Sashe 24
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rufe fuska yayi yana dariya yace ai nafada masu, tace yauwa maganata tayi dede kenan? Adede lokacin da motar su Waziri da su Sarki tashigo harabar gidan, suna haskawa jikin wata bishiya suka haske fuskar Medaki, ai dasauri takara labewa, domin ta dade agurin jiran dama kawai takeyi tasamu tagudu, hannunta rike da dan kullinta, sede babu wanda yaganta daga Sarki Qaseem , se Waziri wanda dama shine yake jan motar, Sarki da Fulani suna baya, wani murmushi Waziri yayi , yawuce.
Bayan yayi parking motar yayi saurin fita yakirawo masu gadin gidan, ai Medaki tana ganin haka tayi surin komawa part dinta, kara jaddadamasu yayi akan su kula da tsaron gidan, kuma akulle kofa babu wanda ze kara shigowa bare fita.
Haka suka raka Sarki da Fulani har falo, Fulani ta kalli Waziri tarike kanta kamar me tunanin Sarki yace lafiya Fulani ko kanki yake ciwo? Kai ta girgiza, can kuma tayi saurin bude ido tace ina yarinyata? Sarki yace kina nufin kin haifi cikin jikinki kuma yana raye? Kai ta girgiza tace dan Allah kubani diyata wlh nasan na haihu, kada kucemun ta mutu.
Waziri yace ki kwantar da hankalinki, diyarki tana nan, araye asalima babu abinda yake rabaku, atare kuka zauna, babu abinda yasameta, sede yanzu tana gurin Gimbiya Suhailat, kuma nasan sun kwanta kinga dare yayi kibari seda safe zaki ganta.
Murmushin jin dadi tayi ta daga mashi kai, sallama sukayi masu suka fita. Sarki yace turani muje daki muyi wanka, murmushi tayi tafara turashi, atare sukayi wanka tana temaka mashi, bayan sunfito sukayi sallah sannan suka kwanta suna me cike da farin cikin ganin junansu, sun rungume juna kamar za,a rabasu.
Suna fita Waziri yakalli Sarki yace kaga abinda nagani kuwa? Sarki yace nagani, kabari kawai Allah yakaimu gobe nasan zamu gano sauran munafukan gidan nan. Sallama yayi mashi kowa yanufi part shi.
Washe gari da misalin karfe 10 Malam na darazo ya iso, aka saukeshi amasauki, bayan yagama cin abinci aka kawoshi fada, alokacin su Sarki Hasheem da fulani sun iso gurin tasha kyau sosai, tana zaune agefen Sarki, bayan sungama gaisawa da Malam, ya tambayi jikinshi yace Alhamdulillahi ai jiki yaya sauki, dama akwai dalilin dayasa kuma yanzu nasamu maganin akusa dani.
Dariya malam yayi yace to mungodema Allah, amma abinda nakeso da akai, sekayi hakuri da duk abinda zakaji ko zaka gani, ayanzu, nasan zaka shiga cikin damuwa, amma munaso mukawo karshen muna fukan gidan nan, kuma kaima nasan zaka so kasan wadan da sukayi ma Fulani haka.
Sarki yace hakane, babu komai, Allah yasa inji alkhairi. Malam yace amin, adede lokacin su Gimbiya Suhailat dasu beauty, Ayman, Jakadiya , Areef da Haisam suka shigo, ai beauty tana ganin Mamanta da gudu taruga tafada kanta tana dariya.
Itma tana ganinta tayi saurin rungumeta tna fadin yarinyata, Sarki da mamaki ya kamashi dasauri ya kalli fulani yace wannan ce diyata? Kai tacdaga mashi, besan lokacin da kwalla tacika mashi ido ba.
Waziri yabada umarnin afito dasu Jakadiya Karima, sannan yasa Jakadiya Safeeya takirawo su Gimbiya Zakiyyah da Medaki, wani bafade yasa yakirawo Baban Fulani da Baban Darazo, kowa yasamu guri yazauna yana kiran abinda za,ayi.
Nima nace bara in anje alkalamina injira shigowar su Sarkin Fada.
Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 100⚜105
Cikin isa da mulki Gimbiya Zakiyyah tashigo, ko sallama ma da kyar tayi, guri tasamu gefen Sarki tazauna, dan batasan yasamu lfy ba. Kallonshi tayi fuskarta dauke da murmushi tace barka da asuba memartaba yajikinka?.
Sanin ko anyi mashi magana baya amsawa yasa tadauke kanta bata kula da motsa bakin dayayi ba. Kallon malam tayi tace malam barka da asuba, yace yauwa kintashi lfy. Medaki ce tashigo jikinta duk yayi sanyi kamar antsamota daga ruwan zafi.
Akusa da bakin kofa tazauna duk tagama rudewa, cikin rashin jindadin abinda tayi Sarki Hasheem yace medaki dawo nan mana. Ai Gimbiya Zakiyyah batasan lokacin datace yaushe kafara magana memartaba?.
Murmushi yayi kawai yayi shiru, haryanzu babu wanda ya kula dasu Fulani, bayan medaki tazauna kusa da Gimbiya Zakiyyah, kallonta tayi tadan duko kusa da kunnanta tana murmushin mugunta tace ina fatan kinyi kwanciyar karshe agidan sarauta? Seki shirya karbar hukunci.
Sallamar su Sarkin fada da Jakadiya ne tasa Medaki tayi saurin tashi tana hawaye. Wani murmushin jindadi Sarki Hasheem yayi, ganin Jakadiyarshi, dama yana so ya tambayeta domin ita yakeso yayima albishir na samun diya da yayi, domin yasan tana daya daga cikin masu son yasamu karuwa.
Da fara,a yace Jakadiya matsonan infara baki albishir medadi, ai jitayi kamar yan hanjin cikinta zasu fito, kamar ance Fulani tadago kai, ai tana dagowa sukayi ido 4 da Sarkin fada. Wani irin ihu tasaka ta ture beauty, tashi tayi kamar zata ruga tana fadin gashi nan yazo zasu kasheni.
Waziri da Sarki Qaseem bakaramin mamakin abinda take fada sukayi ba, duk da dama suna zarginshi. Jakadiya Safeeya da Gimbiya Suhailat ne suka rike Fulani, Sarki Hasheem kuwa jiyayi kamar yatashi, gaba daya jikinshi rawa yakeyi, ganin haka Sarki Qaseem ya matsa kusa dashi yadafashi yana bashi baki.
Gimbiya Zakiyyah kuwa batasan lokacin data mike tsaye ba tana nuna Fulani, Medaki kuwa kukanta har yafito fili, duk da sanyi da falon yakedashi be hana zufa keto mata ba. Gaba daya sauran mutanen Falon sun shiga rudani, Areef kuwa matsawa yayi kusa da beautynshi yari keta sosai, yadora kanta saman kafadarshi, dan yasan batason hayaniya, ita kam kuka tasaka tunda Fulani ta tureta.
Malam da kanshi ya matsa kusa da Fulani datake kwance akan cinyar Jakadiya tana ta kuka, addu,a yafara yimata yana tofa mata. Sarkin fada kuwa da Jakadiya zaman yan bori sukayi suna rarraba idanu.
Sarki Qaseem ne yayi gyran murya sannan yace ya isa, kowa yasamu nutsuwa kuma azauna domin muyi abinda yakawomu. Malam yadade yanama Fulani addu,a kafin tasamu tadawo cikin nutsuwarta. Sarki Hasheem kam gaba daya kanshi yagama daurewa shiru kawai yayi yana karanta addu'oi, hakan yasa yafara samun nutsuwa, sede haryanzu idanunshi suna kan Jakadiyarshi data kasa kallonshi.
Bayan kowa ya nutsu Waziri yatashi yace ma malam yabude masu taro da addu,a. Bayan angama Waziri yafara magana. Alhamdulillahi da farko zanfara dayima Allah godiya daya kawomu wannan rana mecike da farin ciki da kuma bakinciki.
Da farko zanfara gabatar da matar Sarki, kuma amarya agurinshi wadda akafi sani da Fulani. Bayan shekaru 18 da wasu watanni bata gidan nan, inda aka samu wasu marassa imani suka shigo har cikin dakinta suka dauketa........ Sallamar Su Baban Fulani ce ta tsaida Waziri daga jawabin dayakeyi.
Fulani tana ganin Babanta ta tashi tanufi gurinshi, ai shima yana ganinta yabude hannuwa tashige jikinshi tana kuka. Shima kukan yakeyi seda suka bama kowa tausayi. Bayan sun natsu suka zauna, Baban beauty kuwa gaba daya mamaki yagama cikashi ganin abin al,ajabi.
Waziri yaci gaba da magana. Kamar yanda nace ba,asan wadan da sukazo suka dauke Fulani ba, amma tunda Allah yasa gata tadawo kuma tana cikin hankalinta. Kuma zata iya nuna wadanda suka aikata haka akanta to duk wanda yakasance cikin masu laifi, tabbas ze fuskanci hukunci me tsanani, kuma kowane irin matsayi gareshi a masarautar nan.
Ai kamar daga sama sukaji Medaki ta tashi tana fadin shikenan munshiga 3 wlh, ba laifina bane, duk kutsaya wlh zanfadi iyakar gaskiyar dana sani. Gimbiya Zakiyyah tayi wani murmushi aranta tace lallai zaki sha mamakina,ni nasan babu wanda zeyarda idan kikace hadani.
Waziri yayi murmushi yace rankiyadade munajinki. Tashi tayi tana kuka tafada masu duk abinda sukayi itadasu Gimbiya Zakiyyah, akan batan Fulani, sede bata fada masu abinda suke aikatawa da Sarkin fada ba.
Gaba daya falon aka dau salati, Sarki Hasheem kuwa zama yayi kamar dutse, kallon Jakadiya Karima kawai yake idanunshi na zubar da ruwa. Waziri yace da kyau, tashi Gimbiya Zakiyyah tayi tafara magana cike da mulki.
Inada ja agame da maganar Medaki, wannan maganar datayi kawai tafa deta ne sbd wani dalilinata, amma kowa yasan bana shiga harkar talakawa taya za,ayi inhada baki dasu mu aikata irin wannan shirmen.
wanda kowa yasan duk wanda yafito daga gidan sarauta bazeyi haka ba. Idan kuma har tace dani, ni nayarda sukawo sheda, idan har aka sameni da hannu aciki nayarda da duk wani hukunci daza,amun.
Waziri ya jinjina kai, alamar gamsuwa, ya kalli Medaki yace kina da wata shedar dazata nuna mana tana da hannu acikin abinda kika fada? Wata zufa ce takara keto mata, hawaye suna zuba a idonta tafara girgiza kai, tace a,a amma wlh dama tace zan gani....... kamar daga sama Sarkin fada yace nine shedar akwai ta acikin wannan aiki.
Kusan ma itace shugabarmu domin ita tasamu yin wannan aiki, kuma ni inada shedar dazata nunama kowa abinda ma bakusani ba, dama na ajeta sbd irin wannan rana. Ai Gimbiya Zakiyyah batasan lokacin data sauko kasa daga kan kujerar datake ba.
Anan Sarkin Fada yatashi yace tabbas ni nasan ayau asirina yagama tonuwa, dan haka banga dalilin bata maku lokaci ba, nasan Allah ya dade yana aramun rana, sede inaso kuyi hakuri da duk abinda zakuji, bakomai bane yasani aikata haka se SON ZUCIYA.
Wadda azamanin nayanzu shine abinda yake dawainiya da mutane da dama, wanda kuma bakowa bane yake saka mana son zuciya se shedan, da kuma mu kammu idan muka kasa tsarkake zuciyarmu.
Ban kasance mutum nagari ba a masarautar nan, na dade ina aikata abubuwa da dama, sede babu wanda yasani, harzuwa yanzu. Alokacin da aka haifi Yarima Areef, babban dalilin dayasa najawoshi jikina shine dan insalwantar da rayuwarshi, yazamana beda amfani arayuwa gaba daya.
Ada nayi niyar kasheshi sede shakuwar damukayi tahana ni, duk da Jakadiya Karima taso akasheshi, nine na hana. Babu irin maganin da ban bashi ba dan kawai inga yazamo dolo agidan nan amma hakan beyuwu ba, abu daya nasan yayi tasiri ajikinshi shine yanda bedamu da sarauta ba.
Alokacin daya girma se abun yadawo kaina, tunda yadawo daga karatu na lura bayason ganina, hakan yasa naja baya dashi. Amma sanin naci ribar cire mashi sarauta aranshi hankali na ya kwanta.
Wannan kenan.
Bayan yayi parking motar yayi saurin fita yakirawo masu gadin gidan, ai Medaki tana ganin haka tayi surin komawa part dinta, kara jaddadamasu yayi akan su kula da tsaron gidan, kuma akulle kofa babu wanda ze kara shigowa bare fita.
Haka suka raka Sarki da Fulani har falo, Fulani ta kalli Waziri tarike kanta kamar me tunanin Sarki yace lafiya Fulani ko kanki yake ciwo? Kai ta girgiza, can kuma tayi saurin bude ido tace ina yarinyata? Sarki yace kina nufin kin haifi cikin jikinki kuma yana raye? Kai ta girgiza tace dan Allah kubani diyata wlh nasan na haihu, kada kucemun ta mutu.
Waziri yace ki kwantar da hankalinki, diyarki tana nan, araye asalima babu abinda yake rabaku, atare kuka zauna, babu abinda yasameta, sede yanzu tana gurin Gimbiya Suhailat, kuma nasan sun kwanta kinga dare yayi kibari seda safe zaki ganta.
Murmushin jin dadi tayi ta daga mashi kai, sallama sukayi masu suka fita. Sarki yace turani muje daki muyi wanka, murmushi tayi tafara turashi, atare sukayi wanka tana temaka mashi, bayan sunfito sukayi sallah sannan suka kwanta suna me cike da farin cikin ganin junansu, sun rungume juna kamar za,a rabasu.
Suna fita Waziri yakalli Sarki yace kaga abinda nagani kuwa? Sarki yace nagani, kabari kawai Allah yakaimu gobe nasan zamu gano sauran munafukan gidan nan. Sallama yayi mashi kowa yanufi part shi.
Washe gari da misalin karfe 10 Malam na darazo ya iso, aka saukeshi amasauki, bayan yagama cin abinci aka kawoshi fada, alokacin su Sarki Hasheem da fulani sun iso gurin tasha kyau sosai, tana zaune agefen Sarki, bayan sungama gaisawa da Malam, ya tambayi jikinshi yace Alhamdulillahi ai jiki yaya sauki, dama akwai dalilin dayasa kuma yanzu nasamu maganin akusa dani.
Dariya malam yayi yace to mungodema Allah, amma abinda nakeso da akai, sekayi hakuri da duk abinda zakaji ko zaka gani, ayanzu, nasan zaka shiga cikin damuwa, amma munaso mukawo karshen muna fukan gidan nan, kuma kaima nasan zaka so kasan wadan da sukayi ma Fulani haka.
Sarki yace hakane, babu komai, Allah yasa inji alkhairi. Malam yace amin, adede lokacin su Gimbiya Suhailat dasu beauty, Ayman, Jakadiya , Areef da Haisam suka shigo, ai beauty tana ganin Mamanta da gudu taruga tafada kanta tana dariya.
Itma tana ganinta tayi saurin rungumeta tna fadin yarinyata, Sarki da mamaki ya kamashi dasauri ya kalli fulani yace wannan ce diyata? Kai tacdaga mashi, besan lokacin da kwalla tacika mashi ido ba.
Waziri yabada umarnin afito dasu Jakadiya Karima, sannan yasa Jakadiya Safeeya takirawo su Gimbiya Zakiyyah da Medaki, wani bafade yasa yakirawo Baban Fulani da Baban Darazo, kowa yasamu guri yazauna yana kiran abinda za,ayi.
Nima nace bara in anje alkalamina injira shigowar su Sarkin Fada.
Ur's
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 100⚜105
Cikin isa da mulki Gimbiya Zakiyyah tashigo, ko sallama ma da kyar tayi, guri tasamu gefen Sarki tazauna, dan batasan yasamu lfy ba. Kallonshi tayi fuskarta dauke da murmushi tace barka da asuba memartaba yajikinka?.
Sanin ko anyi mashi magana baya amsawa yasa tadauke kanta bata kula da motsa bakin dayayi ba. Kallon malam tayi tace malam barka da asuba, yace yauwa kintashi lfy. Medaki ce tashigo jikinta duk yayi sanyi kamar antsamota daga ruwan zafi.
Akusa da bakin kofa tazauna duk tagama rudewa, cikin rashin jindadin abinda tayi Sarki Hasheem yace medaki dawo nan mana. Ai Gimbiya Zakiyyah batasan lokacin datace yaushe kafara magana memartaba?.
Murmushi yayi kawai yayi shiru, haryanzu babu wanda ya kula dasu Fulani, bayan medaki tazauna kusa da Gimbiya Zakiyyah, kallonta tayi tadan duko kusa da kunnanta tana murmushin mugunta tace ina fatan kinyi kwanciyar karshe agidan sarauta? Seki shirya karbar hukunci.
Sallamar su Sarkin fada da Jakadiya ne tasa Medaki tayi saurin tashi tana hawaye. Wani murmushin jindadi Sarki Hasheem yayi, ganin Jakadiyarshi, dama yana so ya tambayeta domin ita yakeso yayima albishir na samun diya da yayi, domin yasan tana daya daga cikin masu son yasamu karuwa.
Da fara,a yace Jakadiya matsonan infara baki albishir medadi, ai jitayi kamar yan hanjin cikinta zasu fito, kamar ance Fulani tadago kai, ai tana dagowa sukayi ido 4 da Sarkin fada. Wani irin ihu tasaka ta ture beauty, tashi tayi kamar zata ruga tana fadin gashi nan yazo zasu kasheni.
Waziri da Sarki Qaseem bakaramin mamakin abinda take fada sukayi ba, duk da dama suna zarginshi. Jakadiya Safeeya da Gimbiya Suhailat ne suka rike Fulani, Sarki Hasheem kuwa jiyayi kamar yatashi, gaba daya jikinshi rawa yakeyi, ganin haka Sarki Qaseem ya matsa kusa dashi yadafashi yana bashi baki.
Gimbiya Zakiyyah kuwa batasan lokacin data mike tsaye ba tana nuna Fulani, Medaki kuwa kukanta har yafito fili, duk da sanyi da falon yakedashi be hana zufa keto mata ba. Gaba daya sauran mutanen Falon sun shiga rudani, Areef kuwa matsawa yayi kusa da beautynshi yari keta sosai, yadora kanta saman kafadarshi, dan yasan batason hayaniya, ita kam kuka tasaka tunda Fulani ta tureta.
Malam da kanshi ya matsa kusa da Fulani datake kwance akan cinyar Jakadiya tana ta kuka, addu,a yafara yimata yana tofa mata. Sarkin fada kuwa da Jakadiya zaman yan bori sukayi suna rarraba idanu.
Sarki Qaseem ne yayi gyran murya sannan yace ya isa, kowa yasamu nutsuwa kuma azauna domin muyi abinda yakawomu. Malam yadade yanama Fulani addu,a kafin tasamu tadawo cikin nutsuwarta. Sarki Hasheem kam gaba daya kanshi yagama daurewa shiru kawai yayi yana karanta addu'oi, hakan yasa yafara samun nutsuwa, sede haryanzu idanunshi suna kan Jakadiyarshi data kasa kallonshi.
Bayan kowa ya nutsu Waziri yatashi yace ma malam yabude masu taro da addu,a. Bayan angama Waziri yafara magana. Alhamdulillahi da farko zanfara dayima Allah godiya daya kawomu wannan rana mecike da farin ciki da kuma bakinciki.
Da farko zanfara gabatar da matar Sarki, kuma amarya agurinshi wadda akafi sani da Fulani. Bayan shekaru 18 da wasu watanni bata gidan nan, inda aka samu wasu marassa imani suka shigo har cikin dakinta suka dauketa........ Sallamar Su Baban Fulani ce ta tsaida Waziri daga jawabin dayakeyi.
Fulani tana ganin Babanta ta tashi tanufi gurinshi, ai shima yana ganinta yabude hannuwa tashige jikinshi tana kuka. Shima kukan yakeyi seda suka bama kowa tausayi. Bayan sun natsu suka zauna, Baban beauty kuwa gaba daya mamaki yagama cikashi ganin abin al,ajabi.
Waziri yaci gaba da magana. Kamar yanda nace ba,asan wadan da sukazo suka dauke Fulani ba, amma tunda Allah yasa gata tadawo kuma tana cikin hankalinta. Kuma zata iya nuna wadanda suka aikata haka akanta to duk wanda yakasance cikin masu laifi, tabbas ze fuskanci hukunci me tsanani, kuma kowane irin matsayi gareshi a masarautar nan.
Ai kamar daga sama sukaji Medaki ta tashi tana fadin shikenan munshiga 3 wlh, ba laifina bane, duk kutsaya wlh zanfadi iyakar gaskiyar dana sani. Gimbiya Zakiyyah tayi wani murmushi aranta tace lallai zaki sha mamakina,ni nasan babu wanda zeyarda idan kikace hadani.
Waziri yayi murmushi yace rankiyadade munajinki. Tashi tayi tana kuka tafada masu duk abinda sukayi itadasu Gimbiya Zakiyyah, akan batan Fulani, sede bata fada masu abinda suke aikatawa da Sarkin fada ba.
Gaba daya falon aka dau salati, Sarki Hasheem kuwa zama yayi kamar dutse, kallon Jakadiya Karima kawai yake idanunshi na zubar da ruwa. Waziri yace da kyau, tashi Gimbiya Zakiyyah tayi tafara magana cike da mulki.
Inada ja agame da maganar Medaki, wannan maganar datayi kawai tafa deta ne sbd wani dalilinata, amma kowa yasan bana shiga harkar talakawa taya za,ayi inhada baki dasu mu aikata irin wannan shirmen.
wanda kowa yasan duk wanda yafito daga gidan sarauta bazeyi haka ba. Idan kuma har tace dani, ni nayarda sukawo sheda, idan har aka sameni da hannu aciki nayarda da duk wani hukunci daza,amun.
Waziri ya jinjina kai, alamar gamsuwa, ya kalli Medaki yace kina da wata shedar dazata nuna mana tana da hannu acikin abinda kika fada? Wata zufa ce takara keto mata, hawaye suna zuba a idonta tafara girgiza kai, tace a,a amma wlh dama tace zan gani....... kamar daga sama Sarkin fada yace nine shedar akwai ta acikin wannan aiki.
Kusan ma itace shugabarmu domin ita tasamu yin wannan aiki, kuma ni inada shedar dazata nunama kowa abinda ma bakusani ba, dama na ajeta sbd irin wannan rana. Ai Gimbiya Zakiyyah batasan lokacin data sauko kasa daga kan kujerar datake ba.
Anan Sarkin Fada yatashi yace tabbas ni nasan ayau asirina yagama tonuwa, dan haka banga dalilin bata maku lokaci ba, nasan Allah ya dade yana aramun rana, sede inaso kuyi hakuri da duk abinda zakuji, bakomai bane yasani aikata haka se SON ZUCIYA.
Wadda azamanin nayanzu shine abinda yake dawainiya da mutane da dama, wanda kuma bakowa bane yake saka mana son zuciya se shedan, da kuma mu kammu idan muka kasa tsarkake zuciyarmu.
Ban kasance mutum nagari ba a masarautar nan, na dade ina aikata abubuwa da dama, sede babu wanda yasani, harzuwa yanzu. Alokacin da aka haifi Yarima Areef, babban dalilin dayasa najawoshi jikina shine dan insalwantar da rayuwarshi, yazamana beda amfani arayuwa gaba daya.
Ada nayi niyar kasheshi sede shakuwar damukayi tahana ni, duk da Jakadiya Karima taso akasheshi, nine na hana. Babu irin maganin da ban bashi ba dan kawai inga yazamo dolo agidan nan amma hakan beyuwu ba, abu daya nasan yayi tasiri ajikinshi shine yanda bedamu da sarauta ba.
Alokacin daya girma se abun yadawo kaina, tunda yadawo daga karatu na lura bayason ganina, hakan yasa naja baya dashi. Amma sanin naci ribar cire mashi sarauta aranshi hankali na ya kwanta.
Wannan kenan.