Sashe 29
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Malam yace to Alhamdulillahi, muna godiya ga Allah daya nuna mana wannan rana, inafatan wannan abu da yafaru agidan nan ze zame ma kowa darasi, abinda yarage mana shine mucigaba da neman tsari daga sharrin masu sharri, kuma kowa yadage da addu,a, kada kuyi la'akari dacewar wani yana maku addu'a.
Idan har zaka iya saka wani yamaka addu'a to kai meyasa bazaka iya rage wani abu daga cikin darenka katashi karoki mahaliccinka ba? Allah da kanshi yake fada akwai wani lokaci acikin dare wanda yake sakkowa daga sama yazo ya karbi addu'ar bayin da sukayi awannan lokacin. Da aka tambayi manzon Allah wane lokacine wannan? Yace daga karfe hudu zuwa asuba.
Duk wanda yatashi awannan lokacin yayi sallah tabbas Allah ze karbi addua'arsa. Ina me maku nasiha da ku daure kurage jindadin duniya kusami lokacin ganawa da ubangijinku acikin dare, ibadar rana kadai bazata isheka ba, saboda duk yanda kaso kebewa da rana kace zakayi ibada ta tsawon minti 30 kadai, dole se wani abu yashigo maka katashi.
Amma idan akace maka da dare ne, kana da lokaci me yawa. Kuduba manzon Allah, shifa yariga dayasan anyi mashi albishir da aljanna, amma duk da haka yakan tashi cikin dare yayi ta ibada. To kai waye dabazakayi koyi dashi ba? Wanda aduk cikinmu babu wanda yakeda tabbacin shiga aljanna. Dan manzon Allah yace akwai wadan da zasu dade suna aikata aikin alkhairi, amma karshen wuta ce makomarsu. Kamar yanda wasu zasu dade suna aikata zunubi amma aljannace mako marsu.
Dan haka aduk lokacin da kukaga wasu suna aikata alfasha, kada kabata lokacinka gurin aibantasu, kai zaka cinye ladar daka tarama kanka, amai makon haka kayi masu wa'azi idan har kaga zasu dauka, idan kuma abin yafi karfinka to kabisu da addu'a.
Manzon Allah yace aduk lokacin da wani bawa ze rokama wani dan uwanshi abu agurin Allah, batare da sanin wancan ba. Mala'iku zasuyi rika yimashi addu'ar duk abinda yarokama wancan shima.
Daga karshe, ina kara maku nasiha dakuji tsoron Allah, kuma kucire son zuciya a zukatanku, Allah ze temakeku aduk inda kuke, kuma kuzauna da kowa da zuciya daya, idan shi bahaka yake zaune daku ba, wata rana Allah zetonashi kowa yaganshi, kamar yanda yayi ma wadan da suka wuce. Ina fatan kowa zerike duk abinda nafada maku.
Gyaran murya Sarki Qaseem yayi yace, hakika munji dadin irin fadakarwar da malam kayi mana, akwai abubuwa da dama daka tunatar damu, wadanda munshagala dasu abaya, hakika mutum yatashi yaroki Allah da kanshi shine abinda yafi, domin idan kadogara da wani, wata rana Allah yana uya daukeshi, shiyasa akace daka bama mutum kudi yasayi abinci. Gara ka bashi gona yayi noma, haka kuma daka bashi kudi gara ka sakashi makaranta.
Wata rana seya temaki kanshi da al'umma. Mungode kwarai da kulawarka agaremu, Allah yabar zumunci, kuma insha Allahu zamu kawo gyara sosai amasarautar nan, ta yanda zamu temaki sauran bayin dasuke cikin masarautar nan, suma susami ilimin addini kada rayuwarsu takare abauta.
Malam yace idan kukayi haka tabbas zaku kawo cigaba a masarautarku, kuma yin hakan zesa wannan masarauta ta daukaka, harma wasu masarautun suyi koyi daku. Ni kuma nayi alkawarin turo manyan yarana suzo suma subada tasu gudunmuwar, kaga ahakane, suma bayi zasu gane cewa suma mutanene, kamar kowa. Ina rokon Allah ya amshi wannan niya taku, kuma yasama abun albarka. Ina ganin ayau zanzo in koma.
Waziri yace mungode sosai Malam, Allah yasaka da alkahairi, kuma ina ganin kafin kawuce, zamu zabeka amatsayin wanda ze daura mana sabon Sarkin Fada.
Malam yayi murmushi yace, to inaganin yakamata abama wanda yakamata abama sarautar tun farko, kafin aci amanarshi. Koba komai, zeji dadin hakan, kuma sauran mutane zasu kara yarda dacewa duk zakaran da Allah yanufa da cara, to ko ana muzuru ana shaho seyayi, yasha wahala ta dalilin sarauta, ya kwashe shekaru dayawa acikin kurkutu. Tabbas babu wanda ya dace da wannan sarauta se shi.
Kallon Sarki Hasheem yayi yace, inaso inji wane suna kasama diyar tawa, kafin inkoma? Murmushi yayi yakara kallon Fulani sannan yace agaskiya tunkafin a haifeta dama nazaba mata suna, badan komai nazaba mata sunan ba, sedan inyi godiya ga Allah abisa kyautar da yayi mani nasamun karuwa.
AMATULLAHI, shine sunan dana zaba mata. Lumshe ido Areef yayi jin yanda sunan ya burgeshi. Malam yace Alhamdulillahi wannan suna yayi dadi, AMINTATTAR ALLAH kenan, to Allah yasa albarka acikin sunanki da rayuwarki gaba daya. Kowa yace amin.
Waziri yace Malam inaganin zaka kara dawowa nan kusa domin kadaura mana aure amasarautar nan, Murmushi yayi yace lallai kam nima naga alama, dan tunkafin inzo nasan da wannan labari, zuwana kuma yakara tabbatar mani da hakan, dan Yarima yafi kowa kaffa kaffa da diyar tawa, yanda kasan ance za'a kwace mashi ita. Dariya suka saka gaba daya. Anan Baban Fulani shima yayima Malam godiya sannan yakara yima Baba na Darazo godiya.
Sarki Qaseem yace ai basu kadai ba, gawasu masoyan nan agefe, dan haka tare za,a yi muhuta gaba daya. Kowa dariya yayi. Malam yace to Allah ya nuna mana, amma banaso asaka danisa, gara tazauna da mijinta, hakan ze sa tasamu kwanciyar hankali. Anan aka rufe taro da addu'a.
Kwana 3 aka dauka a masarauatar ana zaman jimami, jikin Sarki Hasheem yayi sauki, sede haryanzu yana cikin damuwa, kuma befara takawa da kanshi ba, dole seda sanda, hakan yasa Sarki Qaseem da Waziri suka nemi shawarar likita, shine yace idan ze yarda afitar dashi waje.
Zasuyi mashi wani gashi, insha Allah ze dawo dede. Bayan sun sameshi da maganar babu musu ya amince, hakan yasa Waziri yace dashi za,a tafi. Sarki Hasheem yace amma da Fulani zamu tafi ko? Murmushi sukayi sukace ai badamuwa.
Lokacin da Sarki Qaseem yasamu Gimbiya Suhailat da maganar cewa tayi suyi hakuri abarta akwai abinda zatayi mata kafin sudawo angma. Yace a,a kinsan Yaya baze yarda ba, kawai kibashi matar shi. Da to kawai ta amsa mashi.
Amma azuciyarta tayi alkawarin bazata bari sutafi tare ba, dan Fulani tana bukatar gyara sosai, shekaru 18 acikin hauka, kuma har haihuwa tayi. Dole ma tayi duk yanda zatayi tahana atafi da ita.
Zaune suke afalo ana tashirin tafiyarsu, dan anjima kadan zasu tafi,Fulani datake zaune agefen Sarki, tayi saurin rike cikinta. Dasauri Gimbiya Suhailat tace lafiya de Fulani?
Nana hankalin kowa yadawo kanta, Sarki Hasheem yace adauketa muje asibiti mana. Gimbiya tace a,a inajin baciwon asibiti bane,birin ciwonmu ne, na mata bari muje cikin gida. Sarki Hasheem yace ina ganin za,a daga tafiyar nan kafin tasamu lafiya.
Waziri yace a'a Memartaba, kada wannan yadameka, tafiyarmu bazata wuce kwana 10 ba, inaganin kayi hakuri tunda har angama komai kuma agobe za,a fara gashin nan, kaga likitan yace akwai inda zeje, saboda kaine yadaga tafiyar.
Kayi hakuri muje domin neman lafiyarka, nasan ayanzu kanajin babu dadi kowa yana hidimarshi amma kana zaune, guri guda, idan zajayi tafi seda sanda. Sarki Qaseem ya matso kusa dashi yace dan Allah Yaya kada kaki yarda ayi tafiyar nan, wlh Allah kadai yasan halin damuke ciki akan rashin lafiyarka. Shiru yayi, hawaye suna zuba daga idonshi.
Hannunshi Sarki Hasheem yakama shima idanunshi sunyi ja, yace karka damu dan uwa na, acigaba da shiri,Allah yasa ayi asa'a. Murmushin jindadi yayi yarungume Yayanshi yace nagode Yaya. Sarki Hasheem yakalli Beauty yace zo Amatullah mu gaisa mana.
Murmushi tayi ta tashi tanufi gurinshi tana zuwa tazauna kusa dashi ta dora kanta saman kafarshi. Hannu yasa yashafi fuskarta tace yauwa Amatullahi, Allah yabaki lafiya kema kirika magana kamar kowa. Areef yace Amma Baffa tayi magana so daya a asibiti.
Waziri yace insha Allahu wata rana zata yi magana, dan likita yace matsalarta ne sauki ce, kuma base an kaita asibiti ba, zata iya yin magana akowane,lokaci, yace idan har taga wani abu daya tsora tata bakinta ze iya budewa. Sarki Hasheem yace insha Allahu zata samu lafiya. Kuma da mun dawo za,ayi maganar bikunku, Yarima seka fadama abokinka dan ahada tare, ko Ayman? Murmushi tayi ta tashi tafita.
Lokaci yana cika suka fito domin tafiya, seda aka kai Sarki Hasheem gurin Fulani sukayi Sallama, sannan suka nufi air pot. Suna zuwa aka fara kiran sunaye, haka suka rungume juna shida Kaninshi, har kua seda sukayi. Yana kallonsu har jirginsu yadaga sannan suka dawo.
Dariya Gimbiya Suhailat da jakadiya Safeeya sukayi, Gimbiya tace ai nadauka Fulani bazakiyi yanda nace maki, ba, dan kina tausayin mijinki. Fulani tayi murmushi tace, duk yanda nake tausayinshi ai gara inzauna indawo da martabata ni kaina wani lokacin kyan kyamin kaina nakeji, kiduba fa kigani duk wata kazanta damuke fitarwa haka zanyita ingama babu wani wanka. Kai gaskiya mutanen nan sun cutar dani.
Jakadiya Safeeya tace wai ahaka ma kinsamu bakar da ba, kuma kinga acikin kwana goma zaki samu gyara sosai, wanda Sarki zeyi farin ciki da haka. Gimbiya tace ai wannan gyaran na musamman zakisha, suma Yarana nasu nadabanne.
Kallon Jakadiya Safeeya tayi tace akwai wani abu danake so inhada, amma anjima idan hubby yadawo zamuyi maganar, kema yakamata, ai ko? Jakadiya tace bangane ba? Murmushi Gimbiya tayi tace a'a bakomai dama gani nayi Waziri tunda matarshi ta mutu be kara aure ba, kuma dama diyarshi daya sunyi mata aure. Shine naga kema mijinki yarasu ai.
Dariya Fulani tayi tace kai amma wlh Aunty kin iya hangen nesa. Tashi Jakadiya tayi tana murmushi, Gimbiya tace, ina kuma zakije? Fita tayi bata cemata komai ba. Gimbiya tace Allah da gaske nakeyi, kuma insha Allahu wannan abu seya tabbata, zansa Hubby yafadama Malam, kinga se ayi tare dana su Amatu. Fulani tace Allah yasa.
Zaune suke acikin lambu, beauty Amatullah tana zaune agefen Areef yana koyamata karatu, su Haisam suma suna gefe guda suna firarsu. Areef ya kalli Haisam yace wai abokina ya kukayi da Dady akan maganar Ayman?.
Murmushi yayi yace yafi kowa mafarin ciki shida Momy dasukaji maganar, yace idan Baffa yadawo zasuzo. Areef yace ai gara azo a aurar damu kowama yahuta ko Beauty na? Kai tadaga mashi tana murmshi. Haisam yace Beauty bahaka zakice ba, a,a zakice.
Hararshi Areef yayi yace todan bukulu ai seka hanata, kuma wlh wannan sunan yafita abakinka, tunda de ansamata suna kawai ka kirata da Amatullahin ta. Haisam yace bazan kiraba, ni nariga dana saba.
Idan har zaka iya saka wani yamaka addu'a to kai meyasa bazaka iya rage wani abu daga cikin darenka katashi karoki mahaliccinka ba? Allah da kanshi yake fada akwai wani lokaci acikin dare wanda yake sakkowa daga sama yazo ya karbi addu'ar bayin da sukayi awannan lokacin. Da aka tambayi manzon Allah wane lokacine wannan? Yace daga karfe hudu zuwa asuba.
Duk wanda yatashi awannan lokacin yayi sallah tabbas Allah ze karbi addua'arsa. Ina me maku nasiha da ku daure kurage jindadin duniya kusami lokacin ganawa da ubangijinku acikin dare, ibadar rana kadai bazata isheka ba, saboda duk yanda kaso kebewa da rana kace zakayi ibada ta tsawon minti 30 kadai, dole se wani abu yashigo maka katashi.
Amma idan akace maka da dare ne, kana da lokaci me yawa. Kuduba manzon Allah, shifa yariga dayasan anyi mashi albishir da aljanna, amma duk da haka yakan tashi cikin dare yayi ta ibada. To kai waye dabazakayi koyi dashi ba? Wanda aduk cikinmu babu wanda yakeda tabbacin shiga aljanna. Dan manzon Allah yace akwai wadan da zasu dade suna aikata aikin alkhairi, amma karshen wuta ce makomarsu. Kamar yanda wasu zasu dade suna aikata zunubi amma aljannace mako marsu.
Dan haka aduk lokacin da kukaga wasu suna aikata alfasha, kada kabata lokacinka gurin aibantasu, kai zaka cinye ladar daka tarama kanka, amai makon haka kayi masu wa'azi idan har kaga zasu dauka, idan kuma abin yafi karfinka to kabisu da addu'a.
Manzon Allah yace aduk lokacin da wani bawa ze rokama wani dan uwanshi abu agurin Allah, batare da sanin wancan ba. Mala'iku zasuyi rika yimashi addu'ar duk abinda yarokama wancan shima.
Daga karshe, ina kara maku nasiha dakuji tsoron Allah, kuma kucire son zuciya a zukatanku, Allah ze temakeku aduk inda kuke, kuma kuzauna da kowa da zuciya daya, idan shi bahaka yake zaune daku ba, wata rana Allah zetonashi kowa yaganshi, kamar yanda yayi ma wadan da suka wuce. Ina fatan kowa zerike duk abinda nafada maku.
Gyaran murya Sarki Qaseem yayi yace, hakika munji dadin irin fadakarwar da malam kayi mana, akwai abubuwa da dama daka tunatar damu, wadanda munshagala dasu abaya, hakika mutum yatashi yaroki Allah da kanshi shine abinda yafi, domin idan kadogara da wani, wata rana Allah yana uya daukeshi, shiyasa akace daka bama mutum kudi yasayi abinci. Gara ka bashi gona yayi noma, haka kuma daka bashi kudi gara ka sakashi makaranta.
Wata rana seya temaki kanshi da al'umma. Mungode kwarai da kulawarka agaremu, Allah yabar zumunci, kuma insha Allahu zamu kawo gyara sosai amasarautar nan, ta yanda zamu temaki sauran bayin dasuke cikin masarautar nan, suma susami ilimin addini kada rayuwarsu takare abauta.
Malam yace idan kukayi haka tabbas zaku kawo cigaba a masarautarku, kuma yin hakan zesa wannan masarauta ta daukaka, harma wasu masarautun suyi koyi daku. Ni kuma nayi alkawarin turo manyan yarana suzo suma subada tasu gudunmuwar, kaga ahakane, suma bayi zasu gane cewa suma mutanene, kamar kowa. Ina rokon Allah ya amshi wannan niya taku, kuma yasama abun albarka. Ina ganin ayau zanzo in koma.
Waziri yace mungode sosai Malam, Allah yasaka da alkahairi, kuma ina ganin kafin kawuce, zamu zabeka amatsayin wanda ze daura mana sabon Sarkin Fada.
Malam yayi murmushi yace, to inaganin yakamata abama wanda yakamata abama sarautar tun farko, kafin aci amanarshi. Koba komai, zeji dadin hakan, kuma sauran mutane zasu kara yarda dacewa duk zakaran da Allah yanufa da cara, to ko ana muzuru ana shaho seyayi, yasha wahala ta dalilin sarauta, ya kwashe shekaru dayawa acikin kurkutu. Tabbas babu wanda ya dace da wannan sarauta se shi.
Kallon Sarki Hasheem yayi yace, inaso inji wane suna kasama diyar tawa, kafin inkoma? Murmushi yayi yakara kallon Fulani sannan yace agaskiya tunkafin a haifeta dama nazaba mata suna, badan komai nazaba mata sunan ba, sedan inyi godiya ga Allah abisa kyautar da yayi mani nasamun karuwa.
AMATULLAHI, shine sunan dana zaba mata. Lumshe ido Areef yayi jin yanda sunan ya burgeshi. Malam yace Alhamdulillahi wannan suna yayi dadi, AMINTATTAR ALLAH kenan, to Allah yasa albarka acikin sunanki da rayuwarki gaba daya. Kowa yace amin.
Waziri yace Malam inaganin zaka kara dawowa nan kusa domin kadaura mana aure amasarautar nan, Murmushi yayi yace lallai kam nima naga alama, dan tunkafin inzo nasan da wannan labari, zuwana kuma yakara tabbatar mani da hakan, dan Yarima yafi kowa kaffa kaffa da diyar tawa, yanda kasan ance za'a kwace mashi ita. Dariya suka saka gaba daya. Anan Baban Fulani shima yayima Malam godiya sannan yakara yima Baba na Darazo godiya.
Sarki Qaseem yace ai basu kadai ba, gawasu masoyan nan agefe, dan haka tare za,a yi muhuta gaba daya. Kowa dariya yayi. Malam yace to Allah ya nuna mana, amma banaso asaka danisa, gara tazauna da mijinta, hakan ze sa tasamu kwanciyar hankali. Anan aka rufe taro da addu'a.
Kwana 3 aka dauka a masarauatar ana zaman jimami, jikin Sarki Hasheem yayi sauki, sede haryanzu yana cikin damuwa, kuma befara takawa da kanshi ba, dole seda sanda, hakan yasa Sarki Qaseem da Waziri suka nemi shawarar likita, shine yace idan ze yarda afitar dashi waje.
Zasuyi mashi wani gashi, insha Allah ze dawo dede. Bayan sun sameshi da maganar babu musu ya amince, hakan yasa Waziri yace dashi za,a tafi. Sarki Hasheem yace amma da Fulani zamu tafi ko? Murmushi sukayi sukace ai badamuwa.
Lokacin da Sarki Qaseem yasamu Gimbiya Suhailat da maganar cewa tayi suyi hakuri abarta akwai abinda zatayi mata kafin sudawo angma. Yace a,a kinsan Yaya baze yarda ba, kawai kibashi matar shi. Da to kawai ta amsa mashi.
Amma azuciyarta tayi alkawarin bazata bari sutafi tare ba, dan Fulani tana bukatar gyara sosai, shekaru 18 acikin hauka, kuma har haihuwa tayi. Dole ma tayi duk yanda zatayi tahana atafi da ita.
Zaune suke afalo ana tashirin tafiyarsu, dan anjima kadan zasu tafi,Fulani datake zaune agefen Sarki, tayi saurin rike cikinta. Dasauri Gimbiya Suhailat tace lafiya de Fulani?
Nana hankalin kowa yadawo kanta, Sarki Hasheem yace adauketa muje asibiti mana. Gimbiya tace a,a inajin baciwon asibiti bane,birin ciwonmu ne, na mata bari muje cikin gida. Sarki Hasheem yace ina ganin za,a daga tafiyar nan kafin tasamu lafiya.
Waziri yace a'a Memartaba, kada wannan yadameka, tafiyarmu bazata wuce kwana 10 ba, inaganin kayi hakuri tunda har angama komai kuma agobe za,a fara gashin nan, kaga likitan yace akwai inda zeje, saboda kaine yadaga tafiyar.
Kayi hakuri muje domin neman lafiyarka, nasan ayanzu kanajin babu dadi kowa yana hidimarshi amma kana zaune, guri guda, idan zajayi tafi seda sanda. Sarki Qaseem ya matso kusa dashi yace dan Allah Yaya kada kaki yarda ayi tafiyar nan, wlh Allah kadai yasan halin damuke ciki akan rashin lafiyarka. Shiru yayi, hawaye suna zuba daga idonshi.
Hannunshi Sarki Hasheem yakama shima idanunshi sunyi ja, yace karka damu dan uwa na, acigaba da shiri,Allah yasa ayi asa'a. Murmushin jindadi yayi yarungume Yayanshi yace nagode Yaya. Sarki Hasheem yakalli Beauty yace zo Amatullah mu gaisa mana.
Murmushi tayi ta tashi tanufi gurinshi tana zuwa tazauna kusa dashi ta dora kanta saman kafarshi. Hannu yasa yashafi fuskarta tace yauwa Amatullahi, Allah yabaki lafiya kema kirika magana kamar kowa. Areef yace Amma Baffa tayi magana so daya a asibiti.
Waziri yace insha Allahu wata rana zata yi magana, dan likita yace matsalarta ne sauki ce, kuma base an kaita asibiti ba, zata iya yin magana akowane,lokaci, yace idan har taga wani abu daya tsora tata bakinta ze iya budewa. Sarki Hasheem yace insha Allahu zata samu lafiya. Kuma da mun dawo za,ayi maganar bikunku, Yarima seka fadama abokinka dan ahada tare, ko Ayman? Murmushi tayi ta tashi tafita.
Lokaci yana cika suka fito domin tafiya, seda aka kai Sarki Hasheem gurin Fulani sukayi Sallama, sannan suka nufi air pot. Suna zuwa aka fara kiran sunaye, haka suka rungume juna shida Kaninshi, har kua seda sukayi. Yana kallonsu har jirginsu yadaga sannan suka dawo.
Dariya Gimbiya Suhailat da jakadiya Safeeya sukayi, Gimbiya tace ai nadauka Fulani bazakiyi yanda nace maki, ba, dan kina tausayin mijinki. Fulani tayi murmushi tace, duk yanda nake tausayinshi ai gara inzauna indawo da martabata ni kaina wani lokacin kyan kyamin kaina nakeji, kiduba fa kigani duk wata kazanta damuke fitarwa haka zanyita ingama babu wani wanka. Kai gaskiya mutanen nan sun cutar dani.
Jakadiya Safeeya tace wai ahaka ma kinsamu bakar da ba, kuma kinga acikin kwana goma zaki samu gyara sosai, wanda Sarki zeyi farin ciki da haka. Gimbiya tace ai wannan gyaran na musamman zakisha, suma Yarana nasu nadabanne.
Kallon Jakadiya Safeeya tayi tace akwai wani abu danake so inhada, amma anjima idan hubby yadawo zamuyi maganar, kema yakamata, ai ko? Jakadiya tace bangane ba? Murmushi Gimbiya tayi tace a'a bakomai dama gani nayi Waziri tunda matarshi ta mutu be kara aure ba, kuma dama diyarshi daya sunyi mata aure. Shine naga kema mijinki yarasu ai.
Dariya Fulani tayi tace kai amma wlh Aunty kin iya hangen nesa. Tashi Jakadiya tayi tana murmushi, Gimbiya tace, ina kuma zakije? Fita tayi bata cemata komai ba. Gimbiya tace Allah da gaske nakeyi, kuma insha Allahu wannan abu seya tabbata, zansa Hubby yafadama Malam, kinga se ayi tare dana su Amatu. Fulani tace Allah yasa.
Zaune suke acikin lambu, beauty Amatullah tana zaune agefen Areef yana koyamata karatu, su Haisam suma suna gefe guda suna firarsu. Areef ya kalli Haisam yace wai abokina ya kukayi da Dady akan maganar Ayman?.
Murmushi yayi yace yafi kowa mafarin ciki shida Momy dasukaji maganar, yace idan Baffa yadawo zasuzo. Areef yace ai gara azo a aurar damu kowama yahuta ko Beauty na? Kai tadaga mashi tana murmshi. Haisam yace Beauty bahaka zakice ba, a,a zakice.
Hararshi Areef yayi yace todan bukulu ai seka hanata, kuma wlh wannan sunan yafita abakinka, tunda de ansamata suna kawai ka kirata da Amatullahin ta. Haisam yace bazan kiraba, ni nariga dana saba.