Sashe 19
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kara kiran sunan yayi, ganin bazata dagoba yace haba Angel, ko rowar fuskar ake mani? Wlh bazan boye maki ba, tun lokacin danayi ido biyu dake, kika tafi da zuciyata, Allah yasa babu kowa ataki zuciyar kamar yanda tawa take empty? Wani dadi ne yaziyarci zuciyarta jin abinda yafada.
Angel kode in hakura akwai wani dan uwanki kuma dan kasarku wanda yarigani. Batasan lokacin datace a,a ba, dariya yayi yace kina nufin nasamu karbuwa kenan? Kai tadaga, wani sanyi yaji aranshi, hannu yamika mata yace tobani wayarki insa maki number ta.
Yana cikin sawa Areef yadawo hannunshi dauke da manyan ledoji guda 2, yace kai wlh nagaji zantafi kuma sede kunemi mota. Haisam yace ai mungama harna kashe boss. Dariya yayi yace ainasan dama bazaka sha wahala ba. Ayman cikin hausarta wadda bata goge ba, tace Yaya tsaraba kasiyomun?.
Dariya yayi yace haba Ayman ai yanzu kinfita daga hannuna, nima iyalina nasiya mawa. Turo baki tayi tace kai Yaya yaushe kayi aure? Yace keyanzu aure kikayi dana ganki kina fira? Murmushi tayi tare da saddar da kanta. Haisam yace Angel tashi muje kizabi abinda kike so, Areef yace oho de, aide seda nayi sannan kuma kuyi sauri.
Jikin Sarki Hasheem yafara sauki sosai, dan yanzu yafara motsa hannunshi da kafarshi dasuka dena amfani ada, bakaramin dadi Waziri da Sarki Qaseem sukaji ba, sede haryanzu befara magana ba, kuma akullum tare suke fita dashi fada, sede idan yana bacci.
Acikin matanshi babu wadda take zuwa gurinshi da sunan wani abu, tsakinsu dashi sede su shiga su duba jikinshi, amma ko abinci Waziri ko Sarki Qaseem suke bashi.
Gimbiya Suhailat ce, zaune tare da Sarki, kallonshi tayi tace kasan hubby Ayman da Yarima sunfita yawo, bakaga lokacin daya ganta ba, yanda yake fara,a, itama haka, wlh bakaji yanda naji dadi ba. Sarki yace lallai munkusa shan biki agidan nan, sede inaso abari har yaya yakara samun sauki sannan. Tace hakan ma yayi, Allah yakara mashi lafiya, yace amin.
Suna dawowa, suka nufi gidan jakadiya Safeeya, sede Areef yace ma Haisam sujirashi yashiga yayi magana da Aunty, kade gane menake nufi? Haisam yace hakane gskiya jeka bari muzauna alambu.
Bayan sun gaisa yayi mata bayanin abinda yake tafe dashi. Wani irin dadi ne, yashiga zuciyarta, sede bata fada mashi dalilin zuwan Ayman ba,kallonshi tayi tace gskiya naji dadin wannan maganar kuma Haisam mutumin kirki ne, nasan ko kanwarka yanuna yana so zaka bashi, dan kafi kowa sanin halinshi, amma akwai wani abu guda danakeso infada maku daga kai har Ayman.
Kada ku kuskura kubari Gimbiya ko Sarki wani yasan tarayyarsu da Haisam, kasan dalilin dayasa nafada maka haka? Saboda kasan ra,ayin iyayenka akan sarauta, kubar abin aranku, nan da wani lokaci komai zeyi dede, kaima alokacin zanyi masu maganar Yar Baba, kaga se ahada datasu Ayman, kaje kakirawosu, bakomai nasan idan nace ma Ayman kada tafadama kowa Yar Baba tana gida bazata fada ba. Areef yace Aunty kamar akwai wani abu dakike boyemun dan Allah kifadamun, kinsan halina babu wanda zan fada mawa.
Kai tagirgiza tace babu abinda nake boye maka, kaide inaso kayi biyayya da duk wata magana dazan fada maka, nafika sanin masarautar nan, dan haka kabi abinda nafada maka, kasan bazan taba cutar da kai ba. Kirawosu inyimasu jawabin dana maka, inaso inshiga cikin gida. Waya yadauka yakira Haisam yace su shigo.
Bayan sun gaisa Jakadiya Safeeya tayi masu irin bayanin datayi ma Areef, kallon Ayman tayi tace inafatan kingane abinda nake nufi? Idan har kunaso burinku yacika to kubi abinda nafada, bance soyayyarku akwai matsala ba, sede kuyi hakuri na wani lokaci zaku gane abinda nake nufi. Ayman tace mungode Aunty kuma bazan fadama kowa ba. Tace naji dadin haka, bari inshiga cikin gida. Yar Baba tana shiryawa ne. Kasan mutuniyar ko bacci zatayi setayi kwalliya.
Areef yace ai haka akeso Aunty, wai niko Aunty Beauty bata iya rubutu ba, inaganin kamar tunda tanaji ai zamu iya fira ta waya, muna rubutu ko kuma ta takarda. Shiru tayi kafin tace , kasan tunda tagirma aka gane bataji, shiyasa ba,a sata makaranta ba, amma karatun addini tasan abubuwa da dama kuma Allah yabata wata baiwa tasaurin fahimtar abu, kome aka koya mata cikin lokaci kadan zata daukeshi, har mamakin kokarinta nakeyi, ni kaina danayi boko da hada rubutu zan rika koya mata.
Haisam yace, abu me sauki kenan, ina ganin Areef kafara koya mata rubutu, ahankali sekurika shiga cikin karatun boko, kuma nan gaba za,a iya daukar mata me lesson. Areef yace hakane, tunda tana saurin fahimta, insha Allahu setayi karatu, Allah yayi mana jagora, Aunty kirata, se mubar mata Ayman muje muyi sallar magrib.
Bayan tafito, tazauna kusa da Ayman, tana ta murmushi, Ayman ma murmushi tayi tare da jawo hannunta, ai kamar jira take tadora kanta saman kafadar Ayman, dariya duka suka saka, jakadiya Safeeya tace naga ranar da zaki dena son jiki kekam, daga ganin mutane, baki santa ba amma kin hayeta. Daga ta tayi tana murmushi, Ayman takara jawota tace Aunty kibarta, kinga dama bani da kanwa yanzu nasamu, kwantawa tayi saman cinyarta tana murmushi.
Haisam yace tashi muje masallaci kada Abba yace beganmu ba, Jakadiya tafita tace sekun dawo, akwai abinci akitchen idan kundawo, suka ce to. Areef yaduka kusa da beauty yace wato yau kinga yar uwa shine ko ki kalleni ko? Kai tagirgiza ta tashi ta kalleshi. Dariya Haisam yayi yace beauty bakida matsala, kome akace kiyi sekiyi, gaskiya nan gaba zankoya maki bakomai zaki rika yiba. Duka Areef yakaimashi yana fadin todan bukulu, ai seka hanata, Allah yakashe yabani idan munyi aure base narika magiya ba shine zakace wani tadena. Haisam yace sosai ma, har wannan son jikin duk sena hanata. Dariya Areef yayi yanufi hanayar fita yace tunda kaine mijin ai se ingani, aini naji dadin wannan abu, sonjiki. Ai shine abinso, fita sukayi suna dariya.
Ayman tace sister da kikayi wanka kinyi alwala ko? Kai tadaga mata, tace yauwa tashi muje kiyi sallah nima inyi alwala inyi, hannunta takama suka nufin daki.
Sarkin fada ne tsaye abakin kofar Gimbiya Zakiyyah se waige waige yakeyi kamar marar gaskiya, wani abu yadauko aleda yasa a idonshi, kafin yashiga gidan, alokacin tagama sallah tafito falo, da sallama yashiga, cike da mamaki tace kai? Waya baka ikon shigowa part dina? Ko kuma wani yace maka ina nemanka? Kai yadago suka hada ido, wani irin abu taji ya tsikareta, saurin rufe ido tayi, ganin halin data shiga yasa yayi murmushi aranshi yace anzo gurin. Kallonta yayi yace nadauka ai kinason ganina shiyasa nazo amma bari inkoma.
Saurin bude ido tayi tasaki murmushi tace ni na isa nace ka koma? Shigo sannu da zuwa, zama yayi abisa kujera, tace a,a muje daga ciki kada wasu suganka. Murmushi yayi yatashi yana lashe baki aranshi yana fadin wayyo ni. Daki suka shiga tace meza,a kawo maka? Murmushi yayi yace bakomai zoki zauna kawai fira nazo muyi, wani irin yanayi taji tashiga, tahowa tayi kusa dashi tana wani girgiza, kusa dashi tazauna tace togani, kallonta yayi yakamo hannunta yace babu wanda zeshigo ko? Lumshe idanu tayi alokacin taji wani bakon yanayi yashigeta, tace ina zuwa bari inbada sako akulle mun gidan kuma kada abar kowa yashigo, yace akulle gida nida ba nan zan kwana ba, wani irin kallo tayi mashi tace, kama isa, ai tunda kashigo sede da asuba kafita. Dariya yayi yace duk abinda kika fada dede ne rankiyadade, murmushi tayi tafita. Wani irin tsalle yayi na farin ciki, hannunshi yasa a aljihu yaciro wani abu aranshi yana fadin saboda tsaro.
Bayan sundawo daga sallah part din Jakadiya Safeeya suka wuce, anan suka samesu afalo beauty tana kwance kan cinyar Ayman ita kuma tana ta wasa da gashinta tana bata labari, da sallama suka shiga, Haisam yace to wlh baze yuwu ba, wannan matar taka zata sama Angel dina taurin cinya, Areef yace wlh kai dan iska ne, agaban beauty kake wannan maganar sokake ka kangararmun da ita, bacin kasan yarinya ce. Ai dasauri beauty ta tashi jin abinda Areef yafada, kafafuwa tafara durzawa akasa tana turo baki tana kunkunai.
Dariya Ayman da Haisam sukayi, Ayman tajawota tace yi hakuri, shine yace maki yarinya ko? Kai tadaga tana kara turo baki, kamar zatayi kuka, ai ganin haka yasa Areef ya matso yaduka kasa kusa da ita yana fadin yihakuri beauty na wasa nakeyi kinji? Kai ta daga tana murmushi, Areef yace yauwa beauty na, tashi muci abinci in baki tsara barki. Tashi tayi tanufi kitchen.
Haisam yace gsky kaci sa,ar mata wannan saurin sauka haka, to wlh kaji tsoron Allah, Areef yace da tsoronka nakeji? Sarkin sa ido kawai, kuma badakai zanci abinci ba, nida beauty zanci. Haisam yace Allah nagode maka nima daka hadani da abin sona ayau, nadana shiga 3 agurinka, Angel muma tare zamuci ko? Kai tadaga tana murmushi, lokacin da beauty tafito tasan alokacin ake bama mamanta abinci, harta nufi dakinta se kuma ta tuna da maganar Jakadiya Safeeya,,,,,,,, kada kisake kishiga dakin can idan akwai mutane agidan nan, idan ba haka ba, kamata zasuyi bazaki kara ganinta ba. Maganar Areef ce tadawo da ita, beauty mezakiyi awannan dakin kuma?
Juyowa tayi tana murmushi ta girgiza kai, tanufo gurinsu, ansar abincin yayi ta koma tadauko sauran, atare yazuba masu yamika ma Haisam yace ganaku nan, dariya yayi yajawo yazuba masu, Areef yace taho beauty na muci, zama tayi kusa dashi, sede bega ta jingina dashi ba, murmushi yayi aranshi yace su beauty anfara girma kenan, abaki yafara bata tanaci, shima yace nima bani zakiyi ko? Kai tadaga tana murmushi, haka sukarika cin abincinsu sun manta dawasu Su Haisam.
Dariya Jakadiya Safeeya tayi jin abinda Gimbiya Suhailat tafada, tace ai sundawo tundazu suna gidana, acan nabarsu suna cin abinci ma. Wani murmushin jin dadi Gimbiya tayi tace ai nasan Yarima zeso Ayman, gashi lokaci guda har sun saba, wato kunyata sukeji shiyasa suka tafi can. Jakadiya tace emana agida na za,ayi firar ai, kinsan Yarima. Naguri nane, ai, gimbiya tace aise suyita ta tafiya nima haka nakeso, Allah yabama Yaya lafiya musha biki. Kallon agogo Jakadiya tayi tace bari inje gida seda safe Gimbiya.
Angel kode in hakura akwai wani dan uwanki kuma dan kasarku wanda yarigani. Batasan lokacin datace a,a ba, dariya yayi yace kina nufin nasamu karbuwa kenan? Kai tadaga, wani sanyi yaji aranshi, hannu yamika mata yace tobani wayarki insa maki number ta.
Yana cikin sawa Areef yadawo hannunshi dauke da manyan ledoji guda 2, yace kai wlh nagaji zantafi kuma sede kunemi mota. Haisam yace ai mungama harna kashe boss. Dariya yayi yace ainasan dama bazaka sha wahala ba. Ayman cikin hausarta wadda bata goge ba, tace Yaya tsaraba kasiyomun?.
Dariya yayi yace haba Ayman ai yanzu kinfita daga hannuna, nima iyalina nasiya mawa. Turo baki tayi tace kai Yaya yaushe kayi aure? Yace keyanzu aure kikayi dana ganki kina fira? Murmushi tayi tare da saddar da kanta. Haisam yace Angel tashi muje kizabi abinda kike so, Areef yace oho de, aide seda nayi sannan kuma kuyi sauri.
Jikin Sarki Hasheem yafara sauki sosai, dan yanzu yafara motsa hannunshi da kafarshi dasuka dena amfani ada, bakaramin dadi Waziri da Sarki Qaseem sukaji ba, sede haryanzu befara magana ba, kuma akullum tare suke fita dashi fada, sede idan yana bacci.
Acikin matanshi babu wadda take zuwa gurinshi da sunan wani abu, tsakinsu dashi sede su shiga su duba jikinshi, amma ko abinci Waziri ko Sarki Qaseem suke bashi.
Gimbiya Suhailat ce, zaune tare da Sarki, kallonshi tayi tace kasan hubby Ayman da Yarima sunfita yawo, bakaga lokacin daya ganta ba, yanda yake fara,a, itama haka, wlh bakaji yanda naji dadi ba. Sarki yace lallai munkusa shan biki agidan nan, sede inaso abari har yaya yakara samun sauki sannan. Tace hakan ma yayi, Allah yakara mashi lafiya, yace amin.
Suna dawowa, suka nufi gidan jakadiya Safeeya, sede Areef yace ma Haisam sujirashi yashiga yayi magana da Aunty, kade gane menake nufi? Haisam yace hakane gskiya jeka bari muzauna alambu.
Bayan sun gaisa yayi mata bayanin abinda yake tafe dashi. Wani irin dadi ne, yashiga zuciyarta, sede bata fada mashi dalilin zuwan Ayman ba,kallonshi tayi tace gskiya naji dadin wannan maganar kuma Haisam mutumin kirki ne, nasan ko kanwarka yanuna yana so zaka bashi, dan kafi kowa sanin halinshi, amma akwai wani abu guda danakeso infada maku daga kai har Ayman.
Kada ku kuskura kubari Gimbiya ko Sarki wani yasan tarayyarsu da Haisam, kasan dalilin dayasa nafada maka haka? Saboda kasan ra,ayin iyayenka akan sarauta, kubar abin aranku, nan da wani lokaci komai zeyi dede, kaima alokacin zanyi masu maganar Yar Baba, kaga se ahada datasu Ayman, kaje kakirawosu, bakomai nasan idan nace ma Ayman kada tafadama kowa Yar Baba tana gida bazata fada ba. Areef yace Aunty kamar akwai wani abu dakike boyemun dan Allah kifadamun, kinsan halina babu wanda zan fada mawa.
Kai tagirgiza tace babu abinda nake boye maka, kaide inaso kayi biyayya da duk wata magana dazan fada maka, nafika sanin masarautar nan, dan haka kabi abinda nafada maka, kasan bazan taba cutar da kai ba. Kirawosu inyimasu jawabin dana maka, inaso inshiga cikin gida. Waya yadauka yakira Haisam yace su shigo.
Bayan sun gaisa Jakadiya Safeeya tayi masu irin bayanin datayi ma Areef, kallon Ayman tayi tace inafatan kingane abinda nake nufi? Idan har kunaso burinku yacika to kubi abinda nafada, bance soyayyarku akwai matsala ba, sede kuyi hakuri na wani lokaci zaku gane abinda nake nufi. Ayman tace mungode Aunty kuma bazan fadama kowa ba. Tace naji dadin haka, bari inshiga cikin gida. Yar Baba tana shiryawa ne. Kasan mutuniyar ko bacci zatayi setayi kwalliya.
Areef yace ai haka akeso Aunty, wai niko Aunty Beauty bata iya rubutu ba, inaganin kamar tunda tanaji ai zamu iya fira ta waya, muna rubutu ko kuma ta takarda. Shiru tayi kafin tace , kasan tunda tagirma aka gane bataji, shiyasa ba,a sata makaranta ba, amma karatun addini tasan abubuwa da dama kuma Allah yabata wata baiwa tasaurin fahimtar abu, kome aka koya mata cikin lokaci kadan zata daukeshi, har mamakin kokarinta nakeyi, ni kaina danayi boko da hada rubutu zan rika koya mata.
Haisam yace, abu me sauki kenan, ina ganin Areef kafara koya mata rubutu, ahankali sekurika shiga cikin karatun boko, kuma nan gaba za,a iya daukar mata me lesson. Areef yace hakane, tunda tana saurin fahimta, insha Allahu setayi karatu, Allah yayi mana jagora, Aunty kirata, se mubar mata Ayman muje muyi sallar magrib.
Bayan tafito, tazauna kusa da Ayman, tana ta murmushi, Ayman ma murmushi tayi tare da jawo hannunta, ai kamar jira take tadora kanta saman kafadar Ayman, dariya duka suka saka, jakadiya Safeeya tace naga ranar da zaki dena son jiki kekam, daga ganin mutane, baki santa ba amma kin hayeta. Daga ta tayi tana murmushi, Ayman takara jawota tace Aunty kibarta, kinga dama bani da kanwa yanzu nasamu, kwantawa tayi saman cinyarta tana murmushi.
Haisam yace tashi muje masallaci kada Abba yace beganmu ba, Jakadiya tafita tace sekun dawo, akwai abinci akitchen idan kundawo, suka ce to. Areef yaduka kusa da beauty yace wato yau kinga yar uwa shine ko ki kalleni ko? Kai tagirgiza ta tashi ta kalleshi. Dariya Haisam yayi yace beauty bakida matsala, kome akace kiyi sekiyi, gaskiya nan gaba zankoya maki bakomai zaki rika yiba. Duka Areef yakaimashi yana fadin todan bukulu, ai seka hanata, Allah yakashe yabani idan munyi aure base narika magiya ba shine zakace wani tadena. Haisam yace sosai ma, har wannan son jikin duk sena hanata. Dariya Areef yayi yanufi hanayar fita yace tunda kaine mijin ai se ingani, aini naji dadin wannan abu, sonjiki. Ai shine abinso, fita sukayi suna dariya.
Ayman tace sister da kikayi wanka kinyi alwala ko? Kai tadaga mata, tace yauwa tashi muje kiyi sallah nima inyi alwala inyi, hannunta takama suka nufin daki.
Sarkin fada ne tsaye abakin kofar Gimbiya Zakiyyah se waige waige yakeyi kamar marar gaskiya, wani abu yadauko aleda yasa a idonshi, kafin yashiga gidan, alokacin tagama sallah tafito falo, da sallama yashiga, cike da mamaki tace kai? Waya baka ikon shigowa part dina? Ko kuma wani yace maka ina nemanka? Kai yadago suka hada ido, wani irin abu taji ya tsikareta, saurin rufe ido tayi, ganin halin data shiga yasa yayi murmushi aranshi yace anzo gurin. Kallonta yayi yace nadauka ai kinason ganina shiyasa nazo amma bari inkoma.
Saurin bude ido tayi tasaki murmushi tace ni na isa nace ka koma? Shigo sannu da zuwa, zama yayi abisa kujera, tace a,a muje daga ciki kada wasu suganka. Murmushi yayi yatashi yana lashe baki aranshi yana fadin wayyo ni. Daki suka shiga tace meza,a kawo maka? Murmushi yayi yace bakomai zoki zauna kawai fira nazo muyi, wani irin yanayi taji tashiga, tahowa tayi kusa dashi tana wani girgiza, kusa dashi tazauna tace togani, kallonta yayi yakamo hannunta yace babu wanda zeshigo ko? Lumshe idanu tayi alokacin taji wani bakon yanayi yashigeta, tace ina zuwa bari inbada sako akulle mun gidan kuma kada abar kowa yashigo, yace akulle gida nida ba nan zan kwana ba, wani irin kallo tayi mashi tace, kama isa, ai tunda kashigo sede da asuba kafita. Dariya yayi yace duk abinda kika fada dede ne rankiyadade, murmushi tayi tafita. Wani irin tsalle yayi na farin ciki, hannunshi yasa a aljihu yaciro wani abu aranshi yana fadin saboda tsaro.
Bayan sundawo daga sallah part din Jakadiya Safeeya suka wuce, anan suka samesu afalo beauty tana kwance kan cinyar Ayman ita kuma tana ta wasa da gashinta tana bata labari, da sallama suka shiga, Haisam yace to wlh baze yuwu ba, wannan matar taka zata sama Angel dina taurin cinya, Areef yace wlh kai dan iska ne, agaban beauty kake wannan maganar sokake ka kangararmun da ita, bacin kasan yarinya ce. Ai dasauri beauty ta tashi jin abinda Areef yafada, kafafuwa tafara durzawa akasa tana turo baki tana kunkunai.
Dariya Ayman da Haisam sukayi, Ayman tajawota tace yi hakuri, shine yace maki yarinya ko? Kai tadaga tana kara turo baki, kamar zatayi kuka, ai ganin haka yasa Areef ya matso yaduka kasa kusa da ita yana fadin yihakuri beauty na wasa nakeyi kinji? Kai ta daga tana murmushi, Areef yace yauwa beauty na, tashi muci abinci in baki tsara barki. Tashi tayi tanufi kitchen.
Haisam yace gsky kaci sa,ar mata wannan saurin sauka haka, to wlh kaji tsoron Allah, Areef yace da tsoronka nakeji? Sarkin sa ido kawai, kuma badakai zanci abinci ba, nida beauty zanci. Haisam yace Allah nagode maka nima daka hadani da abin sona ayau, nadana shiga 3 agurinka, Angel muma tare zamuci ko? Kai tadaga tana murmushi, lokacin da beauty tafito tasan alokacin ake bama mamanta abinci, harta nufi dakinta se kuma ta tuna da maganar Jakadiya Safeeya,,,,,,,, kada kisake kishiga dakin can idan akwai mutane agidan nan, idan ba haka ba, kamata zasuyi bazaki kara ganinta ba. Maganar Areef ce tadawo da ita, beauty mezakiyi awannan dakin kuma?
Juyowa tayi tana murmushi ta girgiza kai, tanufo gurinsu, ansar abincin yayi ta koma tadauko sauran, atare yazuba masu yamika ma Haisam yace ganaku nan, dariya yayi yajawo yazuba masu, Areef yace taho beauty na muci, zama tayi kusa dashi, sede bega ta jingina dashi ba, murmushi yayi aranshi yace su beauty anfara girma kenan, abaki yafara bata tanaci, shima yace nima bani zakiyi ko? Kai tadaga tana murmushi, haka sukarika cin abincinsu sun manta dawasu Su Haisam.
Dariya Jakadiya Safeeya tayi jin abinda Gimbiya Suhailat tafada, tace ai sundawo tundazu suna gidana, acan nabarsu suna cin abinci ma. Wani murmushin jin dadi Gimbiya tayi tace ai nasan Yarima zeso Ayman, gashi lokaci guda har sun saba, wato kunyata sukeji shiyasa suka tafi can. Jakadiya tace emana agida na za,ayi firar ai, kinsan Yarima. Naguri nane, ai, gimbiya tace aise suyita ta tafiya nima haka nakeso, Allah yabama Yaya lafiya musha biki. Kallon agogo Jakadiya tayi tace bari inje gida seda safe Gimbiya.