← Book details A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 33

Sashe 27

A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Seda yabama kowa dariya, nan fadawa suka zaunar dashi. Se alokacin Sarki Hasheem yayi magana, jikinshi asanyaye yace Malam, kafadi irin hukuncin daya kamata ayima kowa abisa koyarwa ta addinin musulunci, kamar yanda yazo a Qur'ani. Dan nagaji da kallon fuskokin wadannan mutanen.

Dan duk acikinsu nafijin haushin mutum daya, bakowa bace se Jakadiya Karima. Allah ya isa tsakanina dake, kin cuceni, wlh zan iya yafema kowa agurin nan amma banda ke, bazan taba iya yafe maki ba. Mundaukeki Uwa asheke makiyarmuce nida dan uwana..... kuka yasaka tamkar karamin yaro.

Alokacin hatta da Malam seda yazubar mashi da kwalla sbd yanda yakeyin kuka kowa yasan abun yana cimashi rai sosai. Sarki Qaseem yana kuka yace Malam dan Allah ayanke masu hukunci kada ciwon Yaya yadawo.

Malam yace Alhamdulillahi, kamar yanda kuka sani duk wani laifi na duniya babu hukuncin da Alku'ani da hadisi basu kawo ba, dan haka zamu duba muga irin hukuncin da Allah yace ayima masu irin laifinku. Zanfara daga kasa zuwa sama, wato daga masu karamin laifi zuwa babba.

Zan fara da masu gadi, mati da Lado, tabbas kun aikata babban kuskure, domin da farko kunci amanar masarauta, sannan kunbada gudummuwa gurin aikata fasadi, dan haka hukuncinku anan shine zakuyi zaman kurkutu natsawon shekaru 2, domin aladabtar daku, sannan baku bakara aiki awata masarauta.

Se amintaccen bawan Sarki Hasheem, kaima kaci amanar Uban gidanka, sannan kazamo daya daga cikin wanda yatemaka ma Sarkin fada kuka sace Fulani. Dalili daya ne bazesa ayanke maka hukuncin kisa ba, saboda Fulani bata mutu ba, kuma Qur,ani cewa yayi wanda yakashe akashe shi, sbd haka kaima za,a daureka akurkutu na tsawon shekaru 5, tare da aiki metsanani.

Gimbiya Zakiyya, kinkasance matar aure, wadda aka kamaki da laifuka biyu. Nafarko kina da sa hannu abatan Fulani, wanda dakunsami dama kasheta zakuyi. Nabiyu kuma laifin aikata zina. To hukuncin zina anan yakasu kashi 2, akwai na wadda bata tabayin aure ba, wato budurwa, akwai kuma na wadda ta tabayin aure.

Idan budurwa tayi zina, kuma aka tabbatar dashedu, za,a yanke mata hukunci bulala 100, idan abokin yinnata shima saurayine, hukuncinsu daya.

Matar aure. Duk matar datayi zina kuma tanada aure, ko ta taba yin aure. Hukuncinta kisane, tahanyar jefewa da duwatsu, wanda yara ne zasu jefeta harta mutu, za,a rufe duka jikinta cikin rami abar kanta shine za,ayita jifa harta mutu.

Idan abokin zinarta yataba aure, hukuncinsu daya, idan kuma shi beda aure, to nata daban nashi daban. Abisa shedar da muka samu daga gurin wanda yayi maki asirin da kika fada wannan alfasha.

Kamar yanda yazo a arba'una hadith, mazon Allah yace INNALLAHA TAJAWAZILI AN UMMATI➡➡ Lallai Allah yagafarta ma al'ummata, AL,,KADAHA... abinda sukayi da KUSKURE. WANNISIYANA... abinda sukayi da MANTUWA. WAMASTUKURUHU ALAIHI... da abinda AKA TURSASASU AKANSHI. Rawahul bukhari wa muslim.

Abisa duba da wannan hadisi, sarkin Fada yayi amfani da karfin asiri ta hanayar mallakeki har kika biye mashi kuka aikata alfasha. Abisa wannan hadisi, anan bakida laifi agurin aikata wannan zina. Dan haka bazaki dauki hukuncin zina ba anan.

Sede hukuncin dazaki dauka na aikata laifin cin amana gurin niyar salwantar da rayuwar Fulani, dan haka zakiyi zaman kurkutu shekara 5. Saura hukunci kuma yarage ga mijinki.

Tunkafin yacigaba Sarki Hasheem yace Malam da ita da Medaki duk nayanke igiyara aurena akansu, dan haka kacigaba da yanke hukuncinka. Hannu Zakiyyah ta dora akai tana kuka.

Malam yace Medaki, kema hukuncinki biyu ne. Amma tunda nakarshen megaba daya ne, to hukunci daya zamu yanke maki, naki hukuncin kisa ne, tahanyar jefewa, tunda ke kin amsa kece kika bama sarkin Fada hadin kai da kanki. Dan haka hukuncin kisa zaki dauka.

Jakadiya Karima kema hukuncin kisa ne akanki, sbd kin aikata kisan kai domin kinsa anzubar da cikin Gimbiya Suhailat. Anyanke maki hukuncin kisa daurin rai da rai akurkutu, tare da horo metsanani.

Boka, kaima hukuncin kisa ne, ta hanyar rataya, tunda ka amsa laifinka, kuma Allah kadai yasan iyakar ta,asar dakayi.

Hukuncinmu na karshe akan Sarkin fada, kai kam da ana mutuwa adawo to da seka karbi duka hukuncinka. Amma hukuncinka anan shine kisa ta hanyar rataya.

Anan muka kawo karshen wannan hukunci na MASARAUTAR BUBAYERO. Inafatan hukunci yayi maku, idan kuma akwai wani abu kuna iya fada, yajuya yana kallon Sarki. Sarki Qaseem yakalli Yayanshi. Kai yadaga alamun hukunci yayi, sannan yace kuma agobe za,a aiwatar da wannan hukunci.

Ihu Gimbiya Zakiyyah tasaka kamar meshirin shiga hauka, Medaki da Jakadiya ma kuka kawai sukeyi kamar ransu zefita. Haka aka kara tasasu zuwa kurkutu kafin gobe.

Nima nace Allah yakaimu goben da rai da lafiya.

Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]

Season 110⚜115

Kusa da Baban Darazo Fulani ta matsa, idanunta haryanzu basu dena zubar da kwalla ba, dukawa tayi har kasa tace, Baba hakika banida bakin dazanyi maka godiya, kayimun abinda bakowa ne dan Adam bane ze iya yimani shi.

Tabbas kazamo daya daga cikin mutane masu muhimmanci arayuwata, kuma daga yau inaso kadaukeni tamkar diyarka ta cikinka, inaso kadauko duka iyalanka kudawo nan dazama dan suma sunzama yan uwana.

Baba yace babu komai Fulani, duk abinda nayi maki nayi shine dan Allah, banyi dan wani abu naku ba, asalima bansan wane irin matsayi gareki ba. Hakika naji dadin yanda kika dauke ni, kuma nagode Allah yasaka da alkhairi.

Haka kowa yatashi yanufi bangarenshi kafin gobe da safe. Haisam ya kalli Areef yace abokina nizan tafi gida, amma dole gobe indawo in kalli wasan daza,ayi agidan nan. Tabbas nakara daukar darasi agidanku.

Allah yakara mana karfin imani kuma yacire mana SON ZUCIYA. Areef yace amin, nima kaina abubuwan gidan nan sun gama daga mun hankali, naji tausayin beauty na sosai, ta dalilin masu SON ZUCIYA tarasa ingantatacciyar rayuwa da kowane dan Adam masu galihu suke samu.

Tarasa cikakken Ilimin addini dana Boko, batasan kowa acikin yan uwanta ba, batasan yaya mutane suke ba, har seda Allah yakawota cikin gidan nan. Kalli Umminta, tasamu kanta acikin hauka harna tsawon shekaru 18. Agaskiya mutane basa kyautawa.

Nayi alkawarin zan jiyama beauty rayuwa medadi, wadda batayi irinta abaya ba. Zan sama mata makaranta me kyau wadda zata samu cikakken ilimin addini dana boko. Fatana Allah yabani tsawon rai in cika wannan burin dana dauka. Kamar yanda Sarkin fada yake ikirarin yasa anciremun son sarauta azuciyata, to be cuceni ba.

Kanshi ya cuta, kuma naji dadin hakan, zanyi amfani da damar dana samu dan insamu lokacin beauty na, nasan inda inason sarauta bazan iya samun lokacinta ba, bare incika mata burin dana dauka, dan haka zan rokisu Abba ayi bikinmu akusa dan bana tunanin zama da beauty akasar nan.

Zantafi da ita wata kasa harseta samu ilimi me kyau sannan mudawo. Haisam yace gaskiya ka kyauta, sede kasan da kyar idan su Abba zasu yarda, yanda beauty bata taso agidan nan ba zasu so ace sun sami lokacin zama da ita. Areef yace katayani addu,a insamu shawo kansu.

Washe gari da misalin karfe 10 na safe tawagar Sarkin Yobe wato mahaifin Zakiyyah da mahaifiyarta suka iso masarautar BUBAYERO. Dan tun ajiya Sarki Hasheem yasa Sarki Qaseem yafada masu halin da ake ciki. Ba karamin tashin hankali suka shiga dajin wannan labari, ba kamar mahaifiyarta datasan ta dalilin haka zata zama abin tsangwama acikin kishiyoyinta.

Zaune suke afalo, sede Familyn gidan ne, kawai aciki, tare dasu Mahaifan Zakiyyah, se kuma Waziri, malam da Jakadiya Safeeya. Agefe guda kuma Zakiyyah ce zaune atakure guri guda se kuka takeyi.

Mahaifinta ne yayi gyaran murya yafara magana. Hakika Zakiyyah kinbani mamaki da irin abinda kikayi, saboda kawai kishi irin naku na mata, yanzu inda Allah yabaku sa,a kunsamu damar kashe Fulani da shikenan kema kinza me kisan kai ko?.

Ko agidanku dakika taso acikin kishiyoyi kika samu mahaifiyarki, kintaba ganin ance ta harari wani acikinsu? Duk da takasance karama acikinsu amma hakan besa ta rainasu ba. Agaskiya banji dadin abinda kikayima kishiyarki ba.

Kuma naji dadin hukuncin da aka yanke maki, wannan shine dede ga duk mutumin da yace Son zuciya zerika bi arayuwarshi, koyanzu da kikaga munzo bawai munzo bane dan ke, munzo ne, kawai dan inbada hakuri agurin mutanen da kika zalunta, babu ruwana da hukuncin da aka maki, haka zaki zauna tare da sauran masu laifi har shekaru 5, idan Allah yasa har lokacin ina raye nibazan hanaki zama gida na ba, amma kisani kina dawowa zan aurar dake ga duk wanda naga dama.

Dayake Sarki Hasheem yace kada wanda yafada masu abinda suka aikata da Sarkin Fada hakan yasa basusan maganar ba. Dan Sarki yace yanajin kunyar mahaifinta shiyasa yahana afada masu abinda tayi, duk da ba laifinta bane.

Kuka sosai Zakiyyah takeyi ta matso kusa da Babanta takama. Kafarshi tace dan girman Allah Baba kayafemun, wlh nikaina nayi nadamar abinda na aikata, babu irin shawarar da Umma bata bani ba, amma nabiyema hudubar shedan na aikata abinda yazubar da kimar masarautarmu, dan Allah kuyafe mani koda mutuwa zata riskeni acikin kurkutu.

Seda kwalla tacikama mahaifinta ido, damma bakin glass ne a idonshi, juyawa tayi kusa da Ummanta takifa kanta bisa cinyarta tasaka kuka, tarasa bakin magana, itama Ummar kuka takeyi sosai, seda suka bama mutanen falon tausayi.

Mahaifin Zakiyyah ya kalli Sarki Hasheem da Fulani, yace iname neman gafara agurinku, tabbas Zakiyya ta aikata kuskure dan Allah kuyi hakuri, muzamu koma seku aiwatar da duk hukuncin da kuka yanke ma kowa, kada tausayi ko wani kusanci ya hanaku cika umarnin Allah da Manzonsa.

Tashi yayi yana goge kwallar data zubo mashi, yanufi kofa yana fadin Zakiyyah nayafe maki duniya da lahira, Allah yasa wannan abu daya faru yazama kaffara agareki, idan munkara haduwa zanyi farin ciki da haka idan kuma ta Allah takasance se ince Allah yasadamu da alkhairi, haryanzu kinada lokacin tuba, kada kiga anyanke maki hukunci ki kasa cigaba da neman gafara agurin Allah.

Yana kai nan kuka yaci karfinshi yayi waje, fadawanshi dake bakin kofa suka mara mashi baya. Tashi Umman Zakiyyah tayi itama zata tafi, Zakiyyah tariketa tana kuka, tace Umma bakice komai ba, dan Allah kimun magana kada in mutu da fushinki. Jawota tayi ta rungumeta tace.
Chapter 27 · 0% Book details