Sashe 28
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Nayafe maki Zakiyyah Allah ya yafe maki, insha Allah zanrika kawo maki ziyara harkifito, idan kuma na mutu, addu,ar ki nake nema, idan kinrigani mutuwa, addu,a ta zata sameki har kabarinki. Sakinta tayi tanufi waje dasauri tana kuka.
Da gudu Zakiyyah tabita, sede kafin ta isa harsun tada mota sun nufi gate, haka taruga da gudu, tana binsu, suna fita aka kulle kofar, anan tazube tana kuka, duk mutanen gidan suna kallonta.
Acikin mota kuwa Umman Zakiyyah se kuka takeyi, haka Sarki yajawota yana lallashinta. Tace shikenan yanzu kowa seyasan abinda Zakiyya tayi, shikenan yanzu banida sauran kima agurin mutane. Sarki yace namaki alkawarin babu wanda zesan abinda Zakiyyah tayi, sede idan tadawo gida, zamusan abinda zamu fada. Kwanciya tayi tana fadin nagode.
Tunda suka fita Sarki Hasheem yake kuka, yakasa denawa,gaba daya tausayin Zakiyyah da iyayenta yakamashi, kuka yakeyi kamar karamin yaro, gaba daya jijiyoyin kanshi sunfito, ganin haka Waziri yayima Likitansu waya, yazo.
Bayan yagama dubashi yayi mashi wasu allurai kuma aka bashi magani, ko minti 5 bekara ba yayi bacci. Likita yace jininshi ya hau sosai, kuma zuciyarshi tana bugawa dasauri, saboda tashin hankalin daya shiga, zeyi bacci na tsawon awa 8 kafin ya farka, idan yatashi ayi kokarin mantar dashi duk wata damuwa dazata kara dawo mashi. Sallama yayi masu yafita. Anan suka kulle mashi dakin suka fita.
Sarki Qaseem yace Malam muje agama abinda za,ayi kozamu dena kallon fuskokin wadancan munafukan. Waziri ya kalli Areef yace kaja beautyn taka kubar gurin nan banaso taga komai, idan zaka dawo kayi kallo to ita de kabarota acan.
Haisam ya kalli Ayman yace kema wuce mutafi banason kirika mun kuka, murmushi tayi tace aini babbace kuma nafi Beauty sanin matsalolin rayuwa. Dan haka kabarni in kalla, hakan ze karamun imani dajin tsoron aikata kowane irin zunubi. Murmushi yayi dan yaji dadin kalamanta.
Gaba daya mutanen masarautar harma da mutanen waje seda suka cika babban filin da ake wasan dokuna na Masarautar BUBAYERO, dan kowa yanason yaga yanda za,a aiwatar da wannan hukunci.
Hada manyan malaman masarautar suma sun halacci gurin, haka aka fito da masu laifi kowa yasaka kayan yari ajikinshi, gaba daya kunyar mutanen gurin sukeji, gani sukeyi kamar duka mutanen duniya ne, aka tara agurin ganin irin yawan da mutanen suke dashi.
Kowa neman boyewa yakeyi bayan dan uwanshi, Zakiyyah duk tafi kowa jin kunyar jama'an gurin, jitake kamar kasa ta tsage tashige. Duk abinda takeyi Malam yana kallonta, besan lokacin da kwalla tazubo mashi ba.
Bawai tausayinta yasa shi kuka ba, kawai daya kalli yanda take boyewa dan kawai taga yan tsirarrun mutane, wadan da ko rabin garin Gombe basu kai ba, amma shine take jima kunya. To inda ranar lahira ce Allah ya tadata agaban biliyoyin mutane yazataji? Wannan tunanin shine abinda yasaka Malam kuka.
Bayan sun tsaya agurin da aka tanadar masu, kowa yasamu nutsuwa, sannan Malam yahau kan wani guri medan tudu shida Sarki Qaseem da limamin masallacin masarautar, tayanda kowa ze iya ganinsu.
Seda Malam yasa liman yabude masu taron da addu'a sannan yafara magana. Har yanzu hawaye basu dena fitowa daga idonshi ba, musamman daya hau sama yaga mutane sun nutsu gefe guda kuma ga masu laifi suma sun tsaya suna kuka.
Kyalle yasa ya goge idonshi sannan yafara magana. Alhamdulillahi, kamar yanda kowa yasan dalilin taruwar mu agurin nan, kuma naji dadi matuka da Allah yasa naga Mata da Maza, Yara da Tsofaffi, sun halacci gurin nan.
Saboda kowa ze kalli yanda kowa ze amshi hukuncinsa. Nasan yawancin mutanen gurin nan masu hankali, wannan taron kadai ya isa ya tunatar da kowa tashin kiyama, da kuma tsayuwar hisabi.
Da farko inaso indanyi amfani da wannan dama inyima jama'a tunatarwa akan rayuwar duniya data lahira, hakika wannan abu da mutanen gidan nan suka aikata yasa mutane dayawa zasu koyi darasi.
Zanyi magana akan abu 2.
AMANA, da ZINA.
Wa iyazubillah. Hakika mutane dayawa sun shagala azamanin nan gurin Cin AMANA. Basajin kunyar ha'intar makusantansu. Dama Manzon Allah (s.a.w), yace idan karshen duniya yazo amana zatayi karanci, bawa ze iya cin amanar Uban gidanshi, kamar yanda Da ze iya cin amanar mahaifanshi.
Ayanzu halin damuke ciki kenan mutane basu dauki cin amana abakin komai ba.
(1) Kamar yanda yazo acikin hadisin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi. Inda Abdullahi bn Abbas (RA) yace. Lallai kyawawan aiyuka suna sanya mutum hasken fuska da na zuciya da yalwar arziki da karfin jiki da soyayya daga bayin Allah.
Kamar yanda sabon Allah yake sa fuska da zuciya duhu da raunin jiki da tawayan arziki da kiyayya daga mutane.
Rawahul Muslim.
(2). Allah ta'ala yana cewa. Kuma wadanda sukayi kokari ga nemar yardarmu. Lallai muna shiryar dasu ga hanyoyinmu, kuma lallai tabbas Allah yana tare da masu kyautatawa.
(Suratul Ankabut, Aya ta 69).
(3) Allah ta'ala yana cewa. Babu wata musiba dazata sameku, face sai sakamakon abinda hannuwanku suka aikata.
(Suratul Al shuura Aya ta 30).
Sadakallahul Azim.
Kai jama,a, ina zamu kai wannan girman zunubi damuke daukar ma kanmu? Hakika Allah baya yafe laifin wani akan wani. Baka tunanin idan kaci amanar wani Allah yadauki ranshi ko ranka batare daka nemi yafiyarshi ba? Jama'a yakamata mutuba zuwa ga Allah, wlh duniyar nan tafiya takeyi.
Kada muyarda wasu subamu amana mu ci masu, ayanzu wanda ka yarda dashi shine wanda yake cutarka. Allah yasa mufi karfin zuciyarmu. Kowa da anyi magana seya ce Shedan. Kada kumanta shifa Shedan seyasamu kofar shiga jikin dan Adam yake iya shiga har yasamu damar yimasa mummunar huduba.
Idan har mukayi riko da gaskiya da Amana, muka koma ga Allah, tabbas ze cecemu daga sharrin shaidan. Idan baku manta ba, duk yanda shedan yakai ga hallakar da bayin Allah baze taba samun nasara agurin wadan da Allah ya tsare ba. Ba kuma tsayawa zakayi harse kasamu tabbacin lallai Allah ya tsareka sannan zaka rika addu,a ba.
Manzon Allah dakanshi yana neman tsari daga sharrin shaidan, wanda kowa yasani yafi karfin shedan, Allah yariga da ya haramta ma shedan kusantar manzonsa. Amma duk da haka Annabi be kwanta ba yace Allah yatsa reshi baze nemi wani tsari daga gareshi ba.
To kai waye dabazaka nemi tsari daga sharrin shaidan ba? Yakamata kowa yadage da yaki da zuciyarshi, ita kadaice hanyar dazata tseratar damu. Allah yasa mudace.
Magana ta biyu akan ZINA. Innalillahi Wa inna ilaihirraji'un. Wannan abu itace abinda yake damun mutane dayawa, babu yara, ba manya, marasa aure, har masu aure. ZINA wata musiba ce acikin al'umma.
Allah ya haramta zina, shiyasa ma yace kada ku kusanceta. ZINA tana tarwatsa duk wani mutunci na dan Adama, tana sa talauci. Shiyasa Allah yakawo hukuncin ZINA acikin alkur'ani me girma.
Dan haka ayau kowa zega irin hukuncin daya kamata ayima duk wanda ya aikata ZINA. Allah yashiryar damu da iyalanmu, baki daya. Kafin afara akwai jawabin da Sarki zeyi maku.
Komawa baya Malam yayi yana share kwallan idonshi, Jama,a da dama agurin seda suka zubar da hawaye akan jawabin da Malam yayi. Sarki Qaseem yafara magana, shima daka kalli idonshi zaka gane kuka yayi.
Alhamdulillahi, kamar yanda Malam yayi mana jawabi, nasan mutane dayawa sun kara sanin me ake ciki arayuwa. Kamar yanda zamu fara aiwatar da wannan hukunci, ina me fada da babbar murya, daga yau, duk wanda aka kara kamawa acikin kasata, dumu dumu da laifin aikata ZINA , kowani laifi, tabbas se hukunci yahau kanshi.
Ko wanene, kuma ko wacece, kowane irin matsayi mutum yake dashi, zamu buga tambari wannan doka zata fara ayau. Kuma naji dadi sosai da dokar zata fara daga cikin Masarautar mu, acikinta ma hada masu sarauta aciki. Karewa ma, hada matan Sarki Hasheem guda 2. Tunda har muka iya aiwatar da hukunci akansu.
Babu wanda za,a kara daga ma kafa idan ya aikata zina, watakila hakan yakawo mana sauki acikin kasarmu. Daga karshe ina yima Allah godiya daya nuna mana wannan rana. Sauka yayi idanunshi suna fitar da kwalla.
Anan Waziri yasa aka cire Zakiyya da Jakadiya Karima, dasu Mati da Lado gefe guda, kuma aka fadama mutane irin hukuncin da aka yanke masu. Medaki se Kuka takeyi. Tanufo gurin su Gimbiya Suhailat da Fulani, wadanda suma kukan sukeyi.
Har kasa ta duka sede takasa yin magana saboda kukan datakeyi, hannuwanta biyu kawai tahada alamun neman yafiya tacigaba da kuka. Kamota sukayi suka rungumeta suna kuka.
Seda suka saka kowa kuka agurin, wasu mata sukazo suka kamata, seda tayi addu,a sannan aka sata cikin ramin aka rufe jikinta akabar fuskarta. Tunda su Fulani sukaga haka suka bar gurin suna kuka, mata dayawa seda suka bar gurin, hatta da Sarki Qaseem fada yakoma yana kuka, kasa tsayawa yayi agurin.
Bayan anyi mata addu,a akasa yara suka fara jifarta, ahaka harseda ta mutu😭. Wa iyazubillah. Allah ka tsaremu daga aikata ZINA. Amin.
Zakiyyah agurin tazube asume saboda tsabar kaduwa, Jakadiya kam kuka kawai takeyi. Haka wasu suka dauketa aka shiga da ita ciki.
Boka da Sarkin Fada aka kira. Idanun Sarkin Fada sunyi jajur saboda kuka, haka shima yaje gurin Waziri, da Sauran mutane, yana kuka yana neman yafiyarsu. Bayan anyi masu addu'a aka dorasu saman wani table, aka samasu bakar hula afuskarsu sannan aka ture su daga kan table din. Haka sukayita lilo har suka mutu😭. Sannan aka tasa keyar sauran masu laifi zuwa kurkutu, alokacin Zakiyyah ta farfado itama aka hada da ita.
Gaba daya mutanen dake gurin babu wanda bezubar da hawaye ba, jikin kowa yayi sanyi, tsoro yashiga zukatansu. Haka aka taru akayi masu sallah aka wuce dasu makabarta.
INNALILLAHI WA INNAILAIHIRRAJI'UN😭😭. Allah kasa mufi karfin zuciyarmu. Bazan iya cigaba. Da typing ba se zuwa gobe idan Allah ya kaimu. Abinda nafada da kuskure Allah yayafe mani.
Nagode da kulawarku, sekunjini anext page insha Allah.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 115⚜120
LAST PAGE
Washe gari Sarki Hasheem yasamu karfin jikinshi, da misalin karfe 10, gaba dayansu suka taru a babban falo, bayan anbude taro da addu,a anan aka fada ma Sarki Hasheem duk abinda yafaru jiya, sosai ya tausaya ma Medaki.
Da gudu Zakiyyah tabita, sede kafin ta isa harsun tada mota sun nufi gate, haka taruga da gudu, tana binsu, suna fita aka kulle kofar, anan tazube tana kuka, duk mutanen gidan suna kallonta.
Acikin mota kuwa Umman Zakiyyah se kuka takeyi, haka Sarki yajawota yana lallashinta. Tace shikenan yanzu kowa seyasan abinda Zakiyya tayi, shikenan yanzu banida sauran kima agurin mutane. Sarki yace namaki alkawarin babu wanda zesan abinda Zakiyyah tayi, sede idan tadawo gida, zamusan abinda zamu fada. Kwanciya tayi tana fadin nagode.
Tunda suka fita Sarki Hasheem yake kuka, yakasa denawa,gaba daya tausayin Zakiyyah da iyayenta yakamashi, kuka yakeyi kamar karamin yaro, gaba daya jijiyoyin kanshi sunfito, ganin haka Waziri yayima Likitansu waya, yazo.
Bayan yagama dubashi yayi mashi wasu allurai kuma aka bashi magani, ko minti 5 bekara ba yayi bacci. Likita yace jininshi ya hau sosai, kuma zuciyarshi tana bugawa dasauri, saboda tashin hankalin daya shiga, zeyi bacci na tsawon awa 8 kafin ya farka, idan yatashi ayi kokarin mantar dashi duk wata damuwa dazata kara dawo mashi. Sallama yayi masu yafita. Anan suka kulle mashi dakin suka fita.
Sarki Qaseem yace Malam muje agama abinda za,ayi kozamu dena kallon fuskokin wadancan munafukan. Waziri ya kalli Areef yace kaja beautyn taka kubar gurin nan banaso taga komai, idan zaka dawo kayi kallo to ita de kabarota acan.
Haisam ya kalli Ayman yace kema wuce mutafi banason kirika mun kuka, murmushi tayi tace aini babbace kuma nafi Beauty sanin matsalolin rayuwa. Dan haka kabarni in kalla, hakan ze karamun imani dajin tsoron aikata kowane irin zunubi. Murmushi yayi dan yaji dadin kalamanta.
Gaba daya mutanen masarautar harma da mutanen waje seda suka cika babban filin da ake wasan dokuna na Masarautar BUBAYERO, dan kowa yanason yaga yanda za,a aiwatar da wannan hukunci.
Hada manyan malaman masarautar suma sun halacci gurin, haka aka fito da masu laifi kowa yasaka kayan yari ajikinshi, gaba daya kunyar mutanen gurin sukeji, gani sukeyi kamar duka mutanen duniya ne, aka tara agurin ganin irin yawan da mutanen suke dashi.
Kowa neman boyewa yakeyi bayan dan uwanshi, Zakiyyah duk tafi kowa jin kunyar jama'an gurin, jitake kamar kasa ta tsage tashige. Duk abinda takeyi Malam yana kallonta, besan lokacin da kwalla tazubo mashi ba.
Bawai tausayinta yasa shi kuka ba, kawai daya kalli yanda take boyewa dan kawai taga yan tsirarrun mutane, wadan da ko rabin garin Gombe basu kai ba, amma shine take jima kunya. To inda ranar lahira ce Allah ya tadata agaban biliyoyin mutane yazataji? Wannan tunanin shine abinda yasaka Malam kuka.
Bayan sun tsaya agurin da aka tanadar masu, kowa yasamu nutsuwa, sannan Malam yahau kan wani guri medan tudu shida Sarki Qaseem da limamin masallacin masarautar, tayanda kowa ze iya ganinsu.
Seda Malam yasa liman yabude masu taron da addu'a sannan yafara magana. Har yanzu hawaye basu dena fitowa daga idonshi ba, musamman daya hau sama yaga mutane sun nutsu gefe guda kuma ga masu laifi suma sun tsaya suna kuka.
Kyalle yasa ya goge idonshi sannan yafara magana. Alhamdulillahi, kamar yanda kowa yasan dalilin taruwar mu agurin nan, kuma naji dadi matuka da Allah yasa naga Mata da Maza, Yara da Tsofaffi, sun halacci gurin nan.
Saboda kowa ze kalli yanda kowa ze amshi hukuncinsa. Nasan yawancin mutanen gurin nan masu hankali, wannan taron kadai ya isa ya tunatar da kowa tashin kiyama, da kuma tsayuwar hisabi.
Da farko inaso indanyi amfani da wannan dama inyima jama'a tunatarwa akan rayuwar duniya data lahira, hakika wannan abu da mutanen gidan nan suka aikata yasa mutane dayawa zasu koyi darasi.
Zanyi magana akan abu 2.
AMANA, da ZINA.
Wa iyazubillah. Hakika mutane dayawa sun shagala azamanin nan gurin Cin AMANA. Basajin kunyar ha'intar makusantansu. Dama Manzon Allah (s.a.w), yace idan karshen duniya yazo amana zatayi karanci, bawa ze iya cin amanar Uban gidanshi, kamar yanda Da ze iya cin amanar mahaifanshi.
Ayanzu halin damuke ciki kenan mutane basu dauki cin amana abakin komai ba.
(1) Kamar yanda yazo acikin hadisin Manzon Allah tsira da amincin Allah su tabbata agareshi. Inda Abdullahi bn Abbas (RA) yace. Lallai kyawawan aiyuka suna sanya mutum hasken fuska da na zuciya da yalwar arziki da karfin jiki da soyayya daga bayin Allah.
Kamar yanda sabon Allah yake sa fuska da zuciya duhu da raunin jiki da tawayan arziki da kiyayya daga mutane.
Rawahul Muslim.
(2). Allah ta'ala yana cewa. Kuma wadanda sukayi kokari ga nemar yardarmu. Lallai muna shiryar dasu ga hanyoyinmu, kuma lallai tabbas Allah yana tare da masu kyautatawa.
(Suratul Ankabut, Aya ta 69).
(3) Allah ta'ala yana cewa. Babu wata musiba dazata sameku, face sai sakamakon abinda hannuwanku suka aikata.
(Suratul Al shuura Aya ta 30).
Sadakallahul Azim.
Kai jama,a, ina zamu kai wannan girman zunubi damuke daukar ma kanmu? Hakika Allah baya yafe laifin wani akan wani. Baka tunanin idan kaci amanar wani Allah yadauki ranshi ko ranka batare daka nemi yafiyarshi ba? Jama'a yakamata mutuba zuwa ga Allah, wlh duniyar nan tafiya takeyi.
Kada muyarda wasu subamu amana mu ci masu, ayanzu wanda ka yarda dashi shine wanda yake cutarka. Allah yasa mufi karfin zuciyarmu. Kowa da anyi magana seya ce Shedan. Kada kumanta shifa Shedan seyasamu kofar shiga jikin dan Adam yake iya shiga har yasamu damar yimasa mummunar huduba.
Idan har mukayi riko da gaskiya da Amana, muka koma ga Allah, tabbas ze cecemu daga sharrin shaidan. Idan baku manta ba, duk yanda shedan yakai ga hallakar da bayin Allah baze taba samun nasara agurin wadan da Allah ya tsare ba. Ba kuma tsayawa zakayi harse kasamu tabbacin lallai Allah ya tsareka sannan zaka rika addu,a ba.
Manzon Allah dakanshi yana neman tsari daga sharrin shaidan, wanda kowa yasani yafi karfin shedan, Allah yariga da ya haramta ma shedan kusantar manzonsa. Amma duk da haka Annabi be kwanta ba yace Allah yatsa reshi baze nemi wani tsari daga gareshi ba.
To kai waye dabazaka nemi tsari daga sharrin shaidan ba? Yakamata kowa yadage da yaki da zuciyarshi, ita kadaice hanyar dazata tseratar damu. Allah yasa mudace.
Magana ta biyu akan ZINA. Innalillahi Wa inna ilaihirraji'un. Wannan abu itace abinda yake damun mutane dayawa, babu yara, ba manya, marasa aure, har masu aure. ZINA wata musiba ce acikin al'umma.
Allah ya haramta zina, shiyasa ma yace kada ku kusanceta. ZINA tana tarwatsa duk wani mutunci na dan Adama, tana sa talauci. Shiyasa Allah yakawo hukuncin ZINA acikin alkur'ani me girma.
Dan haka ayau kowa zega irin hukuncin daya kamata ayima duk wanda ya aikata ZINA. Allah yashiryar damu da iyalanmu, baki daya. Kafin afara akwai jawabin da Sarki zeyi maku.
Komawa baya Malam yayi yana share kwallan idonshi, Jama,a da dama agurin seda suka zubar da hawaye akan jawabin da Malam yayi. Sarki Qaseem yafara magana, shima daka kalli idonshi zaka gane kuka yayi.
Alhamdulillahi, kamar yanda Malam yayi mana jawabi, nasan mutane dayawa sun kara sanin me ake ciki arayuwa. Kamar yanda zamu fara aiwatar da wannan hukunci, ina me fada da babbar murya, daga yau, duk wanda aka kara kamawa acikin kasata, dumu dumu da laifin aikata ZINA , kowani laifi, tabbas se hukunci yahau kanshi.
Ko wanene, kuma ko wacece, kowane irin matsayi mutum yake dashi, zamu buga tambari wannan doka zata fara ayau. Kuma naji dadi sosai da dokar zata fara daga cikin Masarautar mu, acikinta ma hada masu sarauta aciki. Karewa ma, hada matan Sarki Hasheem guda 2. Tunda har muka iya aiwatar da hukunci akansu.
Babu wanda za,a kara daga ma kafa idan ya aikata zina, watakila hakan yakawo mana sauki acikin kasarmu. Daga karshe ina yima Allah godiya daya nuna mana wannan rana. Sauka yayi idanunshi suna fitar da kwalla.
Anan Waziri yasa aka cire Zakiyya da Jakadiya Karima, dasu Mati da Lado gefe guda, kuma aka fadama mutane irin hukuncin da aka yanke masu. Medaki se Kuka takeyi. Tanufo gurin su Gimbiya Suhailat da Fulani, wadanda suma kukan sukeyi.
Har kasa ta duka sede takasa yin magana saboda kukan datakeyi, hannuwanta biyu kawai tahada alamun neman yafiya tacigaba da kuka. Kamota sukayi suka rungumeta suna kuka.
Seda suka saka kowa kuka agurin, wasu mata sukazo suka kamata, seda tayi addu,a sannan aka sata cikin ramin aka rufe jikinta akabar fuskarta. Tunda su Fulani sukaga haka suka bar gurin suna kuka, mata dayawa seda suka bar gurin, hatta da Sarki Qaseem fada yakoma yana kuka, kasa tsayawa yayi agurin.
Bayan anyi mata addu,a akasa yara suka fara jifarta, ahaka harseda ta mutu😭. Wa iyazubillah. Allah ka tsaremu daga aikata ZINA. Amin.
Zakiyyah agurin tazube asume saboda tsabar kaduwa, Jakadiya kam kuka kawai takeyi. Haka wasu suka dauketa aka shiga da ita ciki.
Boka da Sarkin Fada aka kira. Idanun Sarkin Fada sunyi jajur saboda kuka, haka shima yaje gurin Waziri, da Sauran mutane, yana kuka yana neman yafiyarsu. Bayan anyi masu addu'a aka dorasu saman wani table, aka samasu bakar hula afuskarsu sannan aka ture su daga kan table din. Haka sukayita lilo har suka mutu😭. Sannan aka tasa keyar sauran masu laifi zuwa kurkutu, alokacin Zakiyyah ta farfado itama aka hada da ita.
Gaba daya mutanen dake gurin babu wanda bezubar da hawaye ba, jikin kowa yayi sanyi, tsoro yashiga zukatansu. Haka aka taru akayi masu sallah aka wuce dasu makabarta.
INNALILLAHI WA INNAILAIHIRRAJI'UN😭😭. Allah kasa mufi karfin zuciyarmu. Bazan iya cigaba. Da typing ba se zuwa gobe idan Allah ya kaimu. Abinda nafada da kuskure Allah yayafe mani.
Nagode da kulawarku, sekunjini anext page insha Allah.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 115⚜120
LAST PAGE
Washe gari Sarki Hasheem yasamu karfin jikinshi, da misalin karfe 10, gaba dayansu suka taru a babban falo, bayan anbude taro da addu,a anan aka fada ma Sarki Hasheem duk abinda yafaru jiya, sosai ya tausaya ma Medaki.