← Book details A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 33

Sashe 7

A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai tashiga girgizawa, ahankali tafara magana, babu inda zanje dannasan rayuwata tazo karshe, sede ina neman wata alfarma agurinka. Sarki yace inajinki, kadubi girman Allah, kamar yanda Allah yadauka kaka, yafifitaka sama da sauran bayinshi badan yafisonka ba, nasan matsayinka ya girmi alfarmar dazan fada maka, sede inason kayi jahadi domin ka ceci marainiyar Allah daga fadawa wata rayuwa.

Sarki yace inajinki, kifadi koma menene nikuma namaki alkawarin zanzamo mecika makishi. Waziri, Qaseem sukayi saurin kallon Sarki jin abinda yafada batare dayasan me matar zata fada ba.

Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]

Season 35⚜40

Zaune suke a falon Malam Bello na Darazo, Sarki ne, se Qaseem da Waziri. Malam Bello babban malami ne, kuma attajiri, duk da yamanyanta amma sbd ilimin dayake dashi idan kaganshi zaka dauka shekarunsa basu kai nashi ba. Shine babban malamin garin Darazo malamin sosai, yana temakon mutane dayawa agarinsu, mutanen garin suna matukar sonshi da girmamashi.

Hakan yasa yagina katon gida me bangarori dayawa, ko yaranshi maza 2 dasukayi aure acikin gidan suke zaune da matansu, da yaransu, dama kuma beda yara dayawa yaranshi 4, maza 3 mace 1, itama tayi aure acikin garin bauchi. Matarshi daya uwar yaranshi, se kanwarshi kuma autar gidansu, tunda mijinta yarasu bata kara aure ba, dama kuma bata taba haihuwa ba, hakan yasa tace bazata kara aure ba, itama ta manyanta akalla zatayi shekara 35.

Mutane dayawa idan sukazo garin basuda masauki yana basu guri acikin gidanshi, ko idan ya musuluntar da wasu yana basu gurin zama, yana da dalibai dayawa dayake karantarwa. Haka kuma baya aiki da aljanu, sede yana fitar dasu kuma suma sunajin tsoronshi, kuma duk wanda aka kawo marar lafiya yana temaka mashi, hakan yasa mutanen garin dana wajen gari suke girmamashi.

Yadade yana yima masarautar Bubayero hidima tun lokacin mahaifansu Qaseem, dan masarautar bata yarda da malamin duba ko boka ba, hakan yasa koda iyayensu suka rasu basu yarda shiba, duk wani temako kowata shawara sukan zogurinshi, kuma Sarki baya aiko kowa gurinshi kode yazo tare dasu Qaseem da Waziri ko kuma ya aikosu su 2, yauma sunzo domin neman wani temako.

Bayan sungama gaisawa, Malam yasa ankawo masu kayan motsa baki, dan sunyi waya da Qaseem tun jiya yafada mashi suna hanya. Qaseem ne, yafara magana cike da ladabi. Allah gafarta malam, kamar yanda muka fara magana dakai jiya awaya. Dama bawani abu bane akan matsalar rashin haihuwar Yaya, tun tuni naso muzo shine yake hanawa, shine nace ai koma menene yanada magani, shine mukazo muji daga gareka.

Gyara zama malam yayi yacire glass din dayake idonshi yace, hakika nima nadade ina tausaya ma, memartaba, kuma dama tun kwanakin baya damukayi magana dakai, nafarayin istahara akan al'amarin. Kuma alhamdulillahi dama kobakuzo ba nayi niyar kiranka, infada maka abinda nagani.

Sede inaso kusani bakomai ne, ake fada ba dan kayi istahara, amma tabbas akwai abinda nagani amma nabarma kaina, kuma insha Allahu abinda ake so ahana za,a sameshi, sede muyita rokon Allah, babu abinda yagagareshi. Kamar kullum abinda nake fada maku kuyi hankali da mutanen da kuke tare dasu bance kuyi bincike ba, amma kada kayarda dakowa kuyarda da kanku, shine zaku zauna lafiya.

Abinda nakeso kusani insha Allahu memartaba yanada rabon samun haihuwa, sede abinda zan fada maku agsky ayanzude rabon dana gani zesamu ba'a agurin matanshi yake ba. Amma koma menene nasan zesamu haihuwa insha Allahu, sede adage da addu'a inafatan kunfahimci bayanina? Waziri yace munfahimceka malam, kuma mungode Allah yasaka da alkhairi, muzamuzo mukoma.

Malam yace tonima inada wata alfarma danakeso kuyi mani, Qaseem yace haba malam ai kawuce komai agurinmu kafadi koma menene. To kamar yanda kuka sani akwai kanwata kuma autarmu, kunsan mijinta yadade da rasuwa kuma taki yarda tayi wani auren, shine nakeso dan Allah kozaku tafi da ita can tarika temaka ma matan sarki dawasu aiyuka inaganin yafi zamandatakeyi anan tunda can akwai jama,a dayawa.

Sarki zeyi magana Qaseem yayi saurin fadin agaskya malam naji dadin wannan magana taka, kuma inaso abani ita inkaima Suhailat, dan mundade muna neman wadda zata zama mekusanci agurinmu, kasan ni bakowa nake yarda dashi ba, itama haka, amma tunda daga gareka tafito, kuma jininkace nayarda da ita sosai. Kuma dama tana da tsohon ciki inata tunanin wadda zata zauna mata. Mungode Allah yabamu zaman lafiya. Ya sunanta? Malam yace sunanta Safeeya.

Murmushi Waziri yayi yace mungode malam Allah yasaka da alkhairi. Sarki yace mungode malam, kuma insha Allahu zamu riketa amana. Malam yace nikeda godiya, bari inje infada mata tashirya.

Daki yakira Safeeya, sundade suna tattaunawa banji abinda suke fada ba, haka tafito tashirya tayima Matar malam sallama da sauran matan gidan, hada kukansu, haka suka shiga mota suka dauki hanya.

Gimbiya Suhailat taji dadin zuwan Safeeya, dan tanajin labarin malam agurin Qaseem, shiyasa tajata ajikinta sosai, dan har karatu take kara mata, hakan yasa suka saba dawuri, duk wata shawara Gimbiya Suhailat tanayi da Safeeya, haka kuma baruwanta dashiga part dinsu Gimbiya Zakiyyah, asalima basu san dazuwanta ba, kamar yanda babu wanda yasan tana da ciki harya tsufa, shiyasa taji dadin zuwan Safeeya. Dan Waziri yahana anuna Safeeya acikin gidan, har seda Sarki yace meyasa Waziri yace yallabai dan Allah abarta, Qaseem yace shikenan yanda kace Waziri.

Haka rayuwar gidan tacigaba da tafiya, Cikin Gimbiya Suhailat harya shiga watan haihuwarshi, Qaseem da Sarki suna farin ciki da cikin, dan kamar Sarki yafi Qaseem farin ciki da Cikin, kuma betaba fadama matanshi ba, dan gani yake kamar sun sani kuma beso suga kamar shima yadamu darashin haihuwar.

Jakadiya dasu Gimbiya sun hada kansu, Gimbiya Zakiyya babu abinda takeso kamar haihuwa, ayanzu bata da abokiyar shawara se Jakadiya, duk wani sirrinta Jakadiya tasani, sede haryanzu bata karbi gurguwar shawarar Jakadiya ba. Ita ko Gimbiya Nafeesa dama tasan bazata kara haihuwa ba, dan tunzubar da cikin datayi har so 3, likita yace mahaifarta tasamu matsala. Shiyasa bata da damuwa agidan, itade burinta kawai tasamu ta tara abin duniyarta, shiyasa takebin Gimbiya Zakiyya soda kafa, sede tabangare guda kuma sun hade kansu ita da Jakadiyya.

Zaune Jakadiya take afalon Gimbiyar Babbar Gida, kallonta tayi tace inajinki Jakadiya wace shawara kika kawo? Gyara zamanta tayi takara rage murya tace Gimbiya bawata shawara bace dama wata dabara nakawo, nace meze hana kicema Memartaba kina da ciki. Saurin tashi Gimbiya tayi tace bangane mekike nufi ba. Wace irin magana kikeyi haka, dama ana cikin karya ne? Murmushi Jakadiya tayi tace Allah yahuci zuciyarki, bahaka nake nufiba. Kinga yanzu ku 2ne matan Sarki, kuma kece Babba taya za,ayi muyarda wata tashigo daga baya ace ta haihu ke baki samu naki ba.

Jiya mukayi magana da Sarkin Fada kinsan mutumina ne, agurinshi nasamu labarin Sarki yace daya samu da namiji tofa lallai shine zegajeshi, shine nace meze hana kawai kice mashi kinada ciki, idan yaso sekirika saka tsummuna idan lokacin girman cikin yayi, kinga semuje gidan marayu mudauko yaro namiji kinga kema kinyi na..... marin da aka dauketa dashine yasata tayi shiru.

Dasauri tamaida kallonta gurin Gimbiya datake ta huci sbd tsananin bacin rai, cike da tsawa tace kitashi kibacemun daga nan. Kuma ina me tabbatar maki da duk ranar dana kara ganin kafarki acikin part dina wlh sekinbar masarautar nan.

Cike da bacin rai Jakadiya tafito, hanyar lambu tanufa inda suka saba haduwa da Sarkin Fada, wata baiwace tafito dagudu zata wuce, dasauri Jakadiya ta tareta dan tagane baiwar Gimbiya suhailat ce. Ke lafiya kike gudu haka? Wlh dama sauri nakeyi inje inyima Sarki Albishir Gimbiya tasauka lafiya tasamu da na miji. Kara goge kunnanta Jakadiya tayi tace bangane mekike fada ba. Dama Gimbiya ciki gareta? Kwarai ma kuwa, aiko Sarki yasan tana dashi. Wani mugun murmushi Jakadiya tayi, tace ki koma za'a isar mashi da sako.

Dasauri Jakadiya tanufi gurin Sarkin Fada, sundade suna magana daga baya tafito tana dariya tanufi bangaren Sarki. Bakaramin dadin Sarki yaji ba, nan take yayima Jakadiya kyauta metsoka, Qaseem ma seda yabata kyauta, dan yana gurin aka fadi haihuwar.

Kafin wani lokaci gidan Sarki ya sheda haihuwar Gimbiya Suhailat, Qaseem boye farin cikinshi yarikayi, dan bayason Yayanshi yashiga damuwa. Bakaramin tashin hankali Gimbiya Zakiyya tashiga ba lokacin da labari yazo mata. Har kuka seda tayi, gashi takori Jakadiya, haka tasa aka kira Gimbiya Nafeesa ita tarika bata hkr, dan ita ko akanta.

Duk wata hidima Safeeya ce take mata, yaronta me kyau sosai, tun yana jariri dayayi kuka se dimple dinshi ya fito. Bayan kwana 7 akayi suna, Sarki da kanshi yasama yaron suna, dan Qaseem yaso yasaka sunan Yayanshi amma Sarki yace yabari zesa mashi suna, shikuwa yayi haka ne, dan yabama matar kaninshi hakkinta ko akwai sunan datakeson tasama yaron. Lokacin dayasa Safeeya ta tambayeta sunan datakeso asama yaron tace tanason asamashi Areef, dan sunan kaninta ne, daya rasu. Sarki yaji dadin tambayr dayasa akayi mata, koba komai yasan ba,a shiga hakkinta ba.

Qaseem yayi mamakin sunan da Sarki yasama yaron, koda yabincika yagane shine yasa atambayi matarshi, bakaramin jin tausayin Yayanshi yayi ba, kuma yakara jinjina adalci irin nashi.

Bakaramin taro akayi ba, hatta da yan uwanta seda sukazo suna, su gimbiya Zakiyya sunga yanda ake mulki da kuma dukiya, haka suka saki jiki kamar bakomai akayi suna lafiya, se alokacin suka san da zaman Safeeya, dan sunga komenene Gimbiya zata sa sede takirata, gashi kuma ita batada uniform bare suce baiwace, alokacin sunan ne Gimbiya Zakiyya tashirya da Jakadiya, dan tasan koba komai tana mata amfani sosai.

Haka rayuwa tacigaba da tafiya, duk yanda suka so susamu wata hanya dazasu kunta tama Gimbiya suhailat babu dama. Jakadiya da sarkin Fada kuwa kansu ahade yake, dan sarkin fada seda yasan yanda yayi yarika shiga bangaren Qaseem, yanuna yana matukar son Areef hakan yasa yashiga jikin Qaseem sosai, duk lokacin da aka kawo Areef Fada, Sarkin Fada shine yake karbarshi yayita renonshi harseyayi kuka sannan amaidashi.

Bayan shekara 1 Areef yakara wayau sosai, kullum afada yake wuni tare dasu Sarki, kowa yasan irin son da Sarkin fada yakema Areef, hakan yasa itama Gimbiya suhailat take mashi kyauta akai akai.
Chapter 7 · 0% Book details