Sashe 10
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Murmushi tayi tace gskiya nafi kowa farin ciki da wannan al'amari, sbd yanzu Uban gidana zesamu abinda ranshi yakeso. Dan haka zan daukota domin akoya mata zama agidan sarauta. Kallonta yayi yace ai inaganin kamar Suhailat tana koya mata, babu damuwa nasan zata kula da ita sosai. Jakadiya tayi murmushin yake tace toshikenan bari inje infada masu Gimbiyar. Check yadauko guda 2 yace takaimasu kowa dai dai. Wasu kudi yadauko yamika mata yace ga wannan kema kirike ahannunki. Godiya tayi mashi tafita.
Gurin Sarkin fada tawuce, abinda yafaru tafada mashi, sosai suka shiga tashin hankali. Sarkin Fada yace kina ganin Sarki baze iya samun haihuwa da wannan yarinyar ba kuwa? Kinsan fa ance larabawa albarka garesu. Jakadiya tace kada kadamu nasan abinda zanyi, damma Sarki yace ba,a gurina zata zauna ba da tunkafin tashiga gidanshi zanyi kokarin hanata haihuwa, amma kasan ni amintattar Sarkice dan haka kome nakai zesata taci, dan haka kada kadamu inde ina raye bazan bar Sarki yaga kwanshi aduniya ba. Shekarata nawa ina mashi hidima amma haryanzu nakasa zama wata acikin gidan nan, haka zankare a Jakadiya?.
Sede inzama fitila ina haska wasu ni ina kona kaina, ai rashin gata ba hauka bane, dan haka gara kowa yayita zama ahaka, shima wannan yaron dande ka hanani dayanzu na aiwatar mashi. Sarkin fada yace kiyi hakuri wannan yaron yashiga rai na, Allah yasani badan so nafara daukarshi ba, amma daga baya yashiga raina sosai, dan haka kibarshi, ninasan ko Sarki yamutu sede Qaseem yahau kujerarshi bade Areef ba, dan haka mutsaya akan sarki da matanshi. Yanzu kije ki kaima Gimbyar Baban Gida mugun labari, dannasan ita kadai zata shiga damuwa, banda Medaki, itakam ai tamu ce. Dariya Jakadiya tayi tace wlh bakada dama. Yace Allah kuwa kinsan daza,a bani Gimbiya medaki ai dana more, tun lokacin datazo gidan nan miyau na yabiya kawai senaji wai Sarki ze aureta. Jakadiya tace ai naga alamar itama yar hannu ce, amma matso kaji. Wata dariya suka kwashe da ita Sarkin fada yace kina ganin haka za,ayi? Tace sosai ma, amma bayanzu ba senan gaba idan komai ya zama dede.
Wani uban gumi ne yake fitowa daga jikin Gimbiya Zakiyya, kara kallon Jakadiya tayi tace yanzu jakadiya har saurin zuwa ki kawomun wannan bakin labarin kikeyi? Jakadiya tayi kasa da kai tace Allah yahuci zuciyarki, shima Sarki ba sonta yake ba, kawai tallarta Babanta yayi mashi, kuma kinsan Sarki dasaukin kai shiyasa ya amsa, amma dakanshi yafadamun ke kadaice macen dayakeso aranshi, duka sauran ya auresu ne abisa lalura. Dan haka ki kwantar da hankalinki.
Komawa tayi tazauna, saurin zuba mata ruwa jakadiya tayi tamika mata. Bayan tasha tace yanzu ya za'ayi kenan? Jakadiya tace Ranki yadade kamar yanda kika saba, hakan zakiyi, kinsan Sarki yana yabonki akan halayyarki tarashin tada hankali aduk lokacin dazeyi aure. Yace shiyasa yake kara sonki. Murmushi Gimbiya tayi tace shikenan, amma wannan karon bazan kyale wannan yarinyar ba. Jakadiya tace ai bazamu barita dadeba.
Ita kuwa Gimbiya medaki duk da taji haushi kadan amma ana bata magudan kudi tamanta da fushin. Jakadiya tace dama nasan bazaki damu ba, se waccan sarkin kishin, ita tana ganin kamar ita kadai sarki yakeso dan tafito daga gidan sarauta. Medaki tace aisetayi tayi nikam inde da kudi ya auri 10 ina ruwa na, nasan kawai zanrasa kulawar danake samu duk bayan kwana 2 , nasan hakanne kawai zedameni dan Sarki akwai iya shiga rai. Dariya Jakadiya tayi tace ai Gimbiya nasan matsalarki, kuma wannan badamuwa bace kede kawai kirikeni zaki samu yanda kikeso. Sarkin fada ma yanzu yaganni zanshigo nan yace ingaisheki, kinsan ke kadai yake gaidawa aduk matan gidan nan gaskiya yanaji dake. Medaki tayi dariya tace ai yana da kirki damma kada ace wani abu ai daya rika rakoki munashan labarai. Murmushi Jakadiya tayi tace ah, tunda kinaso ai angama.
Sati 2 Gimbiya Suhailat tadauka tana gyara Rayhana, takara kyau, sosai kyanta haryaso yayi yawa, tasha gyara sosai. Duk wata kissa Gimbiya ta koya mata, dayanda zata zauna da matanshi, babu abinda bata koya mata ba.
Duk wanda yakwana yatashi agarin Gombe babu wanda besan Sarki zeyi aure ba, gaggarumin biki aka shirya gidan kanshi yasha gyara, hankalin Gimbiya Zakiyya bakaramin tashi yayi ba, dan tagano irin son da Sarki yakema Rayhana, tun daga dukiyar dayake kashewa da kuma irin hidimar da taga Qaseem yanayi, wanda tasan shikanshi yana murna da bikin.
Taso ta tadama Sarki hankali akan auren, amma mamanta tanaji tahanata, tace bakida hankali Zakiyya? Kina ganin akan abinda yakeso baze iya wulakantaki ba? Tunwuri idanma wasu ne suke zugaki togara kidawo hanya, kina ganin nice karama acikin matan Abbanki amma yanzu nice nazama babba, dan haka banyarda kikara tada hankalinki akan auren nan ba. Kuma banyafe maki ba, idan har kika yarda wata tajaki kukaje gurin wani malami ko boka. Hakuri Gimbiya Zakiyya tayi ta bata kuma tayi mata alkawarin bazata je gurin kowa ba, kuma bazata kara tada hankalinta akan auren ba. Da haka ta kwantar da hankalinta, sede tayi alkawarin idan har tuggu da kissa suna sa mutum yaci riba zatayi amfani dasu takori Rayhana daga gidan Sarki.
Ayau ne miliyoyin jama'a daga jahohi daban daban da manyan sarakuna na garu ruwa suka halarci bikin Sarki Hasheem da Rayhana, wanda aka daura akan sadaki million 1, kowa yasheda wannan auren Soyayya ne Sarki yayi, ankashe dukiya sosai, anci ansha maroka da mawaka sun sami kyauta sosai. Adaren ranar Sarki da sauran Sarakuna da manyan masu kudi sukayi kayatattar walima ababban dakin taron masarautar Bubayero.
Bayan sungama kowa yanufi masaukinshi, kuma ranar aka kai amarya Rayhana dakinta dayasha dukiya kamar ba,a nigeria ba. Yayin da wasu suka cika da farin ciki alokacin Gimbiya Zakiyya tarasa inda zata sa kanta sbd tsabar bakin ciki. Jakadiya kuwa jan Sarkin Fada tayi suka nufi part din Medaki acan suka zauna suna bikinsu.
Nima nace yakamata abar amarya da Ango su sha amarcinsu.
Nagode sekunji ni a next page.😘.
Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 50⚜55
Washe gari. Basu suka tashi ba, se 8:00, dasauri Sarki yatashi ganin ko sallah basuyi ba, gaba daya kunyar fita yakeyi dan yasan kowa nagidan yasan baya fashin sallah amasallaci, babban abin kunya ma abokananshi sunce zasu biyo sugaisa da Amarya kafin su wuce, gashi nan yamakara.
Kallon Rayhana yayi wadda take kwance fuskarta tayi haske ga sahun kwallan datayi jiya nan kwance afuskarta. Murmushi yayi yashafi gashinta wanda ya hargitse, ahankali yace kece farin cikina GIMBIYA FULANI. Kiss yayi ma goshinta yatashi yaje yayi wanka yana fitowa yatada sallah, bayan yagama ya dauko Waya yakira Qaseem, yana dauka yace ai Yaya dayanzu zankiraka ince bakifa suna Falo harsun kusa gama karyawa. Sosa kanshi yayi yakara kallon Fulani yayi murmushi yace Uhm ka aika Safeeya taje takiramun Jakadiya tazo gurin Fulani nizan fita gurin baki.
Shiru yayi sannan yace amma Yaya meze hana kamaidata dakinta se inturo Safeeya tazo ta kula da ita, kasan bazata yarda Jakadiya ta kula da ita ba, tunda basu saba ba. Murmushi Sarki yayi yace shikenan to bari in maidata dama dan naga Jakadiya ita kadai keshiga dakina shiyasa nace haka amma yanzu zan maidata dakinta. Kashe wayar yayi kunya duk takamashi yanzu yazecema mutane.
Bayan yamaida Fulani dakinta wanda kofa ce kawai tarabasu da falon Sarki, duk abinda yakeyi tana jinshi kunya ce tahanata bude ido. Zama yayi yana kallonta, can kuma yatashi yafita yanufi gurin baki, akofa yahadu da Safeeya, cike da girmamawa ta durkusa tagaisheshi, amsawa yayi yana me mata fara'a. Yace yauwa Safeeya idan tashirya kaya suna nan su zata saka zasu gaisa da baki. Da to ta amsa mashi yayi waje, yana fita fadawa suka mara mashi baya suna kwasar gaisuwa.
Duk wanda yaganshi aranar yasan yana cikin farin ciki, dan duk yanda yaso yaboye fara'arshi kasawa yayi. Yana shiga falon baki suka fara yimashi tsiya, sosai yake dariya dayake yashigo cikin abokanshi. Wani Sarki yace gskya Hasheem bantaba ganin wannan farin cikin atare da kai ba, kada muna skul baka wannan fara'ar. Lallai baseka fada ba, kowa yasan yanzu ne kayi auren soyayya. Wani yace aidole yayi farin ciki wlh auren so daban yake, shiyasa banyi aure ba seda nasamu wadda nakeso. Haka sukayita barkwanci suna dariya, wani yace kaga kada muyi rana gara afiddo mana Amaryar data hanaka sallah amasallaci muganta muga wane irin zabe ne kayi haka. Dariya yayi yace a gaskiya sede muje Falona babu wanda ze fitomun da mata tana amarcinta tafito waje. Dariya suka saka yafita.
Abakin kofarshi yahadu da Jakadiya, saurin dukawa tayi tana mashi kirari, murmushi yayi yace Jakadiya kina lafiya? Tace lfy lau Rankai dade, dama tundazu naso inzo induba yakuka kwana sekuma naji ance badakai akayi sallah ba, shine nace to kobaku tashi dawuri ba?.
Murmushi yayi yace hakane, ai har Safeeya tazo tana gurin Fulani. Fulani? Jakadiya takara maimaita sunan aranta. Murmushi tayi tace to ai shikenan, bara inje ingyara dakin yace to. Dakin Fulani yawuce, tunkafin ya isa wani da daddai kamshi ya dakar mashi hanci wanda yayi sanadiyar saukar kasala ajikinshi. Lumshe ido yayi aranshi yanakara jin son Fulani.
Kwankwasa kofar yayi, da sauri Safeeya taje tabude. Dukawa tayi tana fadin ai har angama, murmushi yayi yace nagode, Jakadiya zata kawo maki tukuicinki. Godiya takara yimashi tafita. Yana shiga yayi mutuwar tsaye, ganin irin kyan da fulani tayi kamar ba mutum ba. Tasbihi yafarayi aranshi yana kara yabon irin kyan Fulani.
Zaune take tunda taji shigowarshi ta dukar da kanta, hannunshi taji ya zagaye mata kafadu dasu, saurin rufe ido tayi, mikar da ita yayi suna fuskantar juna, murmushi yayi ya matso da fuskarshi dede ta ta harsunajin numfashin juna, ahankali yace Fulanita babu gaisuwa? Saurin kwantar da kanta tayi bisa kirjinshi tana murmushi, kara rungumeta yayi sosai kamar ze maidata ciki, kamshin turaren da Gimbiya Suhailat tabama Safeeya tasa mata duk yafara rikitashi.
Gurin Sarkin fada tawuce, abinda yafaru tafada mashi, sosai suka shiga tashin hankali. Sarkin Fada yace kina ganin Sarki baze iya samun haihuwa da wannan yarinyar ba kuwa? Kinsan fa ance larabawa albarka garesu. Jakadiya tace kada kadamu nasan abinda zanyi, damma Sarki yace ba,a gurina zata zauna ba da tunkafin tashiga gidanshi zanyi kokarin hanata haihuwa, amma kasan ni amintattar Sarkice dan haka kome nakai zesata taci, dan haka kada kadamu inde ina raye bazan bar Sarki yaga kwanshi aduniya ba. Shekarata nawa ina mashi hidima amma haryanzu nakasa zama wata acikin gidan nan, haka zankare a Jakadiya?.
Sede inzama fitila ina haska wasu ni ina kona kaina, ai rashin gata ba hauka bane, dan haka gara kowa yayita zama ahaka, shima wannan yaron dande ka hanani dayanzu na aiwatar mashi. Sarkin fada yace kiyi hakuri wannan yaron yashiga rai na, Allah yasani badan so nafara daukarshi ba, amma daga baya yashiga raina sosai, dan haka kibarshi, ninasan ko Sarki yamutu sede Qaseem yahau kujerarshi bade Areef ba, dan haka mutsaya akan sarki da matanshi. Yanzu kije ki kaima Gimbyar Baban Gida mugun labari, dannasan ita kadai zata shiga damuwa, banda Medaki, itakam ai tamu ce. Dariya Jakadiya tayi tace wlh bakada dama. Yace Allah kuwa kinsan daza,a bani Gimbiya medaki ai dana more, tun lokacin datazo gidan nan miyau na yabiya kawai senaji wai Sarki ze aureta. Jakadiya tace ai naga alamar itama yar hannu ce, amma matso kaji. Wata dariya suka kwashe da ita Sarkin fada yace kina ganin haka za,ayi? Tace sosai ma, amma bayanzu ba senan gaba idan komai ya zama dede.
Wani uban gumi ne yake fitowa daga jikin Gimbiya Zakiyya, kara kallon Jakadiya tayi tace yanzu jakadiya har saurin zuwa ki kawomun wannan bakin labarin kikeyi? Jakadiya tayi kasa da kai tace Allah yahuci zuciyarki, shima Sarki ba sonta yake ba, kawai tallarta Babanta yayi mashi, kuma kinsan Sarki dasaukin kai shiyasa ya amsa, amma dakanshi yafadamun ke kadaice macen dayakeso aranshi, duka sauran ya auresu ne abisa lalura. Dan haka ki kwantar da hankalinki.
Komawa tayi tazauna, saurin zuba mata ruwa jakadiya tayi tamika mata. Bayan tasha tace yanzu ya za'ayi kenan? Jakadiya tace Ranki yadade kamar yanda kika saba, hakan zakiyi, kinsan Sarki yana yabonki akan halayyarki tarashin tada hankali aduk lokacin dazeyi aure. Yace shiyasa yake kara sonki. Murmushi Gimbiya tayi tace shikenan, amma wannan karon bazan kyale wannan yarinyar ba. Jakadiya tace ai bazamu barita dadeba.
Ita kuwa Gimbiya medaki duk da taji haushi kadan amma ana bata magudan kudi tamanta da fushin. Jakadiya tace dama nasan bazaki damu ba, se waccan sarkin kishin, ita tana ganin kamar ita kadai sarki yakeso dan tafito daga gidan sarauta. Medaki tace aisetayi tayi nikam inde da kudi ya auri 10 ina ruwa na, nasan kawai zanrasa kulawar danake samu duk bayan kwana 2 , nasan hakanne kawai zedameni dan Sarki akwai iya shiga rai. Dariya Jakadiya tayi tace ai Gimbiya nasan matsalarki, kuma wannan badamuwa bace kede kawai kirikeni zaki samu yanda kikeso. Sarkin fada ma yanzu yaganni zanshigo nan yace ingaisheki, kinsan ke kadai yake gaidawa aduk matan gidan nan gaskiya yanaji dake. Medaki tayi dariya tace ai yana da kirki damma kada ace wani abu ai daya rika rakoki munashan labarai. Murmushi Jakadiya tayi tace ah, tunda kinaso ai angama.
Sati 2 Gimbiya Suhailat tadauka tana gyara Rayhana, takara kyau, sosai kyanta haryaso yayi yawa, tasha gyara sosai. Duk wata kissa Gimbiya ta koya mata, dayanda zata zauna da matanshi, babu abinda bata koya mata ba.
Duk wanda yakwana yatashi agarin Gombe babu wanda besan Sarki zeyi aure ba, gaggarumin biki aka shirya gidan kanshi yasha gyara, hankalin Gimbiya Zakiyya bakaramin tashi yayi ba, dan tagano irin son da Sarki yakema Rayhana, tun daga dukiyar dayake kashewa da kuma irin hidimar da taga Qaseem yanayi, wanda tasan shikanshi yana murna da bikin.
Taso ta tadama Sarki hankali akan auren, amma mamanta tanaji tahanata, tace bakida hankali Zakiyya? Kina ganin akan abinda yakeso baze iya wulakantaki ba? Tunwuri idanma wasu ne suke zugaki togara kidawo hanya, kina ganin nice karama acikin matan Abbanki amma yanzu nice nazama babba, dan haka banyarda kikara tada hankalinki akan auren nan ba. Kuma banyafe maki ba, idan har kika yarda wata tajaki kukaje gurin wani malami ko boka. Hakuri Gimbiya Zakiyya tayi ta bata kuma tayi mata alkawarin bazata je gurin kowa ba, kuma bazata kara tada hankalinta akan auren ba. Da haka ta kwantar da hankalinta, sede tayi alkawarin idan har tuggu da kissa suna sa mutum yaci riba zatayi amfani dasu takori Rayhana daga gidan Sarki.
Ayau ne miliyoyin jama'a daga jahohi daban daban da manyan sarakuna na garu ruwa suka halarci bikin Sarki Hasheem da Rayhana, wanda aka daura akan sadaki million 1, kowa yasheda wannan auren Soyayya ne Sarki yayi, ankashe dukiya sosai, anci ansha maroka da mawaka sun sami kyauta sosai. Adaren ranar Sarki da sauran Sarakuna da manyan masu kudi sukayi kayatattar walima ababban dakin taron masarautar Bubayero.
Bayan sungama kowa yanufi masaukinshi, kuma ranar aka kai amarya Rayhana dakinta dayasha dukiya kamar ba,a nigeria ba. Yayin da wasu suka cika da farin ciki alokacin Gimbiya Zakiyya tarasa inda zata sa kanta sbd tsabar bakin ciki. Jakadiya kuwa jan Sarkin Fada tayi suka nufi part din Medaki acan suka zauna suna bikinsu.
Nima nace yakamata abar amarya da Ango su sha amarcinsu.
Nagode sekunji ni a next page.😘.
Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 50⚜55
Washe gari. Basu suka tashi ba, se 8:00, dasauri Sarki yatashi ganin ko sallah basuyi ba, gaba daya kunyar fita yakeyi dan yasan kowa nagidan yasan baya fashin sallah amasallaci, babban abin kunya ma abokananshi sunce zasu biyo sugaisa da Amarya kafin su wuce, gashi nan yamakara.
Kallon Rayhana yayi wadda take kwance fuskarta tayi haske ga sahun kwallan datayi jiya nan kwance afuskarta. Murmushi yayi yashafi gashinta wanda ya hargitse, ahankali yace kece farin cikina GIMBIYA FULANI. Kiss yayi ma goshinta yatashi yaje yayi wanka yana fitowa yatada sallah, bayan yagama ya dauko Waya yakira Qaseem, yana dauka yace ai Yaya dayanzu zankiraka ince bakifa suna Falo harsun kusa gama karyawa. Sosa kanshi yayi yakara kallon Fulani yayi murmushi yace Uhm ka aika Safeeya taje takiramun Jakadiya tazo gurin Fulani nizan fita gurin baki.
Shiru yayi sannan yace amma Yaya meze hana kamaidata dakinta se inturo Safeeya tazo ta kula da ita, kasan bazata yarda Jakadiya ta kula da ita ba, tunda basu saba ba. Murmushi Sarki yayi yace shikenan to bari in maidata dama dan naga Jakadiya ita kadai keshiga dakina shiyasa nace haka amma yanzu zan maidata dakinta. Kashe wayar yayi kunya duk takamashi yanzu yazecema mutane.
Bayan yamaida Fulani dakinta wanda kofa ce kawai tarabasu da falon Sarki, duk abinda yakeyi tana jinshi kunya ce tahanata bude ido. Zama yayi yana kallonta, can kuma yatashi yafita yanufi gurin baki, akofa yahadu da Safeeya, cike da girmamawa ta durkusa tagaisheshi, amsawa yayi yana me mata fara'a. Yace yauwa Safeeya idan tashirya kaya suna nan su zata saka zasu gaisa da baki. Da to ta amsa mashi yayi waje, yana fita fadawa suka mara mashi baya suna kwasar gaisuwa.
Duk wanda yaganshi aranar yasan yana cikin farin ciki, dan duk yanda yaso yaboye fara'arshi kasawa yayi. Yana shiga falon baki suka fara yimashi tsiya, sosai yake dariya dayake yashigo cikin abokanshi. Wani Sarki yace gskya Hasheem bantaba ganin wannan farin cikin atare da kai ba, kada muna skul baka wannan fara'ar. Lallai baseka fada ba, kowa yasan yanzu ne kayi auren soyayya. Wani yace aidole yayi farin ciki wlh auren so daban yake, shiyasa banyi aure ba seda nasamu wadda nakeso. Haka sukayita barkwanci suna dariya, wani yace kaga kada muyi rana gara afiddo mana Amaryar data hanaka sallah amasallaci muganta muga wane irin zabe ne kayi haka. Dariya yayi yace a gaskiya sede muje Falona babu wanda ze fitomun da mata tana amarcinta tafito waje. Dariya suka saka yafita.
Abakin kofarshi yahadu da Jakadiya, saurin dukawa tayi tana mashi kirari, murmushi yayi yace Jakadiya kina lafiya? Tace lfy lau Rankai dade, dama tundazu naso inzo induba yakuka kwana sekuma naji ance badakai akayi sallah ba, shine nace to kobaku tashi dawuri ba?.
Murmushi yayi yace hakane, ai har Safeeya tazo tana gurin Fulani. Fulani? Jakadiya takara maimaita sunan aranta. Murmushi tayi tace to ai shikenan, bara inje ingyara dakin yace to. Dakin Fulani yawuce, tunkafin ya isa wani da daddai kamshi ya dakar mashi hanci wanda yayi sanadiyar saukar kasala ajikinshi. Lumshe ido yayi aranshi yanakara jin son Fulani.
Kwankwasa kofar yayi, da sauri Safeeya taje tabude. Dukawa tayi tana fadin ai har angama, murmushi yayi yace nagode, Jakadiya zata kawo maki tukuicinki. Godiya takara yimashi tafita. Yana shiga yayi mutuwar tsaye, ganin irin kyan da fulani tayi kamar ba mutum ba. Tasbihi yafarayi aranshi yana kara yabon irin kyan Fulani.
Zaune take tunda taji shigowarshi ta dukar da kanta, hannunshi taji ya zagaye mata kafadu dasu, saurin rufe ido tayi, mikar da ita yayi suna fuskantar juna, murmushi yayi ya matso da fuskarshi dede ta ta harsunajin numfashin juna, ahankali yace Fulanita babu gaisuwa? Saurin kwantar da kanta tayi bisa kirjinshi tana murmushi, kara rungumeta yayi sosai kamar ze maidata ciki, kamshin turaren da Gimbiya Suhailat tabama Safeeya tasa mata duk yafara rikitashi.