Sashe 17
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 75⚜80
Waziri ne zaune tare da Sarkin Fada, Waziri ya kalli Sarkin fada yace, kasan nifa nafara gajiya da masarautar nan, bamu samun komai se wahala, shi wancan Yana zaune, jaririma yafishi dadin sha,ani, shikuma Sarki Qaseem bawani aiki yake ba, kullum da anyi magana yace Yayanshi, kawai idan bazasu iya ba, yakamata sumika ma nawajenka.
Amma kuma zamusha shiririta, dan nasan Yarima kwata kwata sarauta bata dameshi ba, shiyasa kozaman fada bayaso. Wata irin dariya Sarkin fada yayi, da alama antabo mashi inda yake mashi kai kai, baki ya karkace yafara zuba, ashede kaima kana layina, yoni idan tanine ai dayanzu an dade dashafe babin wadannan sarakunan 2.
Aduniya babu abinda natsana kamar inga wadannan mutane 2 suna farin ciki, shiyasa bakaramin dadi najiba alokacin da akace Sarki ya samu matsalar shanyewar barin jiki. Naso ace Sarki Qaseem be anshi sarautar ba, nasan kila da kai za abama.
Amma kana maganar wani Yarima ai har abada bazeyi sarauta ba, sede idan ubanshi ya mutu, ai akwai dalilin dayasa bayason sarauta, anfada maka son danake mashi nabanza ne? Nifa banason wani daga zuri'arsu yaci gaba da mulkin nan. Waziri yace amma nasan duk ranar da akace angano inda Fulani take nasan daga ranar Sarki zewarke.
Dasauri Sarkin fada yace ina, ai har abada kuwa baze warke ba, dan bana tunanin Fulani tana raye, saurin kallonshi Waziri yayi yace kamar ya kenan? Rufe baki yayi yafara in ina, yace a,a kagane bawai ina nufin tamutu ba, gani nayi yau shekaru nawa da batan ta, inda tana raye ai da anganta. Wani murmushi Waziri yayi yace dama musami labarin mutuwarta ai dayafi, Sarkin fada dasauri yace wlh kuwa da kowa ya huta. Tashi yayi yace bari inje gurin mutuniyata, waziri yace wakenan?.
Jakadiya Karima mana ai kasan duk gidan nan banida aminiya kamarta, wato matar nan tasan takan duniya, sallama yayi mashi yayi gaba. Wata irin zufa ce tafara fitoma Waziri, ahankali yace Jakadiya Karima? Tasan takan duniya? Aminiyarshi?. Murmushi yayi yace nasamu daya, saura na biyu. Waya yaciro yakira malam, sun dade suna magana kafin yakashe yanufi fada.
Areef ne kwance akafar Momynshi Jakadiya Safeeya tana gefe suna fira, ahankali Gimbiya tashafi kanshi tace Yarima haryanzu naji shiru tunda mukayi maganar aure baka kara cewa komai ba, kasanfa kabar Abbanka cikin damuwa. Wani murmushi yasaki tare da lumshe ido, ita yakara gani aidonshi alokacin dayake bata abinci, ahankali yace beauty.
Momy tace wacece kuma Beauty? Saurin bude ido yayi yace kawai Momy inason mace me kyau, shiyasa kikaji nace beauty, murmushi tayi tace to kasamu kenan? Kai ya girgiza mata yace nade kusa samu kitayani addu,a. Momy tace Allah yasa irin zabin muce? Bata fuska yayi yamike tsaye yace Momy wai haryanzu baku cire wannan ra,ayin daga ranku ba? Nifa agskiya bazan auri yarinyar data taso gidan sarauta ba, duk wata al,ada tata da dabi'unta duk na sarauta, nidan sarauta itama yar sarauta towazeyi mulkin kenan?. Shiru Momy tayi tana kallonshi, tashi Jakadiya Safeeya tayi takama hannunshi tace haba dan autan Gimbiya, tomeye na bata ran? Zomuje gida kafadamun abinda kakeso, amma nima zanfada maka wanda nakeso, kayarda ? Kai yadaga mata taja hannunshi suka fita, da murmushi Gimbiya tabisu, aranta tana fatan Allah yasa ya amince.
Gimbiya Zakiyyah ce take tafaman masifa akan jakadiya Karima, wai ke wace irin mata ce, harni zakizo kirika fada ma, wai Sarkin fada yana gaishe ni. Toshi wanene dazemun wannan aiken, ko anfada maki ni baiwace dazakizomun da wannan maganar. Amma balaifinku bane, dan kunsami sakin fuska daga gurina ne, shiyasa kuke fadamun abinda kukaga dama, inda narike mulkina wlh ko kusa dani akace kizauna baza kizoba.
Kuma inaso kifadamun akan wane dalili Sarkin fada yace kigaisheni? Kasa tayi da kai tace Allah yahuci zuciyarki, wlh bada wata manufa yace nagaisheki ba, dama ganina yayi zanshigo nan shine yace ingaisheki, amma ai be isa yayi maki irin gaisuwar dakike tunani ba, agafarceni Gimbiya. Zama tayi tana huci tace, wannan shine karo nakarshe dazaki kara batamun rai, idan bahaka ba, wlh sekin fuskanci hukunci na. Godiya nake ranki yadade uwargida agurin Sarki, mace daya tamkar da dubu, fitila me haske zuciyar Sarki, Allah yakaramaki lafiya da daukaka aduniya, Allah yasa kifi haka. Murmushi tasaki sannan tadaga mata hannu tace muje kirakani gurin Medaki inaso indubata. Zaro ido Jakadiya tayi tace Eye, na'am , mekikace? Wata harara tasakar mata tace kina nufin bakiji menace ba? Nima yau inaso inje bangarenta. Wani miyau medaci Jakadiya tahadiya, dan ta tuna sanda zatazo nan sunhadu da Sarkin fada kuma zeje gurin Medaki. Tashi tayi jiki asanyaye suka nufi bangaren Medaki, bayi suna take mata baya.
Koda suka shiga azaune suka sami yar baba tana kallon casset din da Jakadiya ta kunna mata, tana ganin Areef tashiga sakin murmushi, shima murmushin yasaki, tare da sakin ajiyar zuciya, kusa da ita yazauna yana fadin beauty jiki yayi sauki ko? Matsowa tayi kusa dashi tadora kanta saman kafadarshi tare da daga mashi kai. Girgiza kai jakadiya tayi aranta tace dole in nuna ma Yar Baba matsayin kowane namiji agurinta, wato ita atunaninta yanda take hawan Baba kowama zata mashi haka? Dole musake sabon karatu. Tanaso tace mata ta tashi kuma bataso Areef yadauka dawata manufa, zama tayi akasa tace zonan yar Baba inji jikinki.
Tashi tayi taje tazauna kasa tare da dora kanta saman cinyarta, hannu tasa ajikinta tace ai zazzabin ma yatafi ko? Kai ta daga mata tana maida kallonta gurin Areef. Itama Jakadiya shi ta kalla, aranta tace tabbas kuna kama daga idonku har gurin bakinku, saukowa yayi shima yazauna akasa,ya kalli Jakadiya yace.
Aunty kina ganin idan nafitoma Momy da Abba wadda naji zuciyata tanaso, kuma bata kasance yar sarauta ba, kina ganin zasu ansheta? Murmushi Jakadiya tayi tace kwarai ma kuwa, amma dole sekayi abinda zanfada maka idan bahaka ba to sede ka auri mata 2, nikam banaso ka hada macen da kake so da wata, kana ganin yanda Sarki yakasance alokacin daya samu wadda yakeso, jiyayi dama beyi aure ba, da babu abinda zesa yakara aure bayan ya aurin zabinshi. Kuma kasan yanda sharrin matan sarauta yake, idan har sukaga mijinsu yana nuna fifiko atsakinsu yanzu zakaga anfara shigo da hassada.
Kuma nibanason kayi wani abu daze zo yaraba zumincin dake tsakanin iyayenka, duk da bangama gano wacce kake so ba, amma inaso yanzu kafada mun. Shiru yayi yana kara kallon beauty, itama shi take kallo, yace Aunty zanfada maki amma banaso beauty taji. Ai tanajin abinda yafada tafara dirza kafa akasa, tana turo baki tare dayin bayaninta da hannu na kurame. Dariya suka saka, yace metace wai?.
Jakadiya tace a,a ni baruwana kaine dakayi magana take wannan borin. Kallonta yayi yace beauty ai wannan maganar manya ce shiyasa nace banaso kiji, tashi tayi tadauki pillown kujera takwada mashi tashige daki tana dira kafa, dariya yayi hada rike ciki. Wayarshi ce tayi kara, yana dauka yace kasameni gidan Aunty.
Jakadiya tace hala Haisam ne ? Yace ai kinsan seshi, shikadai ne abokina aduniya nayarda dashi kamar yanda ya yarda dani, shiyasa bana tsoron yasan komai daga gareni. Sallama sukaji, Areef yace kashigo mana katsaya kamar kazo gidan surukai.
Zama yayi bayan sungaisa da Jakadiya yamika ma Areef hannu suka gaisa yana fadin ai garani bagidan surukan nazo nazauna ba. Dariya suka saka, Areef yace yauwa Aunty inajinki menene abinda kikeso inyi? Zama ta gyara ta kalli Haisam tasake fadin abinda tafada da farko, sannan takara dacewa abinda nakeso da kai yanzu kafadamun wace yarinya kakeso kuma a ina take, daga nan ni kuma zanfada maka mezakayi.
Sarki Qaseem ne zaune afalon gimbiya suna fira tana mika mashi kankana, kallonshi tayi tace Hubby, kayi hakuri nayi wani hukunci kuma bansanar da kai ba. Jawota yayi yasata ajikinshi sannan yace bakida damuwa kome kika yanke nasan zeyi dede da ra,ayi na, kinsan muna tafiya akan tsari daya. Murmushi tayi tace haka ne, dama bawani abu bane, munyi waya da Yaya nace mata tashiryo Ayman tadorota jirgi gobe ta taho.
Naga alamar Yarima yakasa samun wadda yakeso, nayi tunanin baya shiga cikin yan mata ne, shiyasa besamu wadda yakeso ba, amma idan Ayman tazo zansata tarika yimashi duk wata hidima, kuma surika fita tare nasan yin hakan zesa su shaku har soyayya tashiga tsakaninsu. Murmushi Sarki yayi yace, shiyasa nake sonki dayawa, kinyarda ra,ayinmu yana tafiya dede? Kai tadaga tana wasa da hannunshi. Yace amma ina fatan baki fadama Ummin Aymana dalilinki nasan tazo ba ko? Tace kamar kasani, banaso mushiga tsakaninsu harsesun shirya kansu sannan.
Yace da kyau, nafison kamar yanda naganki naji inasonki kema haka banaso mushiga hakkin Areef, duk da idan ya gwada bazebi zabinmu ba, bazanyarda ba, amma ko ita kada kifada mata dalilin sawa tazo, kawai kibarta, nasan zasu saba. Rungumeshi tayi tana fadin nagode hubby na. Kiss yayi mata akumatu, yana fadin bari inje gurin yaya yau likitan daze fara yimashi gashi zezo daga,
U.S, Tace Allah yasa adace, amma anan zezauna ko? Yace e zeyi kamar wata guda, kuma insha Allahu munasa ran nasara. Tace Allah yasa.
Da sallama suka shiga falon Medaki, sede bata nan, cike da fargaba Jakadiya karima tace rankiyadade kizauna bari inje indubota, zata shiga kenan tafito tana fadin ashe yau manyan baki garemu, Gimbiya Yaya da kanki aida kin aiko nazo. Ya mutsa fuska tayi tace kawai nima sha,awar fitowar nakeyi.
Zama tayi Jakadiya sebinta da idanu takeyi jikinta yana tsima, wata baiwa ce tashigo hannunta rike da katon faranti medauke da kayan marmari, jakadayi tace barka da fitowa Gimbiya, tace yauwa sannunki. Jakadiya tace ina fatan wannan kayan marmarin nadazu da aka kawo marasa kyau anfitar dasu ko? Medaki ta kalli Jakadiya, tayi murmushi tace ai basu dade bama. Gimbiya Zakiyyah tace shiyasa nakeso arika duba kayan daza,a kawo base ankawo ba ace basuda kyau.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 75⚜80
Waziri ne zaune tare da Sarkin Fada, Waziri ya kalli Sarkin fada yace, kasan nifa nafara gajiya da masarautar nan, bamu samun komai se wahala, shi wancan Yana zaune, jaririma yafishi dadin sha,ani, shikuma Sarki Qaseem bawani aiki yake ba, kullum da anyi magana yace Yayanshi, kawai idan bazasu iya ba, yakamata sumika ma nawajenka.
Amma kuma zamusha shiririta, dan nasan Yarima kwata kwata sarauta bata dameshi ba, shiyasa kozaman fada bayaso. Wata irin dariya Sarkin fada yayi, da alama antabo mashi inda yake mashi kai kai, baki ya karkace yafara zuba, ashede kaima kana layina, yoni idan tanine ai dayanzu an dade dashafe babin wadannan sarakunan 2.
Aduniya babu abinda natsana kamar inga wadannan mutane 2 suna farin ciki, shiyasa bakaramin dadi najiba alokacin da akace Sarki ya samu matsalar shanyewar barin jiki. Naso ace Sarki Qaseem be anshi sarautar ba, nasan kila da kai za abama.
Amma kana maganar wani Yarima ai har abada bazeyi sarauta ba, sede idan ubanshi ya mutu, ai akwai dalilin dayasa bayason sarauta, anfada maka son danake mashi nabanza ne? Nifa banason wani daga zuri'arsu yaci gaba da mulkin nan. Waziri yace amma nasan duk ranar da akace angano inda Fulani take nasan daga ranar Sarki zewarke.
Dasauri Sarkin fada yace ina, ai har abada kuwa baze warke ba, dan bana tunanin Fulani tana raye, saurin kallonshi Waziri yayi yace kamar ya kenan? Rufe baki yayi yafara in ina, yace a,a kagane bawai ina nufin tamutu ba, gani nayi yau shekaru nawa da batan ta, inda tana raye ai da anganta. Wani murmushi Waziri yayi yace dama musami labarin mutuwarta ai dayafi, Sarkin fada dasauri yace wlh kuwa da kowa ya huta. Tashi yayi yace bari inje gurin mutuniyata, waziri yace wakenan?.
Jakadiya Karima mana ai kasan duk gidan nan banida aminiya kamarta, wato matar nan tasan takan duniya, sallama yayi mashi yayi gaba. Wata irin zufa ce tafara fitoma Waziri, ahankali yace Jakadiya Karima? Tasan takan duniya? Aminiyarshi?. Murmushi yayi yace nasamu daya, saura na biyu. Waya yaciro yakira malam, sun dade suna magana kafin yakashe yanufi fada.
Areef ne kwance akafar Momynshi Jakadiya Safeeya tana gefe suna fira, ahankali Gimbiya tashafi kanshi tace Yarima haryanzu naji shiru tunda mukayi maganar aure baka kara cewa komai ba, kasanfa kabar Abbanka cikin damuwa. Wani murmushi yasaki tare da lumshe ido, ita yakara gani aidonshi alokacin dayake bata abinci, ahankali yace beauty.
Momy tace wacece kuma Beauty? Saurin bude ido yayi yace kawai Momy inason mace me kyau, shiyasa kikaji nace beauty, murmushi tayi tace to kasamu kenan? Kai ya girgiza mata yace nade kusa samu kitayani addu,a. Momy tace Allah yasa irin zabin muce? Bata fuska yayi yamike tsaye yace Momy wai haryanzu baku cire wannan ra,ayin daga ranku ba? Nifa agskiya bazan auri yarinyar data taso gidan sarauta ba, duk wata al,ada tata da dabi'unta duk na sarauta, nidan sarauta itama yar sarauta towazeyi mulkin kenan?. Shiru Momy tayi tana kallonshi, tashi Jakadiya Safeeya tayi takama hannunshi tace haba dan autan Gimbiya, tomeye na bata ran? Zomuje gida kafadamun abinda kakeso, amma nima zanfada maka wanda nakeso, kayarda ? Kai yadaga mata taja hannunshi suka fita, da murmushi Gimbiya tabisu, aranta tana fatan Allah yasa ya amince.
Gimbiya Zakiyyah ce take tafaman masifa akan jakadiya Karima, wai ke wace irin mata ce, harni zakizo kirika fada ma, wai Sarkin fada yana gaishe ni. Toshi wanene dazemun wannan aiken, ko anfada maki ni baiwace dazakizomun da wannan maganar. Amma balaifinku bane, dan kunsami sakin fuska daga gurina ne, shiyasa kuke fadamun abinda kukaga dama, inda narike mulkina wlh ko kusa dani akace kizauna baza kizoba.
Kuma inaso kifadamun akan wane dalili Sarkin fada yace kigaisheni? Kasa tayi da kai tace Allah yahuci zuciyarki, wlh bada wata manufa yace nagaisheki ba, dama ganina yayi zanshigo nan shine yace ingaisheki, amma ai be isa yayi maki irin gaisuwar dakike tunani ba, agafarceni Gimbiya. Zama tayi tana huci tace, wannan shine karo nakarshe dazaki kara batamun rai, idan bahaka ba, wlh sekin fuskanci hukunci na. Godiya nake ranki yadade uwargida agurin Sarki, mace daya tamkar da dubu, fitila me haske zuciyar Sarki, Allah yakaramaki lafiya da daukaka aduniya, Allah yasa kifi haka. Murmushi tasaki sannan tadaga mata hannu tace muje kirakani gurin Medaki inaso indubata. Zaro ido Jakadiya tayi tace Eye, na'am , mekikace? Wata harara tasakar mata tace kina nufin bakiji menace ba? Nima yau inaso inje bangarenta. Wani miyau medaci Jakadiya tahadiya, dan ta tuna sanda zatazo nan sunhadu da Sarkin fada kuma zeje gurin Medaki. Tashi tayi jiki asanyaye suka nufi bangaren Medaki, bayi suna take mata baya.
Koda suka shiga azaune suka sami yar baba tana kallon casset din da Jakadiya ta kunna mata, tana ganin Areef tashiga sakin murmushi, shima murmushin yasaki, tare da sakin ajiyar zuciya, kusa da ita yazauna yana fadin beauty jiki yayi sauki ko? Matsowa tayi kusa dashi tadora kanta saman kafadarshi tare da daga mashi kai. Girgiza kai jakadiya tayi aranta tace dole in nuna ma Yar Baba matsayin kowane namiji agurinta, wato ita atunaninta yanda take hawan Baba kowama zata mashi haka? Dole musake sabon karatu. Tanaso tace mata ta tashi kuma bataso Areef yadauka dawata manufa, zama tayi akasa tace zonan yar Baba inji jikinki.
Tashi tayi taje tazauna kasa tare da dora kanta saman cinyarta, hannu tasa ajikinta tace ai zazzabin ma yatafi ko? Kai ta daga mata tana maida kallonta gurin Areef. Itama Jakadiya shi ta kalla, aranta tace tabbas kuna kama daga idonku har gurin bakinku, saukowa yayi shima yazauna akasa,ya kalli Jakadiya yace.
Aunty kina ganin idan nafitoma Momy da Abba wadda naji zuciyata tanaso, kuma bata kasance yar sarauta ba, kina ganin zasu ansheta? Murmushi Jakadiya tayi tace kwarai ma kuwa, amma dole sekayi abinda zanfada maka idan bahaka ba to sede ka auri mata 2, nikam banaso ka hada macen da kake so da wata, kana ganin yanda Sarki yakasance alokacin daya samu wadda yakeso, jiyayi dama beyi aure ba, da babu abinda zesa yakara aure bayan ya aurin zabinshi. Kuma kasan yanda sharrin matan sarauta yake, idan har sukaga mijinsu yana nuna fifiko atsakinsu yanzu zakaga anfara shigo da hassada.
Kuma nibanason kayi wani abu daze zo yaraba zumincin dake tsakanin iyayenka, duk da bangama gano wacce kake so ba, amma inaso yanzu kafada mun. Shiru yayi yana kara kallon beauty, itama shi take kallo, yace Aunty zanfada maki amma banaso beauty taji. Ai tanajin abinda yafada tafara dirza kafa akasa, tana turo baki tare dayin bayaninta da hannu na kurame. Dariya suka saka, yace metace wai?.
Jakadiya tace a,a ni baruwana kaine dakayi magana take wannan borin. Kallonta yayi yace beauty ai wannan maganar manya ce shiyasa nace banaso kiji, tashi tayi tadauki pillown kujera takwada mashi tashige daki tana dira kafa, dariya yayi hada rike ciki. Wayarshi ce tayi kara, yana dauka yace kasameni gidan Aunty.
Jakadiya tace hala Haisam ne ? Yace ai kinsan seshi, shikadai ne abokina aduniya nayarda dashi kamar yanda ya yarda dani, shiyasa bana tsoron yasan komai daga gareni. Sallama sukaji, Areef yace kashigo mana katsaya kamar kazo gidan surukai.
Zama yayi bayan sungaisa da Jakadiya yamika ma Areef hannu suka gaisa yana fadin ai garani bagidan surukan nazo nazauna ba. Dariya suka saka, Areef yace yauwa Aunty inajinki menene abinda kikeso inyi? Zama ta gyara ta kalli Haisam tasake fadin abinda tafada da farko, sannan takara dacewa abinda nakeso da kai yanzu kafadamun wace yarinya kakeso kuma a ina take, daga nan ni kuma zanfada maka mezakayi.
Sarki Qaseem ne zaune afalon gimbiya suna fira tana mika mashi kankana, kallonshi tayi tace Hubby, kayi hakuri nayi wani hukunci kuma bansanar da kai ba. Jawota yayi yasata ajikinshi sannan yace bakida damuwa kome kika yanke nasan zeyi dede da ra,ayi na, kinsan muna tafiya akan tsari daya. Murmushi tayi tace haka ne, dama bawani abu bane, munyi waya da Yaya nace mata tashiryo Ayman tadorota jirgi gobe ta taho.
Naga alamar Yarima yakasa samun wadda yakeso, nayi tunanin baya shiga cikin yan mata ne, shiyasa besamu wadda yakeso ba, amma idan Ayman tazo zansata tarika yimashi duk wata hidima, kuma surika fita tare nasan yin hakan zesa su shaku har soyayya tashiga tsakaninsu. Murmushi Sarki yayi yace, shiyasa nake sonki dayawa, kinyarda ra,ayinmu yana tafiya dede? Kai tadaga tana wasa da hannunshi. Yace amma ina fatan baki fadama Ummin Aymana dalilinki nasan tazo ba ko? Tace kamar kasani, banaso mushiga tsakaninsu harsesun shirya kansu sannan.
Yace da kyau, nafison kamar yanda naganki naji inasonki kema haka banaso mushiga hakkin Areef, duk da idan ya gwada bazebi zabinmu ba, bazanyarda ba, amma ko ita kada kifada mata dalilin sawa tazo, kawai kibarta, nasan zasu saba. Rungumeshi tayi tana fadin nagode hubby na. Kiss yayi mata akumatu, yana fadin bari inje gurin yaya yau likitan daze fara yimashi gashi zezo daga,
U.S, Tace Allah yasa adace, amma anan zezauna ko? Yace e zeyi kamar wata guda, kuma insha Allahu munasa ran nasara. Tace Allah yasa.
Da sallama suka shiga falon Medaki, sede bata nan, cike da fargaba Jakadiya karima tace rankiyadade kizauna bari inje indubota, zata shiga kenan tafito tana fadin ashe yau manyan baki garemu, Gimbiya Yaya da kanki aida kin aiko nazo. Ya mutsa fuska tayi tace kawai nima sha,awar fitowar nakeyi.
Zama tayi Jakadiya sebinta da idanu takeyi jikinta yana tsima, wata baiwa ce tashigo hannunta rike da katon faranti medauke da kayan marmari, jakadayi tace barka da fitowa Gimbiya, tace yauwa sannunki. Jakadiya tace ina fatan wannan kayan marmarin nadazu da aka kawo marasa kyau anfitar dasu ko? Medaki ta kalli Jakadiya, tayi murmushi tace ai basu dade bama. Gimbiya Zakiyyah tace shiyasa nakeso arika duba kayan daza,a kawo base ankawo ba ace basuda kyau.