Sashe 5
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yarima yace Momy niduk lokacin damuka hadu da Sarkin Fada kawai se inji raina yana baci, kawai nide mutumin be kwantamun arai ba, ganinshi nake da siffar munafukai. Momy tace Allah sarki, kaine kake ganinshi haka, amma aduk cikin fadar Sarki ai inaji babu wanda yake maka son da sarkin Fada yake maka tun kana yaro, kama cire wannan abun daga ranka kawai shedanne yake maka wasiwasi azuciyarka. Shiru Areef yayi amma sam zuciyarshi bata yarda da abinda tafada ba.
Bayan sungama shafa mashi maganin ajikinshi bacci yadaukeshi, kamashi sukayi suka kwantar dashi bisa gadonshi suka rufo mashi kofar, Sarki yace insha Allahu Allah yakusa kawo mana karshen wannan halin da muke ciki. Waziri yace da alama wannan maganin zeyi aiki ajikinshi dan tunda naga yasha naga wasu alamu. Sarki yace Allah yasa, suna fita sukaci karo da Jakadiya, kara gaishesu tayi, Sarki ya kalleta yadauke kai, Waziri yace zaki iya tafiya dan me martaba baya bukatar wani abu, kuma ma yasamu bacci, Jakadiya tace to ai shikenan Allah yabashi lafiya, juyawa tayi ta tafi tana me hararar Waziri tagefe.
Da Sallama tashiga falon Gimbiya ita kadai tasamu se bayin dasuke mata hidima, zama tayi tana fadin Allah yatemakeki, Allah yasa kifi haka, murmushi tayi tadaga mata hannu, Jakadiya ta kalli sauran bayin dasuke falon, lokaci guda sukayi hanyar waje.
Gimbiya tace da alama akwai magana abakinki? Tace kwarai ma kuwa Gimbiya, waigawa tayi tace amma rankishidade banga Gimbiya karama ba, ko lafiya? Yamutse fuska tayi tace oho kinsanta da nawa yanzu haka tana can tana shiryawa kinsan yau ita zata karbeni. Gyara zama Jakadiya tayi tace ai me martaba ma yasamu bacci, kuma da alama ya karbi maganin dasuka bashi, dasauri Gimbiya ta tashi zaune, tace haba Jakadiya wane irin labari ne marar dadinji kike fadamun haka?
Allah yahuci ranki Gimbiya 'Yar Babbar Gida, kaina bisa wuya, banga amfanina aduniya ba idan har nazamo daya daga cikin masu bata maki rai, agafarceni Gimbiyar Sarki mace daya tamkar da dubu, kedayace me haske agurin me martaba, duk sauran matanshi bayinki ne Gimbiya me mulki gaba da baya. Wani kayataccen murmushi Gimbiya tasaki, ahankali tace inajinki menene shawara?
Nagode Gimbiya, amma aganina meze hana mubi shawarar dana fara kawowa daga farko inaganin ita kadaice hanyar dazata bulle mana, dan mutanen nan suntashi tsaye akan wannan al'amari inajin tsoron abinda zedawo. Maganar Gimbiya medaki sukaji tana fadin wannan shawara taki Jakadiya tayi dede, amma ina ganin kamar haryanzu Yaya batayi na'am da ita ba.
Zama tayi tare da daukar apple tafaraci. Jakadiya tace Allah yatemakeke Gimbiya, barka da fitowa, hannu tadaga mata tamaida kallonta gurin Gimbiya tace Yaya dan Allah wannan karin kada kice zaki ki karbar shawararmu, wlh ayanzu kissa da tuggu basuci kawai mubama Jakadiya dama kamar yanda tanema daga farko.
Wani kallo Gimbiya tabita dashi, sannan tace wai meyasa kuka kasa fahimtata, koda yake ba laifinku bane daga ke har ita babu wanda yakeda jinin sarauta ajikinshi. Tashi tayi ranta abace tashige daki, da kallo Gimbiya medaki tabita, Jakadiya ko cikin sauri tabi bayanta jiki na bari. Karamin tsaki Gimbiya medaki taja ta tashi itama tabi bayan Jakadiya tana Allah wadai da wannan kaskancin datasa kanta ake mata.
Washe gari bayan sunje asibiti likitoci suka taru akanta, anyi mata gwaje gwaje kala kala, bayan sungama likitan yakira malam office, seda yayi rubutunshi sannan yakalli malam yace, agsky munyi duk wani bincikenmu kuma sakamako daya yake bamu, wannan mata lalurarta acikin kanta take, kuma mtsalace mesauki, sede kafin asamu abinda zedawo maka da hankalinka shine aiki, abinciken damukayi mungano cewar buguwa tasamu akanta, komade hadari ne, ko kuma akwai abinda yabugar mata kai, wanda shiyayi sanadiyar haukacewarta.
Amma abu mafi sauki shine duk ranar data kara samun makamancin abinda yafaru da ita, kota bige ko kuma ace arika nuna mata abubuwan datayi tarayya dasu kafin tasamu matsalar to zata iya dawowa hankalinta. Dan haka yanzu gida zaku koma da ita, akwai magungunan dana rubuta sekuyi mata amfani dasu. Godiya malam yayi mashi yakarbi takardar maganin yafita.
Koda sukaje gida ajikin Jakadiya Yar Baba takwanta hartayi bacci, dan yanzu tafara sakin jikinta, sede daga Jakadiya bata yarda da kowa agidan se ita. Adaren ranar bayan sallar isha'i malam yakara tarasu, hada Baba dan yaje yadauko iyalanshi yazo anan malam yabashi daya daga cikin gidajenshi suka sauka aciki kuma yasa aka zuba mashi kayan abinci dana amfani.
Malam yace to Baba kajide abinda likita yace agame da ciwon wannan mata ko? Dan haka nayanke shawarar za'a bama Jakadiya su ta tafi dasu can masarautar datake, dan Sarki mutumina ne, dazu munyi waya da waziri, kuma nafada mashi komai sede banfada mashi tarihinsu ba, kuma Baba wannan tafiya hada kai za'ayita, acan zaka samu aikin dazakayi idan yaso daga baya idan komai yadedeta zaka iya zuwa kadauki iyalinka.
Sede Baba banaso kafadama kowa labarinsu, kasan mutane akwai son zuciya nafiso kabarshi atsakaninmu wata rana zasuji labarinsu, kuma abangaren Jakadiya Waziri yace zasu zauna, kasan kuwa bangarenta yana daga bayan lambun gidan, bakowane yake zuwa ba, sede kai tunda sunsan kowaye kai zaka iya zuwa aduk lokacin dakakeso. Allah yabaka ikon rike sirrinku, sekayi ahankali da gidan sarauta, ba,a aboki agidan, kowa da halinshi yake zaune, dan haka kazama cikin shiri gobe insha Allahu zakutafi da safe. Allah yakareku daga dukkan sharri.
Baba yace amin, kuma naji dadin abinda kamun, ga iyalai na nan, nasan zaka kulamun dasu Allah yabaka ikon zama dasu lafiya, amma taya zamurika magana da kai? Murmushi malam yayi yace kada kasamu damuwa akwai waya ahannun Jakadiya, kuma iyalanka zasu zauna cikin kwanciyar hnkl, fatana Allah yabaku sa'a. Haka kowa yatashi Jakadiya tanacike da murna, harta tashi yace Jakadiya kisameni adaki, Bayan sun shiga naji malam yafara magana, akwai abubuwa da dama da zuciyata take sakamun akan wannan matar, shiyasa ma nace zakutafi tare. Kara rage murya yayi yana mata bayani,akan yanda yakeson abubuwan sutafi, sede duk yanda naso inji abinda suke fada ya gagara, haka nadawo inajiransu sufito, sundauki kusan awa daya suna tattaunawa sannan tafito.
Washe gari dasafe Malam yabada mota akadaukesu suka nufi babbar masarautar Gombe.
To jama,a bara muji menene asalin labarin wannan masarauta.
Tuna baya,
Asalin Labarin.
MASARAUTAR BUBAYARO.
Muhadu a page nagaba.
Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 30⚜35
Qaseem yayi saurin fadin haba Yaya kasan mekake fada kuwa? Sarki yace koma menene Qaseem nasan baze wuce tace in....... kara kamo rigarshi datayi ne yasashi yin shiru yamai da hankalinshi gareta. Bawan Allah ga 'Yata nan, ita kadai Allah yabani, mahaifinta yarasu nikadai narage mata, kuma nima gashi Allah zerabata dani. Daga cikin wancan kauyen muka fito, mutanen garin suka koromu sbd kawai wani yayi ma mahaifinta kazafi, sakamakon hakan ciwon zuciya yayi ajalinshi.
Mu kuma suka koromu komai basu bari mundauka ba. Inarokonka kobayan babu raina kada kabari Nafeesa takoma garinmu, kamar yanda kamun alkawari inason rayuwar Nafeesa tayi albarka dan Allah kadaure ka auri Nafeesa.
Qaseem cike da bacin rai yace dalla malama kifadi abu meyuwuwa kinko san dawanda kike magana? Idan baki sani ba, to........ tarin daya taso matane yasashi yinshiru suka maida hankalinsu kanta bakaramin shiga tashin hankali Sarki yashiga ba, ganin tana wani irin aman jini, Nafeesa ko se kuka takeyi, Sarki yatashi yace ma Waziri adauketa ko akan doki ne, mutafi da ita asibitin cikin gari.
Wani bafade Waziri yasa yadaukota, Haka Nafeesa ta tashi tana kuka. Cak bafaden daya dauketa ya tsaya jin jikinta yakara nauyi, Waziri yace muje mana katsaya kana bata lokaci, Ranka yadade ade zo aduba wannan baiwar Allah naji jikinta yasaki, dasauri Sarki yadawo dabaya, suna zuwa Waziri yataba hannunta yaji yadawo, yasa hannunshi gurin hancinta yaji ba numfashi, sam yamanta da diyarta agurin yace Rankai dade inaji fa ta mutu. Wani kara da Nafeesa tasaka nan take tafadi kasa sumammiya. Sarki cike da damuwa yasa Fadawa suka dauketa da mahaifiyarta aka dorasu akan doki aka nufi gida dasu, Qaseem kanshi jikinshi yayi sanyi yatausaya ma Nafeesa sosai.
Ko kafin sukai gida maman Nafeesa harta saki, dan akwai dan tafiya, suna zuwa sarki yasa aka kira Jakadiya nan Waziri yayi mata bayanin komai aka shiga da gawar cikin gida. Ita kuma Nafeesa aka kira likitansu domin yadubata.
Babu bata lokaci aka gama shiryata akayi mata sallah tasamu jama'a sosai, haka aka kaita gidanta na gaskiya, jikin Sarki yayi sanyi sosai dan yasan yariga da yadauki alkawarin da dole yacikashi. Bayan sundawo yakira Waziri dan suyi magana, bebi takan Qaseem ba, dan yasan baze bada goyon baya ba.
Sosai Waziri yakara karfafa mashi guiwa kuma yakara tunasar dashi muhimmanci alkawari, da kuma irin jihadin dazeyi, Waziri yace kobaka aureta ba, kasama mata miji acikin gidan nan ko awaje hankalinka baze taba kwanciya ba sbd bakasan irin rikon dazeyi mata ba. Sarki yace bakomai ai itama mutum ce, kamar kowa kuma yin hakan dazanyi baze ragemun wani abuba, sede Allah yasani atsarina banida ra'ayin auren macen da bata fito daga gidan sarauta ba, kuma wannan ra'ayi nane shiyasa Qaseem yakeda irin ra'ayin, segashi nashi haryafi nawa. Nasan zeji haushi na, amma dole incika alkawarin dana dauka dazaran Nafeesa tasamu sauki za adaura auren banason tashiga cikin damuwa. Allah yabani ladar abinda nayi.
Bakaramin tashin hankali Gimbiya Zakiyya tashiga ba da Jakadiya takawo mata maganar auren Sarki ba, duk da batason Jakadiya amma daga ranar tafara sakar mata fuska dan tasan zatayi mata amfani. Koda tafada ma mamanta shawara daya tabata, kada tasake tanuna bacin ranta akan auren, kogurin Sarki banyarda ki nuna bacin ranki ba. Da wannan shawarar Gimbiya tasamu sauki aranta. Koda Jakadiya taga tafara samun sakin fuska agurin Gimbiya seta kawo mata shawarar kozata kaita gurin bokanta.
Dawani kallo Gimbiya tabita, cike da bacin rai tace waiku meyasa bakuda tunani idan zakuyi magana. Ko anfada maki gidan sarauta gidan hauka ne? To kada kikara zomun da wannan maganar banzar. Jakadiya cike da ladabi tace Allah yahuci zuciyarki, kiyi hkr insha Allahu baza'a karaba, tace tashi kije idan kinsamo wata shawarar wadda tayi dede da tsarina zaki iya dawowa.
Wacece NAFEESA?
Bayan sungama shafa mashi maganin ajikinshi bacci yadaukeshi, kamashi sukayi suka kwantar dashi bisa gadonshi suka rufo mashi kofar, Sarki yace insha Allahu Allah yakusa kawo mana karshen wannan halin da muke ciki. Waziri yace da alama wannan maganin zeyi aiki ajikinshi dan tunda naga yasha naga wasu alamu. Sarki yace Allah yasa, suna fita sukaci karo da Jakadiya, kara gaishesu tayi, Sarki ya kalleta yadauke kai, Waziri yace zaki iya tafiya dan me martaba baya bukatar wani abu, kuma ma yasamu bacci, Jakadiya tace to ai shikenan Allah yabashi lafiya, juyawa tayi ta tafi tana me hararar Waziri tagefe.
Da Sallama tashiga falon Gimbiya ita kadai tasamu se bayin dasuke mata hidima, zama tayi tana fadin Allah yatemakeki, Allah yasa kifi haka, murmushi tayi tadaga mata hannu, Jakadiya ta kalli sauran bayin dasuke falon, lokaci guda sukayi hanyar waje.
Gimbiya tace da alama akwai magana abakinki? Tace kwarai ma kuwa Gimbiya, waigawa tayi tace amma rankishidade banga Gimbiya karama ba, ko lafiya? Yamutse fuska tayi tace oho kinsanta da nawa yanzu haka tana can tana shiryawa kinsan yau ita zata karbeni. Gyara zama Jakadiya tayi tace ai me martaba ma yasamu bacci, kuma da alama ya karbi maganin dasuka bashi, dasauri Gimbiya ta tashi zaune, tace haba Jakadiya wane irin labari ne marar dadinji kike fadamun haka?
Allah yahuci ranki Gimbiya 'Yar Babbar Gida, kaina bisa wuya, banga amfanina aduniya ba idan har nazamo daya daga cikin masu bata maki rai, agafarceni Gimbiyar Sarki mace daya tamkar da dubu, kedayace me haske agurin me martaba, duk sauran matanshi bayinki ne Gimbiya me mulki gaba da baya. Wani kayataccen murmushi Gimbiya tasaki, ahankali tace inajinki menene shawara?
Nagode Gimbiya, amma aganina meze hana mubi shawarar dana fara kawowa daga farko inaganin ita kadaice hanyar dazata bulle mana, dan mutanen nan suntashi tsaye akan wannan al'amari inajin tsoron abinda zedawo. Maganar Gimbiya medaki sukaji tana fadin wannan shawara taki Jakadiya tayi dede, amma ina ganin kamar haryanzu Yaya batayi na'am da ita ba.
Zama tayi tare da daukar apple tafaraci. Jakadiya tace Allah yatemakeke Gimbiya, barka da fitowa, hannu tadaga mata tamaida kallonta gurin Gimbiya tace Yaya dan Allah wannan karin kada kice zaki ki karbar shawararmu, wlh ayanzu kissa da tuggu basuci kawai mubama Jakadiya dama kamar yanda tanema daga farko.
Wani kallo Gimbiya tabita dashi, sannan tace wai meyasa kuka kasa fahimtata, koda yake ba laifinku bane daga ke har ita babu wanda yakeda jinin sarauta ajikinshi. Tashi tayi ranta abace tashige daki, da kallo Gimbiya medaki tabita, Jakadiya ko cikin sauri tabi bayanta jiki na bari. Karamin tsaki Gimbiya medaki taja ta tashi itama tabi bayan Jakadiya tana Allah wadai da wannan kaskancin datasa kanta ake mata.
Washe gari bayan sunje asibiti likitoci suka taru akanta, anyi mata gwaje gwaje kala kala, bayan sungama likitan yakira malam office, seda yayi rubutunshi sannan yakalli malam yace, agsky munyi duk wani bincikenmu kuma sakamako daya yake bamu, wannan mata lalurarta acikin kanta take, kuma mtsalace mesauki, sede kafin asamu abinda zedawo maka da hankalinka shine aiki, abinciken damukayi mungano cewar buguwa tasamu akanta, komade hadari ne, ko kuma akwai abinda yabugar mata kai, wanda shiyayi sanadiyar haukacewarta.
Amma abu mafi sauki shine duk ranar data kara samun makamancin abinda yafaru da ita, kota bige ko kuma ace arika nuna mata abubuwan datayi tarayya dasu kafin tasamu matsalar to zata iya dawowa hankalinta. Dan haka yanzu gida zaku koma da ita, akwai magungunan dana rubuta sekuyi mata amfani dasu. Godiya malam yayi mashi yakarbi takardar maganin yafita.
Koda sukaje gida ajikin Jakadiya Yar Baba takwanta hartayi bacci, dan yanzu tafara sakin jikinta, sede daga Jakadiya bata yarda da kowa agidan se ita. Adaren ranar bayan sallar isha'i malam yakara tarasu, hada Baba dan yaje yadauko iyalanshi yazo anan malam yabashi daya daga cikin gidajenshi suka sauka aciki kuma yasa aka zuba mashi kayan abinci dana amfani.
Malam yace to Baba kajide abinda likita yace agame da ciwon wannan mata ko? Dan haka nayanke shawarar za'a bama Jakadiya su ta tafi dasu can masarautar datake, dan Sarki mutumina ne, dazu munyi waya da waziri, kuma nafada mashi komai sede banfada mashi tarihinsu ba, kuma Baba wannan tafiya hada kai za'ayita, acan zaka samu aikin dazakayi idan yaso daga baya idan komai yadedeta zaka iya zuwa kadauki iyalinka.
Sede Baba banaso kafadama kowa labarinsu, kasan mutane akwai son zuciya nafiso kabarshi atsakaninmu wata rana zasuji labarinsu, kuma abangaren Jakadiya Waziri yace zasu zauna, kasan kuwa bangarenta yana daga bayan lambun gidan, bakowane yake zuwa ba, sede kai tunda sunsan kowaye kai zaka iya zuwa aduk lokacin dakakeso. Allah yabaka ikon rike sirrinku, sekayi ahankali da gidan sarauta, ba,a aboki agidan, kowa da halinshi yake zaune, dan haka kazama cikin shiri gobe insha Allahu zakutafi da safe. Allah yakareku daga dukkan sharri.
Baba yace amin, kuma naji dadin abinda kamun, ga iyalai na nan, nasan zaka kulamun dasu Allah yabaka ikon zama dasu lafiya, amma taya zamurika magana da kai? Murmushi malam yayi yace kada kasamu damuwa akwai waya ahannun Jakadiya, kuma iyalanka zasu zauna cikin kwanciyar hnkl, fatana Allah yabaku sa'a. Haka kowa yatashi Jakadiya tanacike da murna, harta tashi yace Jakadiya kisameni adaki, Bayan sun shiga naji malam yafara magana, akwai abubuwa da dama da zuciyata take sakamun akan wannan matar, shiyasa ma nace zakutafi tare. Kara rage murya yayi yana mata bayani,akan yanda yakeson abubuwan sutafi, sede duk yanda naso inji abinda suke fada ya gagara, haka nadawo inajiransu sufito, sundauki kusan awa daya suna tattaunawa sannan tafito.
Washe gari dasafe Malam yabada mota akadaukesu suka nufi babbar masarautar Gombe.
To jama,a bara muji menene asalin labarin wannan masarauta.
Tuna baya,
Asalin Labarin.
MASARAUTAR BUBAYARO.
Muhadu a page nagaba.
Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 30⚜35
Qaseem yayi saurin fadin haba Yaya kasan mekake fada kuwa? Sarki yace koma menene Qaseem nasan baze wuce tace in....... kara kamo rigarshi datayi ne yasashi yin shiru yamai da hankalinshi gareta. Bawan Allah ga 'Yata nan, ita kadai Allah yabani, mahaifinta yarasu nikadai narage mata, kuma nima gashi Allah zerabata dani. Daga cikin wancan kauyen muka fito, mutanen garin suka koromu sbd kawai wani yayi ma mahaifinta kazafi, sakamakon hakan ciwon zuciya yayi ajalinshi.
Mu kuma suka koromu komai basu bari mundauka ba. Inarokonka kobayan babu raina kada kabari Nafeesa takoma garinmu, kamar yanda kamun alkawari inason rayuwar Nafeesa tayi albarka dan Allah kadaure ka auri Nafeesa.
Qaseem cike da bacin rai yace dalla malama kifadi abu meyuwuwa kinko san dawanda kike magana? Idan baki sani ba, to........ tarin daya taso matane yasashi yinshiru suka maida hankalinsu kanta bakaramin shiga tashin hankali Sarki yashiga ba, ganin tana wani irin aman jini, Nafeesa ko se kuka takeyi, Sarki yatashi yace ma Waziri adauketa ko akan doki ne, mutafi da ita asibitin cikin gari.
Wani bafade Waziri yasa yadaukota, Haka Nafeesa ta tashi tana kuka. Cak bafaden daya dauketa ya tsaya jin jikinta yakara nauyi, Waziri yace muje mana katsaya kana bata lokaci, Ranka yadade ade zo aduba wannan baiwar Allah naji jikinta yasaki, dasauri Sarki yadawo dabaya, suna zuwa Waziri yataba hannunta yaji yadawo, yasa hannunshi gurin hancinta yaji ba numfashi, sam yamanta da diyarta agurin yace Rankai dade inaji fa ta mutu. Wani kara da Nafeesa tasaka nan take tafadi kasa sumammiya. Sarki cike da damuwa yasa Fadawa suka dauketa da mahaifiyarta aka dorasu akan doki aka nufi gida dasu, Qaseem kanshi jikinshi yayi sanyi yatausaya ma Nafeesa sosai.
Ko kafin sukai gida maman Nafeesa harta saki, dan akwai dan tafiya, suna zuwa sarki yasa aka kira Jakadiya nan Waziri yayi mata bayanin komai aka shiga da gawar cikin gida. Ita kuma Nafeesa aka kira likitansu domin yadubata.
Babu bata lokaci aka gama shiryata akayi mata sallah tasamu jama'a sosai, haka aka kaita gidanta na gaskiya, jikin Sarki yayi sanyi sosai dan yasan yariga da yadauki alkawarin da dole yacikashi. Bayan sundawo yakira Waziri dan suyi magana, bebi takan Qaseem ba, dan yasan baze bada goyon baya ba.
Sosai Waziri yakara karfafa mashi guiwa kuma yakara tunasar dashi muhimmanci alkawari, da kuma irin jihadin dazeyi, Waziri yace kobaka aureta ba, kasama mata miji acikin gidan nan ko awaje hankalinka baze taba kwanciya ba sbd bakasan irin rikon dazeyi mata ba. Sarki yace bakomai ai itama mutum ce, kamar kowa kuma yin hakan dazanyi baze ragemun wani abuba, sede Allah yasani atsarina banida ra'ayin auren macen da bata fito daga gidan sarauta ba, kuma wannan ra'ayi nane shiyasa Qaseem yakeda irin ra'ayin, segashi nashi haryafi nawa. Nasan zeji haushi na, amma dole incika alkawarin dana dauka dazaran Nafeesa tasamu sauki za adaura auren banason tashiga cikin damuwa. Allah yabani ladar abinda nayi.
Bakaramin tashin hankali Gimbiya Zakiyya tashiga ba da Jakadiya takawo mata maganar auren Sarki ba, duk da batason Jakadiya amma daga ranar tafara sakar mata fuska dan tasan zatayi mata amfani. Koda tafada ma mamanta shawara daya tabata, kada tasake tanuna bacin ranta akan auren, kogurin Sarki banyarda ki nuna bacin ranki ba. Da wannan shawarar Gimbiya tasamu sauki aranta. Koda Jakadiya taga tafara samun sakin fuska agurin Gimbiya seta kawo mata shawarar kozata kaita gurin bokanta.
Dawani kallo Gimbiya tabita, cike da bacin rai tace waiku meyasa bakuda tunani idan zakuyi magana. Ko anfada maki gidan sarauta gidan hauka ne? To kada kikara zomun da wannan maganar banzar. Jakadiya cike da ladabi tace Allah yahuci zuciyarki, kiyi hkr insha Allahu baza'a karaba, tace tashi kije idan kinsamo wata shawarar wadda tayi dede da tsarina zaki iya dawowa.
Wacece NAFEESA?