← Book details A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 33

Sashe 25

A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan Jakadiya Karima tazo tasameni akan Gimbiya Zakiyyah tana nemana, bayan naje ita da Medaki suna zaune tafadamun abinda takeso inyi, sunaso insan yanda zanyi inhallaka Fulani da abinda ke cikinta. Aranar da dare itace agurin Sarki, hakan yabamu damar shiga dakin Fulani mu biyu, nina fesa mata abinda yake sa mutum bacci, sede ban fesa mata ba sebayan muntasheta, alokacin taganni seta fara kokarin yimana ihu, hartaji mani ciwo afuska, ganin za,a jimu ne yasani fesa mata maganin, nan take tayi bacci.

Kamata mukayi muka fita da ita, muka sata mota, dama munhada baki da masu gadin gate su 2, wato Lado da Mati, hakan yasa suka bude mana kofa muka fita. Munyi tafiya menisa dan seda mukaje wani daji dayake bayan garin Darazo kusa da wata Mabarta, anan muka wurgata cikin wani rami.

Sede wanda muka aikata laifin dashi banganshi anan ba, amma inaso ashigomun da amintaccen bawan Sarki Hasheem me kula da komai nashi nacikin gida, shine wanda yatemaka mun mukayi wannan abun.

Sarki Hasheem runtse idonshi kawai yayi yana karanto addu,a dan zuciyarshi zafi takeyi, jiyake kamar zata fito. Ganin haka Malam yasa aka miko mashi ruwa yayi addu,a aciki yabama Sarki Qaseem wanda shima kukan yakeyi, yace yabashi.

Dakin yayi shiru sautin kukan mutane kawai akeji, jisukeyi kamar almara ce ake fada masu. Bayan anshigo da bawan, anan yaxube yana kuka, yace dan Allah kumun rai wlh Son Zuciya ne da kwadayin abun duniya suka kaini da aikata wannan abu. Waziri yace haka kowa yake fada Son Zuciya, Ai kowa yasan son Zuciya bacinta.

Sarkin fada yafiddo wata karamar waya daga aljihunshi yamika ma Waziri yace wannan shine shedar dazata nuna maku akwai sa hannun Zakiyyah acikin duk wani munafunci da akayi, bazan kirata Gimbiya ba sbd tazama tamkar mata agurina. Saurin dafe kai Sarki Hasheem yayi dajin abinda Sarkin fada yafada.

Wata waya waxiri yaciro yajona ajikin wayar yahada da T. V ya kunna kowa yamaida hankalinshi akan t,v. Tun daga lokacin dasuke zaune afalon Gimbiya Zakiyyah tana fada masu yanda za,a kawar da Fulani, da duk wani munafunci dasukayi, harzuwa lokacin daya fara neman Medaki, tunda Sarki yaga sunfara aikata masha,a yarufe idonshi, aranshi yana fadin wato dama karya medaki tamashi babu wani fyaden da akayi mata, dama can yar iska ce. Areef kuwa yahana beauty ma ta kalli abinda akeyi, ya kwantar da ita akan cinyarshi yana shafa mata kai, daga haka tayi bacci.

Babban abinda ya dagama kowa hankali lokacin da aka nuno sanda suka fara aikata masha,a da Gimbiyyah Zakiyyah. Salati kowa yafarayi, hakan yasa Sarki yabude idonshi, sede yayi dana sanin ganin abinda matarshi da bafadenshi suke aikatawa. Waziri yasa hannu yakashe wayar.

Shiru kowa yayi se kukan Gimbiya Zakiyyah dana medaki kawai akeji. Jakadiya Karima ta tashi tace wlh shima akwai abinda befada maku ba, idan bazaku manta ba, alokacin da za,a nada Sarkin fada bashi bane aka zaba ko? Waziri yadaga kai. Nan Jakadiya tashiga basu labarin da Sarkin fada yabata.

Mamaki yakama kowa jin irin abinda sarkin fada ya aikata. Hayanice tacika falon. Bayan kowa yanutsu, Waziri yace lallai babu abinda zamuce sede muyi godiya ga Allah wanda shine yake tsaremu aduk inda muke.

Tabbas akace dazama da makiyi gara zama da barawo, kuma dama ance makusan cinka shine makashinka. Tabbas kunso kashe abinda Allah yaso yafito duniya, sede babu wanda ya isa ya aikata wani abu seda izinin Allah. Matar da kukaso kashewa da diyarta gasunan araye. Kallon Areef yayi yace daga matar taka kowa yaganta.

Murmushi yayi dan seyanzu yafara fita daga duhun dayake ciki, tashin beauty zeyi Malam yace abarta, zata tashi da kanta. Kowa mamakin ganin beauty yakeyi wai itace diyar Fulani, Sarki kam wani irin sanyi yaji yana ratsashi duk da damuwar datake ranshi.

Waziri yace akwai bayanin da Malam zeyi mana kafin afadi irin hukuncin daza,ayi ma kowa. Amma zamuje hutu daga nan zuwa bayan azahar dan sallah tagabato, wasu fadawa yasa suka tasa keyar su Gimbiya Zakiyyah, Medaki dasu Jakadiya yace atsaresu. Kuma yasa suhada da mati da Lado.

Kuka kawai sukeyi. Sarkin fada kuwa murmushi kawai yakeyi.
Matsawa yayi kusa da Gimbiya Zakiyyah yace kinsan akullum tunanin yan sarauta akullum iya karshi harshe, dan basa amfani da tunaninsu sede na bayinsu. Kinga koyanzu ya isa kigane banbanci tsakanin Bawa da me mulki. Kuka tasaka, aka turasu zuwa kurkutu.

Nima yakamata inhuta haka kafin sudawo.

Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady).
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]

Season 105⚜110

Zaune suke gaba daya harda masu laifi, zuwa wannan lokacin idanunsu haryagaji da zubar hawaye. Sarki Hasheem ya kalli Gimbiya Zakiyya, duk tafita hayyacinta, har seda tabashi tausayi dan yasan halin mahaifiyarta idan hartaji abinda tayi tabbas zata saba mata.

Kawar da kanshi yayi ya kalli beauty wadda take haryanzu ajikin Areef, tunda Fulani ta tureta haryanzu taki kara kallonta kuma koda aka dawo sallah agurin Areef ta tsaya, shikam dama haka yakeso, yariketa kamar ance za,a kwaceta. Dan bemanta da halin data shiga ba lokacin da Momynshi tayi mashi fada.

Malam yayi gyaran murya yace Alhamdulillahi Allah yakawomu abinda na dade ina fatar Allah yakawomana karshen shi, tabbas masarautar nan tashiga tashin hankali da rudani, wanda zance bacewar Fulani agidan nan tamkar saukowar wani haske ne wanda yazo ya haske duk wani duhu dayake gidan nan. Kuma ya haska duk wasu munafukai dasuke tare da mutanen gidan.

Abin mamaki wai ace wanda kayarda dashi yanzu aduniya shine yake cutarka. Gaskiya nayi matukar girgiza dajin wadanda suka aikata wannan ta,asa wai makusantan Sarki ne, acikinsu kaf babu wani bare.

Dama haka duniya take, duk wanda zakayima hassada tamkar kana kara kusan tashi da ubangiji ne, domin tunda annabi yasamu makiya to babu wani dan adam din daze iya kubuta daga sharrinsu.

Sede abinda nakeso inkara tunatar daku, shine addu,a domin itace makamin mumini, duk da ake cewa bawa baya iya kaucema kaddararshi, amma idan muka rike addu,a babu abinda bazata yimana ba.

Addu,a takan canza sharri yazama khairi, kuma tanasa tsanani yazama sauki, dan haka koda Allah ya kaddaro maka wata kaddara marar kyau, idan har karike addu,a abun ze iya zo maka dasauki. Arayuwa baka taba gane makiyinka, harse ranar da asirinshi yatonu.

Agskiya Sarkin Fada kabamu mamaki sosai, da irin abubuwan damukaji ka aikata, ba kowane me imani bane ze iya aikata abinda ka aikata. Kaci amanar kanka, addininka, iyayenka, matarka, da kuma Ubangidanka.

Duk irin halaccin dayayi maka arayuwa, seda ka ha'inceshi, kashiga gonarshi har 2, duk da haka bata isheka ba seda kayi sanadiyar rugujewar farin cikinshi, tahanyar kauda abinda yake matukar so, kaso ka halakar dasu amma Allah be baka iko ba.

Ko kasan ta dalilinka irin ukubar da Fulani da diyarta suka shiga? Mezaka cema Allah aranar gobe kiyama idan yatambayeka akan amana? Ko kasan kalar abincin dasukaci atsawon shekaru 18 acikin MAKABARTA?

Ta dalilinka matar da babu ruwanta, bata yima kowa komai ba, amma saboda SON ZUCIYA irin taku kaida mabiyanka kunsa baiwar Allah tahaihu a MAKABARTA. Yarinya ta tashi a MAKABARTA. Bata san kowa ba se Mamanta da kaburbura, da bishiyoyi.

Wancen bawan Allah da kuke ganinshi agidan nan badan kowa yake zaune ba sedan farin cikin yarinyar da kukaso ku hanata zuwa duniya. Shine mutum na 2 daya temakeso, wanda badanshi ba haka Yarinya zata girma har shekaru 18 amma batasan komai ba, kuma ita ba hauka ba, barashin lafiya ba.

Kawai saboda tsabar SON ZUCIYA irin taku, bara infada maku abinda bakusani ba, kuma zakusan cewar duk zakaran da Allah yanufa da tsara to ko ana muzuru ana shaho se yayi.

Idan bakusani ba aranar da kuka wurgar da Fulani acikin dare kuka wurgata cikin rami, to aranar ta haihu, kunsan suwa Allah yaturo mata kawai dan yanason yanuna maku baya bacci? Wasu bayinsa ne, kuma yan uwa musulmai, wadan da suka fito daga jinsin aljanu.

Akusa da fadarsu kuka wurgata, kuma cikin ikon Allah alokacin suka temaka mata harta haifi diyarta acikin koshin lafiya. Zakusha mamaki idan nabaku labarin da daya daga cikin aljanun, wanda yakasance shugaba agurinsu, shine yabani labarin abinda yafaru. Bara kuji....

Kaf duk abinda Malam yasani seda yafada masu, gaba daya falon babu wanda beyi kuka ba saboda tausayin Fulani da beauty, kowa ya tausaya masu yanda sukayi rayuwarsu acikin MAKABARTA. Fulani da Beauty sunfi kowa kuka, dan ita beauty tade taso taganta a MAKABARTA.

Atunaninta nanne muhallinsu, kuma Fulani ita kadaice wadda tasani, mace, se kuma Baba wanda shima shikadai tasani namiji. Kuka takeyi sosai ayau dataji labarinta, ashe inda take tunanin muhallinsu ne, take cewa acan aka haifeta, ashe muhallin matattune, segashi yanzu ana fadin AMAKABARTA AKA HAIFETA.

Malam yace ga Baba nan, shine megadin MAKABARTAR da suke zaune, kuma shine mutumin daya zauna dasu bisa gaskiya da amana, kuma ko matarshi betaba fada mawa ba, harseda yaga lokaci yayi daya kamata yafada mawani, alokacinne yazo yasameni yafadamun.........

Duk abinda Baba yafada mashi seda yafada masu, da irin dawainiyar da yayi dasu. Hakanne yasa alokacin da yagama bani labari, mukaje muka daukosu duk da seda wannan aljanu suka rokemu akan mukula dasu idan har wani yakara yunkurin cutar dasu bazasu kyaleshi ba.

Tundaga ranar damuka daukosu, nafara tunanin tabbas abinda nagani acikin istaharata yana shige da wadannan bayin Allah, idan baku manta ba Waziri, azuwan da kukayi nafada maku naga Fulani akusa dani, kuma tana raye, sede bansan awane waje take ba.

Hakan yasa nafara zargin wannan mata da diyarta zasu iya kasancewa matar Sarki da diyarshi. Amma gudun kada inyi saurin fadar abinda zuciyata take fada mun hakan yasa lokacin da Safeeya tazo mani da alfarmar abata wannan yarinya ta taho da ita nan gidan yasa nayi tunanin barinsu suzo, sena cemata dole sutaho su duka.
Chapter 25 · 0% Book details