← Book details A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 18 OF 33

Sashe 18

A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jakadiya tace kwarai ma kuwa, ai tunda basu cikin gidan nan hankalina ai yakwanta. Gimbiya Zakiyyah tace se akara kula. Medaki datake dariya aciki takara kallon Jakadiya wadda jikinta yayi sanyi, aranta tace lallai Jakadiya yar duniya ce, aifa sekayan marmarin, Sarkin Fada ai yamafisu komai. Gimbiya Zakiyyah tace yanzu fa idan Sarki yafadi ya mutu shikenan munzama yan kallo agidan sarauta ko?

Medaki tace nima nayi wannan tunanin anya babu saka hannun kaninshi arashin warke warshi kuwa? Ace ciwo shekara 18 harda watanni amma be warke ba. Kiduba fa kiga yanda yaki yarda afitar dashi waje, kullum seyarika fadin wai yace baya so, to mutumin da baya magana taya zece bayaso?

Jakadiya tace nizan fada maku haka, nida ake komai agabana, aduk lokacin da za,ayima Sarki gashi ko za,a bashi magani, daga Sarki Qaseem se Waziri kadai suke shiga dakin, nima nasan akwai abinda suke kullawa, kalli yanda Waziri da Sarki suka hade kansu, kullum yana manne dashi, Sarkin fada beda wani anfani agurinsu.

Gimbiya Zakiyyah tace, to gaskiya bazan yarda ba, daga yanzu inaso kirika saka idanu akan duk wani abu dasukeyi, tunda kowa yasan kece makusanciyar Sarki, dole subarki kizauna tare dashi. Jakadiya tace angama Gimbiya, tashi tayi tace nizan koma. Medaki tace nagode, kigaida gida sena shigo.

Inajinka Yarima fadamun kasande babu abinda bazan iya yimaka ba, dan farin cikinka. Shiru yayi yana sosa kai, Haisam yace Aunty wlh beauty yakeso, tunda nake da Areef bantaba jin yayi maganar wata ba, amma aranar dayafara haduwa da beauty beda magana se tata, kumani tun alokacin nagane yafada soyayyarta, amma sanin halin iyayenshi yasa yayi shiru.

Jakadiya Safeeya tace, na jima dasanin haka, sede akwai abinda nakeso kasani, idan har kanason yar Baba dole Kaboye ma Iyayenka harse zuwa wani lokacin daya kamata, banaso azo ahada tashin hankali, wanda zeyi sanadiyar rushewar zumunci. Areef yace Aunty akwai wani zumunci atsakaninki dasu Abba ne? Saurin girgiza kai tayi tace bahaka nake nufi ba, kaide kawai kayi yanda nace, kawai kanuna masu kana nema nan da dan lokaci komai zezo karshe.

Areef yace amma Aunty yanaga kamar beauty ba irin ta yan nigeria bace, gsky kyanta yawuce misali. Rasa mezata ce mashi tayi, tace kasan dangin mamarta ba yan nan bane, buzaye ne. Areef yayi murmushi yace haba shiyasa. Amma haka aka haifeta bataji, tomeyasa ba,a kaita asibiti ba? Jakadiya tace gsky ba,a kaita asibiti ba, kuma banaso kace zaka kaita ayanzu, idan lokaci yayi seka kaita, nima inaji ajikina kamar zata warke. Haisam yace mungode Aunty Allah yabiyaki, tace amin, tashi yayi yace bara inje inbada hakuri.

Jakadiya tace, a,a nasan tayi bacci kabarta kawai anjima sekadawo. Haisam yace malam muje akwai inda nakeso muje, sallama sukayi mata suka fita. Ajiyar zuciya tayi tace Allah katona asirin mutanen dasukayi wannan abu kowa yahuta, nasan Gimbiya zakifi kowa farin cikin zabin da Yarima yayi, sede ina tsoron zuwan Ayman kada ahada rigima, nasan duk mun son da kikema Fulani bekai na yar uwarki ba. Tashi tayi tashiga dakin Fulani.

Zama tayi takura mata ido tana kwance tana bacci, tace tabbas wahala tana canzama mutum kamanni, nayi mamakin yanda banganeki ba tun farko, amma ba abun mamaki bane, sbd irin wuyar da kikasha ashekaru 18 ko Sarki baze iya ganekiba. Fita tayi tanufi dakin beauty.

Jawota tayi tana fadin haba yar leleta, yihakuri, yace zedawo anjima ai, kobakison yadawo? Kaita girgiza tana turo baki, dariya Jakadiya tayi tace, shikenan, tashi muyi wata magana me amfani, tashi tayi tazauna tare da dora kanta bisa kafadar Jakadiya, murmushi tayi tace Sarkin son jiki, to kinsan menakeso infada maki? Daga yau banason inkara ganin Yarima yazo kinhau jikinshi, ko hannunshi banaso kitaba, kinsan nafada maki babu kyau kataba namijin da ba,a maku aure ba ko? Dan haka yanzu yace yana sonki, kuma aurenki zeyi.

Tokinga duk macen da akace anaso bazata kara bari saurayinta yataba taba harse an daura aure, kinji ko? Kai tadaga tana rufe fuska, Jakadiya tace kobaki sonshi, dasauri tayi mata alamun a,a dariya tayi tace kamar gaske keda bakisan wani so ba. To inde kinasonshi idan yazo kirika zama nesa dashi kinji? Ta daga kai. Jakadiya tace yauwa tashi kidauko Fikhu mucigaba da karatunmu.

Shiru Sarkin fada yayi yana jin bayanin Jakadiya karima, harta gama yayi dariya yace lallai, wato nine ma kayan marmarin? Amma kinhadu, wlh kamar nasani inazuwa nace mata sauri nakeyi. Ita kuma Gimbiya dan tasamu ance ana gaisheta zata fadamun haka. To wlh tunda miyau na yabiya da ita kota halin yaya senasha romonta. Jakadiya tace wlh bakada dama, wato duk matan Sarki seka more? Yace kede muje zuwa kawai.

Washe gari tunda safe aka shiga da Sarki Hasheem dakin gashi, inda sabon likitan yafiddo kayan aiki masu nagarta yafara yimashi gashi dasu, Sarki Qaseem da Waziri se addu,a sukeyi Allah yasa adace. Jakadiya Karima ce tayi sallama tashigo falon, bayan tamika gaisuwarta da tambayar me jiki, tace dazu naga wani bature shine nace ko bako mukayi ne?

Waziri yace abokin Sarki ne, tace aiyo, nace memartaba ko wanka akemashi ne? Waziri yace dan Allah kifita koma menene idan angama za,a kiraki, tashi tayi tana cewa to to afito lafiya, da harara yarakata aranshi yana fadin tabbas abinda zuciyata take fadamun akanki yafara zama gaskiya, amma muje zuwa nasan lokacin yataho. Sarki yace meyasa baka fada mata gaskiya ba, kasan aduk gidan nan babu wadda Yaya yakeso kamarta, Yanda muka dauketa kamar Uwa take agaremu dan mundade da ita. Waziri cike da takaici yace nasani, kawai banason yawan magana ne kasan addu,a mukeyi shiyasa nace mata haka dan karta katsemu. Kallonshi Sarki yayi badan ya yarda da abinda yafada ba.

Sarkin fada ne zaune adakinshi hannunshi rike da wani abu yana kallo yana murmushi, yace Gidan sarauta babu gsky, nasan wata rana dole asirinmu zetonu, akullum idan bayi suka hada kai da yan sarauta karshe sune masha wuya, nasan mu munfi bayi matsayi, amma kuma kaskantattau Gimbiya take daukarmu agidan nan, ranar tonan asiri aranar zakamun rana. Dariya yayi yamaida abun cikin jakarshi yana fadin wai Sarkin Fada? Kode Sarkin tsiya? Wata dariya yayi yace koni ina tsoron kaina.

Seda Ayman takwana 1 dazuwa sannan suka hadu da Areef, yafito da yamma cikin shirin fita afalo yagansu zaune, Areef yace kai, Momy yaushe Ayman tazo bansani ba? Murmushi tayi tace kana can gurin Haisam kuma sanda kadawo tayi bacci, dasafe kuma kafita aiki bata tashi ba, dama cewa nayi zaka ganta da idonka. Dariya yayi yazauna yana fadin mutanen misrah tace Yaya Areef inakwana, yace lfy lau, kinzo lafiya ya yan gidan? Tace lafiya lau suna gaisheka, yace to ina tsarabata? Tace tana nan, yace yauwa bari inje Haisam yana jirana idan nadawo zan karba.

Momy tace inazakuje? Yace wlh kawai zamufita garine, tace to ai dakuntafi tare itama taga garin, yace hakanefa taso muje kiga birni, dariya tayi tace wane birnin kuma, fita sukayi suna fadin semun dawo Momy. Da kallon sha,awa tabisu tana murmushi, tare da fadin Allah kasa su hada kansu amin.

Tare suka jero har bakin motar da Haisam yake tsaye yana jiranshi. Idanu Haisam yaware yana kallon Ayman wadda taketa dariya ita da Areef, gaba daya tagama tafiya dashi, suna zuwa gaban motar Areef yace yi hakuri kaga wadda ta tsaidani nan, se alokacin itama ta kula dashi. Idanu itama tazuba mashi tana kallonshi cike da burgewa, gaba daya yagama tafiya da ita. Areef ya tsaya yana kallon Haisam wandda bemasan abinda yakeyi ba, juyawa yayi yakalli Ayman, itama mamaki tabashi yanda ta tsaya tana kallon Haisam, dariya Areef yayi ya harde hannuwa akirji tare da jingina jikin mota yana fadin ikon Allah.

Nima nace Ikon Allan gaske, Areef tayani gani.

Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]

Season 80 ⚜85

Da karfi Areef yabugi kafadar Haisam yana dariya, cikin sauri Haisam da Ayman suka dawo cikin hankalinsu, kunya duk takamata ganin Areef yagane kallon dasukeyi, cikin dakewa Haisam yace wlh kai dan iska ne, ni nayima haka lokacin dakaga Beauty?.

Dariyar da yakeyi ya dena yana fadin ai gani nayi kunmaida ni dan kallo, Haisam yajuya yakara kallon Ayman wadda ta sadda kanta kasa tana wasa da yatsunta, murmushi yayi yace yaushe kukayi bakuwa bansani ba?.

Areef yace kaide kashiga mota muje, kuma kabani key din, Haisam yace saboda? Areef yace kaima kasan bazan shiga tukinka yanzu ba, idan ko zaka tuka to wlh sede acire center mirrior. Dariya Haisam yayi ya cilla mashi key din, yana fadin ai se inzauna baya kaga nahuta da waige.

Tunda suka fara tafiya Haisam yakasa zama dede, ita ko duk kunya takamata, da kyar ta iya gaishe shi. Haisam yace lfy lau kinzo lfy? Tace lafiya lau, Areef yace malam yazaka barni ina tuki karika juyawa gurinta anbarni sekace driver. Dariya Haisam yayi yace Allah yabaka hakuri Yaya Babba.

Dariya Areef yayi, yace kaji munafunci, zakayi bayani ne. Wani gurin shakatawa sukaje, bayan yayi parking suka sami guri suka zauna, haryanzu Haisam yakasa dauke idonshi akan Ayman. Jan Areef yayi gefe, anan yace dan Allah abokina ina kasamo wannan me kyan? Dariya Areef yayi yace diyar Yayar Momy ce fa, jiya tazo, nima seyau naganta shine Momy tace mufito tare. Ajiyar zuciya yayi yace Allah yasa wani beriga ni ba, kasan Allah? Alokacin dana ganta jinayi numfashina yana neman tafiya.

Bantaba haduwa da macen data tafi dani alokaci guda ba, se Ayman, kuma yanzu ba se anjima ba, zanshigar da kaina. Areef yace ai bazaka sha wahala ba, dan naga itama ta kyasa. Haisam yace muje munbarta ita kadai, Areef yace kawaide kutashi mutafi gida nima wlh beauty na nakeson gani. Haisam yace dan Allah kabani 5 minutes ya isa.

Cikin wani shopping complex Areef yashiga, haka yayi ta daukarma Beauty kayan lashe lashe. Zama Haisam yayi akan kujerar datake fuskantar Ayman, shiru yayi yana kallonta har nawani lokaci, ahankali cikin murya mecike da so yakira sunanta da Angel. Seda taji wani Yarrr alokacin dataji sunan, kara dukar da kanta tayi tana murmushi.
Chapter 18 · 0% Book details