Sashe 22
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ai dasauri Gimbiya ta tashi tana kallonshi, se alokacin ta kula da yanayinshi, idanunshi sunyi ja sosai,cike da kaduwa tace hubby dan Allah meyafaru, kallonta yayi dan yafara kulewa da ita, tureta yayi cike da bacin rai, yace ya ina tambayarki kina tambayata dan kin rai nani, kawai kifadamun abinda yafaru idan bahaka zanbar maki gidan. Matsowa tayi ta rungumeshi tana kuka, dan tunda suke betaba yimata irin wannan ba, asalima bata taba ganinshi cikin irin wannan yanayin ba.
Dagowa tayi tajawoshi suka zauna bisa gado, kanshi tajawo tadora saman cinyarta tana ta shafa kanshi, lumshe ido yayi, yana sauke ajiyar zuciya. shiru sukayi nawani lokaci, jinyayi shiru yasa tadagshi ta tashi takawo mashi ruwa mesanyi, dakanta tabashi, kofi guda ya shanye, sannan takara jawoshi yakwanta akan cinyarta.
Ahankali tana shafa kanshi tace hubby karika fadin Innalillahi Wainnailaihirraji,un, kayi haka harso 5, sannan infada maka abinda yafaru, amma ina fatan bazakamun fada ba idan kaji abinda nayi?
Cike da fargaba Medaki tashiga falon Gimbiya Zakiyyah, alokacin tana zaune tana hutawa, kallonta tayi tace kekuma lafiyarki zaki shigo mani gida ahaka, ko Sarki ne ya mutu? Medaki tazauna tace ai da mutuwa yayi zefi sauki da halin dazamu shiga nida ke, da su Jakadiya, cinkin lokaci kadan.
Tashi tayi daga kishingiden datake tana yamutsa fuska tace bangane abinda kike nufi ba? Anan tafada mata duk abinda yafaru, har halin datake ciki ita da Sarkin Fada seda tafada mata, dan ita tariga da tagama yarda da ita, tunda taga halinsu daya ne. Wani irin miskilin murmushi Gimbiya Zakiyyah tayi, tayi mata wani irin kallo, tace.
Lallai bansan ke Jahila bace se yau, wato keda Sarkin fada kundade kuna aikata alfasha, saboda kinga Sarki beda lafiya, kai, wama yasan tun lokacin da kuke tare? Hmmmm dama nafada, shiyasa duk abinda yafaru daku wlh bazanji tausayinku ba, kema kijira sammaci anjima ko gobe, dan tunda Waziri yakamaku da kanshi, kema kinsan hukuncin kisane akanki.
Tir da ke, kina matar Sarki kinabin maza, mazan ma wai Sarkin Fadan Mijinki. Kodayake ba laifinki bane, dama shi talaka kome akayi dashi, seya baka kunya, yanzu tayaya wanda yafito daga jinin sarauta ze aikata irin abinda kikayi?
To wlh bari infada maku dake dasu gaba daya, daga yau babu ni babu ku, kuma koda kunbude baki kunfadi abinda nasa akayima Rayhana, babu wanda zeyarda daku, dan bakuda sheda, kuma ni daga gidan sarauta nake, zan iya amfani da karfin mulkina inkwaci kaina, dan kunsan atsari na sarauta ba,a yanke hukunci dole seda sheda bayyanan na, ku kam bakuda wata shedar dazata nuna akwai sa hannuna aciki.
Kitashi kibani guri tunkafin azo aganki agurina. Cikin kuka Medaki tace dan Allah kada kinmani haka, nabaki duka yarda, banda kowa aduniyar nan kece silar jefani cikin wannan harka dan Allah kada kice zaki juya mun baya, kinsani duk wani abu da muka aikata shawararki mukebi, saboda kece babba. Hannu tadaga mata tamike tsaye tace nace kitashi kibani guri kada inkara ganin kafarki agidana.
Ni nabi shawarar kiyi zina da kaskantaccen talaka kuma yaron mijinki? Kafin asirinku yatonu kintaba fadamun halin dakuke ciki? Dan haka wlh kinji narantse maki baruwana acikin harkarku, fita nace. Tashi Medaki tayi tana kuka tafita waje. Wata irin dariya Gimbiya Zakiyya tasaka tace, uhmm dani kuke magana, anfada maku sarauta haukace? Kaima sarkin fada nasan kana tunanin katona asirina.
Ni kuma zan nuna maka bakada wayau,duk duniyar nan babu wanda zeyarda da kai dan kafada masu munyi harka tare, domin kuwa babu wanda yasan munyi daga ni sekai, kuma agidan sarauta ba,a karbar shedar mutum daya, kuma shedar ma tabaki. Dariya tasa tashige daki.
Saurin tashi Sarki Qaseem yayi yana kallon Gimbiya Suhailat, bayan tagama bashi labarin abinda yafaru. Kai yafara girgizawa ta kalleshi tace dan Allah kayi hakuri, wlh banyi haka dan in cutar dashi ba, kuma ni bansan Son dayake mata ya kai haka ba, kuma gani nayi nida kai munzaba mashi wadda ze aura shiyasa nayi haka.
Murmushi Sarki yayi yace kinzaba mashi de, kuma ita Ayman din ai tasamu wanda take so, to koma bata samu ba, yarinyar dayakeso ita zanbashi sede ita Ayman tazo ta 2, domin kuwa kinso ki tabka babban kuskure, ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba, yarinyar da kika gansu tare da Areef jinina ce, kuma shima jininshi ce, bari inje asibitin inga halin dasuke ciki.
Kuma kisani tunda har Ayman tasamu wanda takeso to bazata auri Areef ba, da ace tana sonshi, to zanbashi shawara ya aureta, amma tunda haka tafaru, kowa ze auri zabinshi. Kuma kisamu kalaman dazaki bama Jadiya Safeeya hakuri dasu, dan kinci mata mutunci, matar da ta sadaukar da jin dadinta domin takaremu.
Matar da tabaro kowa nata, badan tana cikin talauci ba, a,a kawai dan tazauna damu da gaskiya. Juyawa yayi yanufi kofa zefita, da gudu tarugo tarikeshi tabaya tana kuka tace, dan Allah hubby kayi hkr kada kamun irin wannan horon, naji nayarda da duk abinda kace, kuma nahakura Yarima ya auri koma wacece amma dan Allah kafitar dani duhu, kuma kada kayi fushi dani kasan bamu saba haka ba.
Murmushin jindadi yayi, sede bejuyo ba, yace ki kwantar da hankalinki, danki ze auri irin yarinyar da mukeso, yar gidan sarauta, albishir daya zan maki, wannan yarinyar da kika gani ba kowa bace se diyar Yaya da Fulani. Kuma wani abun farin cikin yanzu haka Fulani tana cikin gidan nan, sauran bayani sena dawo zakiji, yana fadin haka yayi waje. Wani irin yanayi tashiga, gaba daya tarasa mezatayi, ga kunyar abinda tayi yadameta, musamman idan ta tuno kalaman data fadama jakadiya, komawa tayi daki tana tunani.
Cikin sa,a da kwarewa tare da temakon Allah beauty ta farfado, numfashinta ya dedeta, sede haryanzu bata bude ido ba, kuma bugun zuciyarta be dedeta ba. Likita yace sukaita dakin hutu, nan da wani lokaci zata dawo dede akwai abinda ya tsoratata shiyasa tashiga wannan yanayin.
Adede lokacin Sarki da Waziri suka iso asibitin,kai tsaye office din likita suka wuce, bayan sun gaisa yayi masu bayanin halin da ake ciki. Sarki yace amma yaya jikin yarinyar? Likita yace insha Allahu babu wata damuwa, zata dawo dede. Amma Yarima jikinshi dasauki. Godiya suka mashi yasa aka nuna masu dakin Areef da beauty.
Seda Sarki yafara shiga gurin beauty, kwance yasameta kamar matatta, Jakadiya Safeeya tana gefenta se kuka takeyi, sallamarsu ce tasa tayi saurin goge idonta, ta tashi tana mika gaisuwa, da kyar ya amsa, hankalinshi yana kan beauty, sak kamarta da Fulani da Areef yake gani afuskarta, wasu hawayen farin ciki ne, suka zubo mashi.
Kusa da ita ya matsa, fuskarta ya shafa ya kalli Waziri yace tabbas ita ce, ko ba,a fadamun ba nasan wannan jinin Yaya ce, Allah sarki, Allah maji rokon bayinsa, insha Allahu ayau Yaya zesamu babban albishir, ayanzu base gobe ba. Kallon Jakadiya yayi yace kifadamun Ina Fulani take, inje da kaina inkaima Yaya ita?.
Se alokacin Jakadiya ta tuna sunbarta agida, damma tasan barci takeyi, sede tana duba agogo taga lokacin tashinta yakusa, gashi basu kulle gidan ba, cike da tashin hankali ta kalli Sarki tace Rankai dade tana gida kuma yanzu zuwa wani lokaci zata iya farkawa, gashi bankulle gidan ba, ina tsoron tafito, koza,a sa amaidani gida kada tafito?.
Waziri yace babu damuwa, muje muga jikin Areef semuwuce tare. Sarki yace a,a tunda ance jikin nashi dasauki kawai. Muwuce, Jakadiya tace to bari inma Ayman magana seta dawo nan tazauna kada tafarka. Waziri yace rankaidade muje gaba daya muga jikinshi semu wuce.
Areef da Haisam suna cikin tsara yanda zasu hada plan, Ayman tana gefe duk tashiga damuwa se kallon Haisam takeyi tana tunanin idan aka rabasu bazata iya. Hakura dashi ba. Turo kofar da akayi ne. Tasa su saurin kallon kofa, Areef suna hada ido da sarki yayi saurin komawa ya kwanta tare da rufe ido.
Dariya yakusa bama Sarki, bayan sun shigo Sarki ya matsa kusa dashi yace lallai yarona kai ragone tunda har zaka iya kwanciya asibiti saboda mace, to danazo ince maka na amince da zabinka amma tunda naga baka warke ba, nafasa, ai dasauri yamike yariko hannun Sarki yana fadin wlh nawarke koyanzu ma asallameni. Gaba daya dakin seda suka sa dariya, hada Ayman me kuka. Sarki yace ka kwantar da hankalinka babu wanda ze hanaka auren zabinka, kuma jininka, bari muje gida mudawo, kallon Haisam yayi yace ka kula dasu, ke kuma me kukan soyayya sekiyi shiru tunda zaki samu abinda kikeso, kitashi kije gurin Diyata kizauna zamu dawo yanzun nan. Juyawa yayi yafita suma suka bisu abaya.
Cike da Mamaki Areef ya kalli Haisam yace Jinina, kuma diyar Abba? Tome yake nufi? Kafada Haisam yadaga alamun shima besani ba, yace mujira sudawo maji daga garesu.
Jakadiya Karima se kuka take tana fadin tsakanina da Gimbiya Zakiyya Allah ya isa, muguwar mata tasamu cikin bala,i kuma gashi yanzu mune akulle, bamuda wata sheda dazata nunama mutane tanada hannnu acikin abinda muka aikata. Kaicona ni Karima, ban rike amanar da mutanan nan suka bani ba, naci amanarsu, nima kuwa Allah baze barni ba. Yanzu shikenan haka za,a yanke mana hukunci muna kallo abar Gimbiya?.
Wata irin dariya Sarkin fada yayi yace kidena bata hawayenki abanza, waye yace maki itama zata kubuta? Aini bana barin baya da kura, inde zanyi aiki to dole se nasamu madafa nake farashi, ko anfada maki nima irin kwakwalwar jinin sarauta nakeda ita wadda bata da seti? Kawai malama kizuba ido kisha kallo gobe.
Suna zuwa gidan afalo sukaci karo da ita tafito se raba idanu takeyi. Cak Sarki ya tsaya yazuba mata ido, tabbas ita ce, sede tarame, hannu yadaga sama yanama Allah godiya, Waziri yace Jakadiya kamota muwuce. Hannunta takama suka nufi waje.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 95⚜100
Da sallama suka shiga falon Sarki Hasheem, yana zaune abisa kekenshi yana sana,ar tashi wato tunanin Fulaninshi, matsawa kusa dashi Sarki Qaseem yayi.
Kafadarshi ya dafa ahankali yadago yana kallonshi, wasu siraran hawaye suka fito daga idanunsu su duka biyun, alamu Sarki Hasheem yayi mashi da lafiya? Murmushi yayi mashi yakama kekenshi yafara turawa.
Dagowa tayi tajawoshi suka zauna bisa gado, kanshi tajawo tadora saman cinyarta tana ta shafa kanshi, lumshe ido yayi, yana sauke ajiyar zuciya. shiru sukayi nawani lokaci, jinyayi shiru yasa tadagshi ta tashi takawo mashi ruwa mesanyi, dakanta tabashi, kofi guda ya shanye, sannan takara jawoshi yakwanta akan cinyarta.
Ahankali tana shafa kanshi tace hubby karika fadin Innalillahi Wainnailaihirraji,un, kayi haka harso 5, sannan infada maka abinda yafaru, amma ina fatan bazakamun fada ba idan kaji abinda nayi?
Cike da fargaba Medaki tashiga falon Gimbiya Zakiyyah, alokacin tana zaune tana hutawa, kallonta tayi tace kekuma lafiyarki zaki shigo mani gida ahaka, ko Sarki ne ya mutu? Medaki tazauna tace ai da mutuwa yayi zefi sauki da halin dazamu shiga nida ke, da su Jakadiya, cinkin lokaci kadan.
Tashi tayi daga kishingiden datake tana yamutsa fuska tace bangane abinda kike nufi ba? Anan tafada mata duk abinda yafaru, har halin datake ciki ita da Sarkin Fada seda tafada mata, dan ita tariga da tagama yarda da ita, tunda taga halinsu daya ne. Wani irin miskilin murmushi Gimbiya Zakiyyah tayi, tayi mata wani irin kallo, tace.
Lallai bansan ke Jahila bace se yau, wato keda Sarkin fada kundade kuna aikata alfasha, saboda kinga Sarki beda lafiya, kai, wama yasan tun lokacin da kuke tare? Hmmmm dama nafada, shiyasa duk abinda yafaru daku wlh bazanji tausayinku ba, kema kijira sammaci anjima ko gobe, dan tunda Waziri yakamaku da kanshi, kema kinsan hukuncin kisane akanki.
Tir da ke, kina matar Sarki kinabin maza, mazan ma wai Sarkin Fadan Mijinki. Kodayake ba laifinki bane, dama shi talaka kome akayi dashi, seya baka kunya, yanzu tayaya wanda yafito daga jinin sarauta ze aikata irin abinda kikayi?
To wlh bari infada maku dake dasu gaba daya, daga yau babu ni babu ku, kuma koda kunbude baki kunfadi abinda nasa akayima Rayhana, babu wanda zeyarda daku, dan bakuda sheda, kuma ni daga gidan sarauta nake, zan iya amfani da karfin mulkina inkwaci kaina, dan kunsan atsari na sarauta ba,a yanke hukunci dole seda sheda bayyanan na, ku kam bakuda wata shedar dazata nuna akwai sa hannuna aciki.
Kitashi kibani guri tunkafin azo aganki agurina. Cikin kuka Medaki tace dan Allah kada kinmani haka, nabaki duka yarda, banda kowa aduniyar nan kece silar jefani cikin wannan harka dan Allah kada kice zaki juya mun baya, kinsani duk wani abu da muka aikata shawararki mukebi, saboda kece babba. Hannu tadaga mata tamike tsaye tace nace kitashi kibani guri kada inkara ganin kafarki agidana.
Ni nabi shawarar kiyi zina da kaskantaccen talaka kuma yaron mijinki? Kafin asirinku yatonu kintaba fadamun halin dakuke ciki? Dan haka wlh kinji narantse maki baruwana acikin harkarku, fita nace. Tashi Medaki tayi tana kuka tafita waje. Wata irin dariya Gimbiya Zakiyya tasaka tace, uhmm dani kuke magana, anfada maku sarauta haukace? Kaima sarkin fada nasan kana tunanin katona asirina.
Ni kuma zan nuna maka bakada wayau,duk duniyar nan babu wanda zeyarda da kai dan kafada masu munyi harka tare, domin kuwa babu wanda yasan munyi daga ni sekai, kuma agidan sarauta ba,a karbar shedar mutum daya, kuma shedar ma tabaki. Dariya tasa tashige daki.
Saurin tashi Sarki Qaseem yayi yana kallon Gimbiya Suhailat, bayan tagama bashi labarin abinda yafaru. Kai yafara girgizawa ta kalleshi tace dan Allah kayi hakuri, wlh banyi haka dan in cutar dashi ba, kuma ni bansan Son dayake mata ya kai haka ba, kuma gani nayi nida kai munzaba mashi wadda ze aura shiyasa nayi haka.
Murmushi Sarki yayi yace kinzaba mashi de, kuma ita Ayman din ai tasamu wanda take so, to koma bata samu ba, yarinyar dayakeso ita zanbashi sede ita Ayman tazo ta 2, domin kuwa kinso ki tabka babban kuskure, ko rantsuwa nayi bazanyi kaffara ba, yarinyar da kika gansu tare da Areef jinina ce, kuma shima jininshi ce, bari inje asibitin inga halin dasuke ciki.
Kuma kisani tunda har Ayman tasamu wanda takeso to bazata auri Areef ba, da ace tana sonshi, to zanbashi shawara ya aureta, amma tunda haka tafaru, kowa ze auri zabinshi. Kuma kisamu kalaman dazaki bama Jadiya Safeeya hakuri dasu, dan kinci mata mutunci, matar da ta sadaukar da jin dadinta domin takaremu.
Matar da tabaro kowa nata, badan tana cikin talauci ba, a,a kawai dan tazauna damu da gaskiya. Juyawa yayi yanufi kofa zefita, da gudu tarugo tarikeshi tabaya tana kuka tace, dan Allah hubby kayi hkr kada kamun irin wannan horon, naji nayarda da duk abinda kace, kuma nahakura Yarima ya auri koma wacece amma dan Allah kafitar dani duhu, kuma kada kayi fushi dani kasan bamu saba haka ba.
Murmushin jindadi yayi, sede bejuyo ba, yace ki kwantar da hankalinki, danki ze auri irin yarinyar da mukeso, yar gidan sarauta, albishir daya zan maki, wannan yarinyar da kika gani ba kowa bace se diyar Yaya da Fulani. Kuma wani abun farin cikin yanzu haka Fulani tana cikin gidan nan, sauran bayani sena dawo zakiji, yana fadin haka yayi waje. Wani irin yanayi tashiga, gaba daya tarasa mezatayi, ga kunyar abinda tayi yadameta, musamman idan ta tuno kalaman data fadama jakadiya, komawa tayi daki tana tunani.
Cikin sa,a da kwarewa tare da temakon Allah beauty ta farfado, numfashinta ya dedeta, sede haryanzu bata bude ido ba, kuma bugun zuciyarta be dedeta ba. Likita yace sukaita dakin hutu, nan da wani lokaci zata dawo dede akwai abinda ya tsoratata shiyasa tashiga wannan yanayin.
Adede lokacin Sarki da Waziri suka iso asibitin,kai tsaye office din likita suka wuce, bayan sun gaisa yayi masu bayanin halin da ake ciki. Sarki yace amma yaya jikin yarinyar? Likita yace insha Allahu babu wata damuwa, zata dawo dede. Amma Yarima jikinshi dasauki. Godiya suka mashi yasa aka nuna masu dakin Areef da beauty.
Seda Sarki yafara shiga gurin beauty, kwance yasameta kamar matatta, Jakadiya Safeeya tana gefenta se kuka takeyi, sallamarsu ce tasa tayi saurin goge idonta, ta tashi tana mika gaisuwa, da kyar ya amsa, hankalinshi yana kan beauty, sak kamarta da Fulani da Areef yake gani afuskarta, wasu hawayen farin ciki ne, suka zubo mashi.
Kusa da ita ya matsa, fuskarta ya shafa ya kalli Waziri yace tabbas ita ce, ko ba,a fadamun ba nasan wannan jinin Yaya ce, Allah sarki, Allah maji rokon bayinsa, insha Allahu ayau Yaya zesamu babban albishir, ayanzu base gobe ba. Kallon Jakadiya yayi yace kifadamun Ina Fulani take, inje da kaina inkaima Yaya ita?.
Se alokacin Jakadiya ta tuna sunbarta agida, damma tasan barci takeyi, sede tana duba agogo taga lokacin tashinta yakusa, gashi basu kulle gidan ba, cike da tashin hankali ta kalli Sarki tace Rankai dade tana gida kuma yanzu zuwa wani lokaci zata iya farkawa, gashi bankulle gidan ba, ina tsoron tafito, koza,a sa amaidani gida kada tafito?.
Waziri yace babu damuwa, muje muga jikin Areef semuwuce tare. Sarki yace a,a tunda ance jikin nashi dasauki kawai. Muwuce, Jakadiya tace to bari inma Ayman magana seta dawo nan tazauna kada tafarka. Waziri yace rankaidade muje gaba daya muga jikinshi semu wuce.
Areef da Haisam suna cikin tsara yanda zasu hada plan, Ayman tana gefe duk tashiga damuwa se kallon Haisam takeyi tana tunanin idan aka rabasu bazata iya. Hakura dashi ba. Turo kofar da akayi ne. Tasa su saurin kallon kofa, Areef suna hada ido da sarki yayi saurin komawa ya kwanta tare da rufe ido.
Dariya yakusa bama Sarki, bayan sun shigo Sarki ya matsa kusa dashi yace lallai yarona kai ragone tunda har zaka iya kwanciya asibiti saboda mace, to danazo ince maka na amince da zabinka amma tunda naga baka warke ba, nafasa, ai dasauri yamike yariko hannun Sarki yana fadin wlh nawarke koyanzu ma asallameni. Gaba daya dakin seda suka sa dariya, hada Ayman me kuka. Sarki yace ka kwantar da hankalinka babu wanda ze hanaka auren zabinka, kuma jininka, bari muje gida mudawo, kallon Haisam yayi yace ka kula dasu, ke kuma me kukan soyayya sekiyi shiru tunda zaki samu abinda kikeso, kitashi kije gurin Diyata kizauna zamu dawo yanzun nan. Juyawa yayi yafita suma suka bisu abaya.
Cike da Mamaki Areef ya kalli Haisam yace Jinina, kuma diyar Abba? Tome yake nufi? Kafada Haisam yadaga alamun shima besani ba, yace mujira sudawo maji daga garesu.
Jakadiya Karima se kuka take tana fadin tsakanina da Gimbiya Zakiyya Allah ya isa, muguwar mata tasamu cikin bala,i kuma gashi yanzu mune akulle, bamuda wata sheda dazata nunama mutane tanada hannnu acikin abinda muka aikata. Kaicona ni Karima, ban rike amanar da mutanan nan suka bani ba, naci amanarsu, nima kuwa Allah baze barni ba. Yanzu shikenan haka za,a yanke mana hukunci muna kallo abar Gimbiya?.
Wata irin dariya Sarkin fada yayi yace kidena bata hawayenki abanza, waye yace maki itama zata kubuta? Aini bana barin baya da kura, inde zanyi aiki to dole se nasamu madafa nake farashi, ko anfada maki nima irin kwakwalwar jinin sarauta nakeda ita wadda bata da seti? Kawai malama kizuba ido kisha kallo gobe.
Suna zuwa gidan afalo sukaci karo da ita tafito se raba idanu takeyi. Cak Sarki ya tsaya yazuba mata ido, tabbas ita ce, sede tarame, hannu yadaga sama yanama Allah godiya, Waziri yace Jakadiya kamota muwuce. Hannunta takama suka nufi waje.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 95⚜100
Da sallama suka shiga falon Sarki Hasheem, yana zaune abisa kekenshi yana sana,ar tashi wato tunanin Fulaninshi, matsawa kusa dashi Sarki Qaseem yayi.
Kafadarshi ya dafa ahankali yadago yana kallonshi, wasu siraran hawaye suka fito daga idanunsu su duka biyun, alamu Sarki Hasheem yayi mashi da lafiya? Murmushi yayi mashi yakama kekenshi yafara turawa.