← Book details A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 33 OF 33

Sashe 33

A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 2 min read

Se nace mata tomiyasa tacemun beauty? Kasan metace? Wai nima inada kyau shiyasa kake cemun haka. Dariya yayi yace ai bata fadi karya ba. Kuma nibazan iya dena cemaki beauty ba, domin sunan yadace dake, alokacin dabansan sunanki ba, kawai naga beauty ne kadai yadace dake. Kuma Fahad da gaskiyarshi, nima bakiga lokacin da Haisam yana cemaki beauty ba nahanashi.

Ai sunan dakake kiran masoyinka dashi, kai kadai yakamata ka fadeshi. Murmushi tayi tace Allah yanuna mana muga girman su fahad, Areef yace aini tunyanzu nabama Fahad Khairat.

Dariya tayi tace duniya komai mewucewa. Allah ne yayi zanrayu, gashi yanzu wai harnice da yara 2. Kamar banice aka haifa AMAKABARTA BA. Daure fuska Areef yayi yace banaso inkarajin wannan maganar abakinki, kinaso au Khairat su san wannan labarin ne? Duk wani da nagari bazeso yaji wannan bakin labarin ba, kuma ace da mahaifiyarshi yafaru. Daga yau na kashe wannan labarin na AMAKABARTA AKA HAIFEKI.

Murmushi tayi takama kunnanta tace afuwan Habibina, insha Allahu daga yau bazan kara cewa AMAKABARTA AKA HAIFENI ba. Jawota yayi ya rungumeta yana fadin yauwa BEAUTY NAH!!!!!!

ALHAMDULILLAH!!!

Ina godiya ga Allah (s.w.a) daya kawoni karshen wannan littafi nawa na AMAKABARTA AKA HAIFENI.

Abinda nafada da kuskure Allah ya yafemani, kuma banyi wannan labari ba, dan cin zarafin masu aikata irin wannan laifi. Nayishine domin yazama darasi ga mutane.

Ina mika sakon jinjina da godiya ga duk kanin masoyana, Allah yabar zumunci da kauna, nagode da irin kaunarku agareni.

Se kunjini alittafina nagaba me suna . DARAJAR MUHALLI.

SADAUKARWA GA FAMILIES OF LATE RABI'U IDRIS ZANGO

UR'S.

NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
08028525263
Chapter 33 · 0% Book details