in shaa Allahu yanzu ummi ta dawo wurina kenan har Abada ko da tana so ba zan bar ta komawa cikin uƙubar da ta fito ba"
Maami ta ƙarasa da alhini, da sauri Alayah ta rungumeta
"Na gode Maami mun gode sossai Allah ya saka miki da alkhairi, Allah ya biya miki buƙatunki na alkhairi ya saka ki cikin aljannah maɗaukakiya"
Har lokacin bata daena hawaye ba, tana cikin wani sabon damuwar duba da yadda saɓani ke shirin shiga tsakanin Maami da Abban saboda su kuma.

Jan ta Maami tayi zuwa É—akin da aka kwantar da ummin, daga jikin window suka tsaya Alayah ta É—aura hannunta bisa kai tana sake zub da hawaye, ummin ta ce haka? Me ya faru bayan barin ta gidan? Taya duk waennan abubuwa suka faru ba tare da ummin ta sanar mata tun wuri ba? Ummin ta aka bari da najasa Allah andi tsawon lokacin da ta É—auka a hakan, kuka ta sake saki.
"Ashe ba zaki ji magana ta ba Binty? Ban ce ki daena É—aga hankalin nan ba saboda yanayin ki? Toh shikenan kiyi ta yi"
Ta ƙarasa tana juyawa alamar tayi fushi da sauri Alayah ta riƙe hannunta tana anfani da ɗayan hannun wurin share hawayenta tace

"Na daena Maami, wlh na daina ki yi hakuri"
"yauwa ko ke fa? Mu je ki kimtsa ki samu ki ci wani abu sai a ƙara duba ki ko?"
Kai ta gyaɗa suka juya suka nufi ɗakin ta, wanka tayi bayan ummi ta haɗa mata ruwa ko da ta fito ma ta samu ƙannen Maami Aisha da ruqayyah tare da wasu ƴaƴan yayyunta maza sun shigo, da farin cikin ganinta hakan suka shiga amsa gaisuwar ta suna mata ya jiki? Tana amsawa da jikin da sauƙi sossai, abinci ta ci wanda yayi mugun mata daaɗi faten dankalin turawa ne aka saka mishi ugwu ya ji kifi ice fish, bayan ta gama nurse da Maami suka shigo ta kara dubata kan ta mayar da ruwan, kwanciya tayi tare da juya bayanta idanunta a lumshe.
Chapter 22 · 0% Book details