Sashe 15
A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gimbiya tace hakane, amma nafison yabi zabin dana yimashi, diyar yayata nakeso ya aura,duk da ban fada masuba, banaso infada masu Yarinyar tasa abun aranta, nasan bayanzu zatayi aure ba,shiyasa nayi shiru harseya amince, sannan nayi masu magana. Jakadiya tace bakomai Allah yashige mana gaba, nima zanyi mashi magana tunda de besamu wadda yakeso seya auri zabinku, idan yaso daga baya seya auri zabinshi. Gimbiya tayi murmushi jin dadi tace shiyasa nake sonki. Allah yayi mana zabi nagari.
Da yamma kamar yanda Waziri yace, haka yasa driver yadauki Jakadiya Safeeya yanufi kasuwa da ita, acan tasiya masu kayan amfani dayawa, sede yawan siyayyar duk ta Yar Baba tafi yawa, kananan kaya ma duk nata sunfi yawa, dasauran kayan amfani na yan mata. Data gama suka wuce gurin tela, anan tayi mashi bayanin yanayinsu tabiya kudin dinki yabata ranar karba.
Jakadiya Karima ce zaune afalon Gimbiyar Babbar Gida tare da Medaki, Gimbiya tace waini Jakadiya kina kula da Suhailat kuwa? Kada fa ta shammacemu kamar yanda Rayhana tayi mana. Jakadiya tace haba Ranki yadade ai ita da haihuwa sede alahira, kada kidamu bazan baki kunya ba. Murmushi tayi tace, haka nakesonji.
Medaki tace bari intashi inje nasan yanzu angama shirya Sarki inje induba jikinshi, yamutsa fuska Gimbiya tayi ta kauda kai, Jakadiya tace afito lafiya Gimbiya. Tana fita Gimbiya taja tsaki tace aikin banza kamar wata tsiya zata iya yimashi, ni wannan mata tsau tsayi ne kawai yasa Sarki ya aureta, shide talaka duk yanda akayi dashi baya iya sakewa. Shiru de Jakadiya tayi bata ce komai ba, tashi tayi tace bari inje gurin Sarkin Fada.
Koda Jakadiya Safeeya takoma part dinta har lokacin maman Yar Baba bata tashi daga baccin datakeyi ba, saboda acikin maganin da likita yabata akwai mesa bacci, dan yace idan tana yawan bacci kwakwalwarta zatafi samun hutu, YarBaba kuwa tana zaune tana kallo.
Jakadiya tace Yar baba zokiga wani abu, tashi tayi tamatsa kusa da ita tazauna tare da jingina da jikinta, jakadiya Tayi murmushi tace, hmmm ke kam mage ma nan taganki tabarki inde gurin sonjiki ne. Dariya Yar Baba tayi takara kwantawa jikinta.
Kayan tafiddo tafara nuna mata, hada inner wears duk tarika gwada mata yanda ake saka su, se murna Yar Baba takeyi, Jakadiya tace zankoya maki yanda ake amfani dasu duka, kuma kinsande nafada maki banason kazanta ko? Kai ta daga mata, tace yauwa, yanzu tashi muje ciki kiyi wanka semu fara.
Ranar litinin Areef yafara zuwa office, aranar duk macen data ganshi se miyanta ya tsinke, sbd kyawun da yayi, tare suke da Haisam, Areef yace nifa nafara tsarguwa, naga se kallona akeyi. Dariya Haisam yayi yace kada kadamu sunga dan saurayi me kyau ne. Duka ya kaimashi yana fadin kai dan iska ne, yace emana kasani ko anan kasamu zabinka tunda babu yar gidan sarauta acikinsu.
Areef yace Allah ya kyauta, anfada maka ni matata zatayi aiki ne, lallai ma, kai bakasan irin macen danake so na aura ba. Kawaide katayani da addu,a. Haisam yace ato idan kuma nizan rigaka aishikenan,Areef yace nima zanfi son haka, da haka suka isa Office dinsu.
Jikin Sarki Hasheem yafara sauki sosai sbd yanzu yanashan magani tunda yaji maganar da Malam yayi, kuma yana cin abinci sosai, hakan yasa Sarki Qaseem yace afara fita dashi fada hakan zerika rage mashi zaman kadaicin dayakeyi.
Haka suka cigaba da rayuwa agidan Sarki, babu wanda yasan dazamansu, aduk lokacin da Baba yaso ganin Yar Baba yakanje yaganta susha fira, har mamakin ganin yanda tacanza cikin lokaci kadan yakeyi, gashi tsafta agurinta kamar da ita aka halicceta, akullum setayi wanka so 3 kuma ko sallah tayi setayi kwalliya, Jakadiya safeeya kam har mamakin saurin fahimtar datake da ita take, kome takoya mata ba wuya tadaukeshi.
Akullum da dare kafin su kwanta se sunyi karatun littattafai, dan zaman datayi takara sanin abubuwa dayawa agurin Jakadiya safeeya, harta da girki tafara koya mata, sbd tace idan bata nan setarika dafa masu. Duk da ankawo dinkunansu amma bata son saka atamfa ko less, tafison tasa kananan kaya, Mamanta kuwa tunda takeshan magani, yanzu haukanta da sauki, batayin komai, sede tazauna tayi shiru idan kuma kaga tana dariya to ita da yarta ce, duk da baccinta yafi yawa akan idonta biyu.
Zaune Areef da Haisam suke acikin lambu suna hutawa, babu kowa agurin, danshi Areef becika son fadawa suna binshi ba, yafison daga shi se Abokinshi Haisam wadda yakasance da ga dupty gvernor na gombe, kuma tare sukayi karatu dashi.
Yar Baba tana gama kwalliya tafito dasauri dan ta nuna ma Jakadiya dan tasan bata fita ba, tana zuwa falo taga bata nan, kitchen tashiga nan ma bata ganta ba, turo baki tayi dantagane tafita, hanyar dataga tana bi tashigo ko tafita tabi, tana zuwa ta tura kofar cikin sa,a tajita abude, murmushi tayi tafita.
Cike da tsoro tafara takawa tana bin cikin lambun, swimming pool tagani kallonshi tayi. Taci gaba da tafiyarta, can taji dawisu yafara kuka, ai batasan lokacin data juya dagudu zata koma inda tafito ba, cikin rashin sa,a tayi tuntube da dutse kawai tafada cikin ruwan.
Su Areef dasuke zaune nesa da ruwan sukaji karar wani abu acikin ruwa, koda Areef yakai kallonshi ga ruwan kawai yaga mutum yana ta daga hannu da kafa acikin ruwa. Cikin sauri yatabo Haisam yana nuna mashi, duk da basu san kowaye ba, Dasauri suka nufi bakin ruwan.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady )
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 70 ⚜75
Babu bata lokaci Yarima Areef ya fada cikin ruwan, yana zuwa kusa da ita yadaukota, alokacin tasha ruwa harta suma, fitowa yayi daga ruwan tana rungume ajikinshi, abisa kafet din dasuke zaune yakwantar da ita yadora kanta saman cinyarshi, Haisam yana biye dashi duk sun rude.
Kallon tsoro, mamaki suka farayi mata, addu.a duk wadda tazo bakin Areef yinta yakeyi danshi gani yake kamar ba mutum bace. Haisam yace Areef bakada hankali kana ganin kamar ba mutum ba amma zaka dorata akan cinyarka? Tunda de kacirota tashi mutafi, fara jan hannun Areef yayi.
Areef da jikinshi yagama mutuwa sbd tsabar firgici bema san yanayi ba. Da karfi yajashi sannan yadawo hankalinshi, katashi mubar gurin nan, nidama can nafara zargin gurin, gashi yanzu munfara gani. Areef yafara girgiza kai, yamaida kallonshi kan kyakkyawar fuskarta, sannan yace ba aljana bace, duk da bantaba ganinta amasarautar nan ba, amma kalli kafarta babu alamun tako ajiki. Haisam yace anfada maka aljanu basa fitowa asiffar mutane? Hmmm kaga malam wannan yarinya kyanta yayi yawa, wlh zantafi inkira mutane ko katashi mutafi.
Idanun Areef suka cika da kwalla yakalli Haisam yace dan Allah, katsaya ni nayarda mute maketa ta farfado, kaga zamu fidda kanmu daga zargin da muke mata. Haisam yace naji, idan ma Mutum ce daga ina tafito? Areef be tsaya bashi amsa ba, kawai yaduka tare da saka bakinshi cikin nata yafara hura mata iska, shiru yaji, yamike yana kara kallonta.
Kamshin jikinta duk yagama cika mashi hanci, Haisam yace kadanna cikinta, hannu yasa, jikinshi se rawa yakeyi yafara danna cikinta, can sega ruwa yafara fitowa ta bakinta, haka yayi tayi, harseda tagama fitar da ruwan datasha.
Tari tafarayi hakan ya tabbatar masu data farfado, cike da firgici ta tashi ta shige jikin Areef, duk ta kanan nadeshi, tafara kuka. Areef kasa magana yayi, dan duk tasakan mashi kasala ajiki, dukawa Haisam yayi yace ya isa haka, tashi muji daga ina kike.
Kintashi tayi, sede tadena kukan datakeyi , tayi lamo ajikin Areef kamar wata yar baby, Areef kuwa kallonta kawai yakeyi, bemasan abinda Haisam yake fada ba, ganin haka yasa Haisam ya bugi kafadar shi, dasauri yamaida kallonshi gurinshi, gira yadaga mashi yana fadin kallon fa nameye?.
Kabari mutambayi yarinya daga ina tashigo amma kawani rungumeta kamar kana shirin bata mama. Murmushi Areef yayi yana sosa kai. Dagota yayi, ahankali ta tashi tana kallonshi, sede taki barin jikinshi, se rawar sanyi takeyi.
Areef yace daga ina kike, meyakawoki nan har kika fada ruwa? Hannu ta daga tana mashi nuni da hanyar part din Jakadiya Safeeya. Haisam yace baki iya magana ne, kinaji ana maki magana zaki tsaya kina mana maganar kurame, kuma gashi alamu yanuna kinji me yace. Komawa tayi jikin Areef zata kwanta, dan gaba daya wani zazzabi takeji, sanyi sekara shigarta yakeyi.
Dasauri Haisam yajawota yana fadin yau ko sunanki mage senaga karshen son jiki. Areef yace haba bros kabita ahankali mana, kama hannun Areef tayi tarike sosai tafara kuka. Tsaki Haisam yaja yace toni zantafi.
Areef kamar zeyi kuka yace plsss kabari muji daga bakinta. Kallonta yayi, yace Beauty tashi kifadamun daga ina kike kinji, kinga kada yatafi yabarni kuma nasan mutane zekira kuma kamaki zasuyi, ai dasauri ta tashi tarike hannunshi, shima tashi yayi yana murmushi.
Haisam yace daganinta batada gaskiya gashi daga yin maganar kamawa tamike. Hannu tasa tana kara nuna mashi hanyar data fito, Areef yace baki iya magana ne? Kai tadaga mashi, tare da fara janshi zuwa hanyar. Atunaninshi ko sanyi ne yahanata magana, hakan yasa yafara binta. Da har Haisam ya kyaleshi se kuma yayi tunanin kada ta cutar dashi seyabisu.
Sunkusa zuwa gurin sukaci karo da Jakadiya tafito daga cikin gida hankalinta atashe. Cak ta tsaya tana masu kallon mamaki, kara kallon Yar Baba tayi, nan hankalinta yafara tashi ganin kayanta ajike, sede ganin wanda suke tare, yasa taboye tashin hankalinta. Da gudu taruga ta rungume Jakadiya Safeeya, janta tayi zuwa cikin gida, suma suka bi bayansu.
Seda tashiga da ita daki tasata tacire kayan tace tasaka wasu kafin tafito, juyawa tayi takoma falo. Bayan sungama gaisawa, Areef yace Aunty ashe beauty agidanki take? Kawai muna zaune nida Haisam agurin lambu semukaji karar wani abu acikin ruwa, muna dubawa ashe ita ce tafada, koda nacirota, ta suma, da kyar ta farfado. Shine tabamu tsoro, dan bamutaba ganinta agidan nan ba, gashi kuma kyanta ya kai akirata da aljana.
Da yamma kamar yanda Waziri yace, haka yasa driver yadauki Jakadiya Safeeya yanufi kasuwa da ita, acan tasiya masu kayan amfani dayawa, sede yawan siyayyar duk ta Yar Baba tafi yawa, kananan kaya ma duk nata sunfi yawa, dasauran kayan amfani na yan mata. Data gama suka wuce gurin tela, anan tayi mashi bayanin yanayinsu tabiya kudin dinki yabata ranar karba.
Jakadiya Karima ce zaune afalon Gimbiyar Babbar Gida tare da Medaki, Gimbiya tace waini Jakadiya kina kula da Suhailat kuwa? Kada fa ta shammacemu kamar yanda Rayhana tayi mana. Jakadiya tace haba Ranki yadade ai ita da haihuwa sede alahira, kada kidamu bazan baki kunya ba. Murmushi tayi tace, haka nakesonji.
Medaki tace bari intashi inje nasan yanzu angama shirya Sarki inje induba jikinshi, yamutsa fuska Gimbiya tayi ta kauda kai, Jakadiya tace afito lafiya Gimbiya. Tana fita Gimbiya taja tsaki tace aikin banza kamar wata tsiya zata iya yimashi, ni wannan mata tsau tsayi ne kawai yasa Sarki ya aureta, shide talaka duk yanda akayi dashi baya iya sakewa. Shiru de Jakadiya tayi bata ce komai ba, tashi tayi tace bari inje gurin Sarkin Fada.
Koda Jakadiya Safeeya takoma part dinta har lokacin maman Yar Baba bata tashi daga baccin datakeyi ba, saboda acikin maganin da likita yabata akwai mesa bacci, dan yace idan tana yawan bacci kwakwalwarta zatafi samun hutu, YarBaba kuwa tana zaune tana kallo.
Jakadiya tace Yar baba zokiga wani abu, tashi tayi tamatsa kusa da ita tazauna tare da jingina da jikinta, jakadiya Tayi murmushi tace, hmmm ke kam mage ma nan taganki tabarki inde gurin sonjiki ne. Dariya Yar Baba tayi takara kwantawa jikinta.
Kayan tafiddo tafara nuna mata, hada inner wears duk tarika gwada mata yanda ake saka su, se murna Yar Baba takeyi, Jakadiya tace zankoya maki yanda ake amfani dasu duka, kuma kinsande nafada maki banason kazanta ko? Kai ta daga mata, tace yauwa, yanzu tashi muje ciki kiyi wanka semu fara.
Ranar litinin Areef yafara zuwa office, aranar duk macen data ganshi se miyanta ya tsinke, sbd kyawun da yayi, tare suke da Haisam, Areef yace nifa nafara tsarguwa, naga se kallona akeyi. Dariya Haisam yayi yace kada kadamu sunga dan saurayi me kyau ne. Duka ya kaimashi yana fadin kai dan iska ne, yace emana kasani ko anan kasamu zabinka tunda babu yar gidan sarauta acikinsu.
Areef yace Allah ya kyauta, anfada maka ni matata zatayi aiki ne, lallai ma, kai bakasan irin macen danake so na aura ba. Kawaide katayani da addu,a. Haisam yace ato idan kuma nizan rigaka aishikenan,Areef yace nima zanfi son haka, da haka suka isa Office dinsu.
Jikin Sarki Hasheem yafara sauki sosai sbd yanzu yanashan magani tunda yaji maganar da Malam yayi, kuma yana cin abinci sosai, hakan yasa Sarki Qaseem yace afara fita dashi fada hakan zerika rage mashi zaman kadaicin dayakeyi.
Haka suka cigaba da rayuwa agidan Sarki, babu wanda yasan dazamansu, aduk lokacin da Baba yaso ganin Yar Baba yakanje yaganta susha fira, har mamakin ganin yanda tacanza cikin lokaci kadan yakeyi, gashi tsafta agurinta kamar da ita aka halicceta, akullum setayi wanka so 3 kuma ko sallah tayi setayi kwalliya, Jakadiya safeeya kam har mamakin saurin fahimtar datake da ita take, kome takoya mata ba wuya tadaukeshi.
Akullum da dare kafin su kwanta se sunyi karatun littattafai, dan zaman datayi takara sanin abubuwa dayawa agurin Jakadiya safeeya, harta da girki tafara koya mata, sbd tace idan bata nan setarika dafa masu. Duk da ankawo dinkunansu amma bata son saka atamfa ko less, tafison tasa kananan kaya, Mamanta kuwa tunda takeshan magani, yanzu haukanta da sauki, batayin komai, sede tazauna tayi shiru idan kuma kaga tana dariya to ita da yarta ce, duk da baccinta yafi yawa akan idonta biyu.
Zaune Areef da Haisam suke acikin lambu suna hutawa, babu kowa agurin, danshi Areef becika son fadawa suna binshi ba, yafison daga shi se Abokinshi Haisam wadda yakasance da ga dupty gvernor na gombe, kuma tare sukayi karatu dashi.
Yar Baba tana gama kwalliya tafito dasauri dan ta nuna ma Jakadiya dan tasan bata fita ba, tana zuwa falo taga bata nan, kitchen tashiga nan ma bata ganta ba, turo baki tayi dantagane tafita, hanyar dataga tana bi tashigo ko tafita tabi, tana zuwa ta tura kofar cikin sa,a tajita abude, murmushi tayi tafita.
Cike da tsoro tafara takawa tana bin cikin lambun, swimming pool tagani kallonshi tayi. Taci gaba da tafiyarta, can taji dawisu yafara kuka, ai batasan lokacin data juya dagudu zata koma inda tafito ba, cikin rashin sa,a tayi tuntube da dutse kawai tafada cikin ruwan.
Su Areef dasuke zaune nesa da ruwan sukaji karar wani abu acikin ruwa, koda Areef yakai kallonshi ga ruwan kawai yaga mutum yana ta daga hannu da kafa acikin ruwa. Cikin sauri yatabo Haisam yana nuna mashi, duk da basu san kowaye ba, Dasauri suka nufi bakin ruwan.
Ur's.
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady )
08028525263
[23/08, 1:48 p.m.] Nabeelert Lady: ..🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
AMAKABARTA AKA HAIFENI
🛤🛤🏕🏕🏕🛤🛤🛤
(The story of hard kingdom)
Nah
Marubuciyar Zamani
NABILA RABI'U ZANGO
(Nabeelert Lady)
@House of Novella Association
(H,O,N,A)
[email protected]
Season 70 ⚜75
Babu bata lokaci Yarima Areef ya fada cikin ruwan, yana zuwa kusa da ita yadaukota, alokacin tasha ruwa harta suma, fitowa yayi daga ruwan tana rungume ajikinshi, abisa kafet din dasuke zaune yakwantar da ita yadora kanta saman cinyarshi, Haisam yana biye dashi duk sun rude.
Kallon tsoro, mamaki suka farayi mata, addu.a duk wadda tazo bakin Areef yinta yakeyi danshi gani yake kamar ba mutum bace. Haisam yace Areef bakada hankali kana ganin kamar ba mutum ba amma zaka dorata akan cinyarka? Tunda de kacirota tashi mutafi, fara jan hannun Areef yayi.
Areef da jikinshi yagama mutuwa sbd tsabar firgici bema san yanayi ba. Da karfi yajashi sannan yadawo hankalinshi, katashi mubar gurin nan, nidama can nafara zargin gurin, gashi yanzu munfara gani. Areef yafara girgiza kai, yamaida kallonshi kan kyakkyawar fuskarta, sannan yace ba aljana bace, duk da bantaba ganinta amasarautar nan ba, amma kalli kafarta babu alamun tako ajiki. Haisam yace anfada maka aljanu basa fitowa asiffar mutane? Hmmm kaga malam wannan yarinya kyanta yayi yawa, wlh zantafi inkira mutane ko katashi mutafi.
Idanun Areef suka cika da kwalla yakalli Haisam yace dan Allah, katsaya ni nayarda mute maketa ta farfado, kaga zamu fidda kanmu daga zargin da muke mata. Haisam yace naji, idan ma Mutum ce daga ina tafito? Areef be tsaya bashi amsa ba, kawai yaduka tare da saka bakinshi cikin nata yafara hura mata iska, shiru yaji, yamike yana kara kallonta.
Kamshin jikinta duk yagama cika mashi hanci, Haisam yace kadanna cikinta, hannu yasa, jikinshi se rawa yakeyi yafara danna cikinta, can sega ruwa yafara fitowa ta bakinta, haka yayi tayi, harseda tagama fitar da ruwan datasha.
Tari tafarayi hakan ya tabbatar masu data farfado, cike da firgici ta tashi ta shige jikin Areef, duk ta kanan nadeshi, tafara kuka. Areef kasa magana yayi, dan duk tasakan mashi kasala ajiki, dukawa Haisam yayi yace ya isa haka, tashi muji daga ina kike.
Kintashi tayi, sede tadena kukan datakeyi , tayi lamo ajikin Areef kamar wata yar baby, Areef kuwa kallonta kawai yakeyi, bemasan abinda Haisam yake fada ba, ganin haka yasa Haisam ya bugi kafadar shi, dasauri yamaida kallonshi gurinshi, gira yadaga mashi yana fadin kallon fa nameye?.
Kabari mutambayi yarinya daga ina tashigo amma kawani rungumeta kamar kana shirin bata mama. Murmushi Areef yayi yana sosa kai. Dagota yayi, ahankali ta tashi tana kallonshi, sede taki barin jikinshi, se rawar sanyi takeyi.
Areef yace daga ina kike, meyakawoki nan har kika fada ruwa? Hannu ta daga tana mashi nuni da hanyar part din Jakadiya Safeeya. Haisam yace baki iya magana ne, kinaji ana maki magana zaki tsaya kina mana maganar kurame, kuma gashi alamu yanuna kinji me yace. Komawa tayi jikin Areef zata kwanta, dan gaba daya wani zazzabi takeji, sanyi sekara shigarta yakeyi.
Dasauri Haisam yajawota yana fadin yau ko sunanki mage senaga karshen son jiki. Areef yace haba bros kabita ahankali mana, kama hannun Areef tayi tarike sosai tafara kuka. Tsaki Haisam yaja yace toni zantafi.
Areef kamar zeyi kuka yace plsss kabari muji daga bakinta. Kallonta yayi, yace Beauty tashi kifadamun daga ina kike kinji, kinga kada yatafi yabarni kuma nasan mutane zekira kuma kamaki zasuyi, ai dasauri ta tashi tarike hannunshi, shima tashi yayi yana murmushi.
Haisam yace daganinta batada gaskiya gashi daga yin maganar kamawa tamike. Hannu tasa tana kara nuna mashi hanyar data fito, Areef yace baki iya magana ne? Kai tadaga mashi, tare da fara janshi zuwa hanyar. Atunaninshi ko sanyi ne yahanata magana, hakan yasa yafara binta. Da har Haisam ya kyaleshi se kuma yayi tunanin kada ta cutar dashi seyabisu.
Sunkusa zuwa gurin sukaci karo da Jakadiya tafito daga cikin gida hankalinta atashe. Cak ta tsaya tana masu kallon mamaki, kara kallon Yar Baba tayi, nan hankalinta yafara tashi ganin kayanta ajike, sede ganin wanda suke tare, yasa taboye tashin hankalinta. Da gudu taruga ta rungume Jakadiya Safeeya, janta tayi zuwa cikin gida, suma suka bi bayansu.
Seda tashiga da ita daki tasata tacire kayan tace tasaka wasu kafin tafito, juyawa tayi takoma falo. Bayan sungama gaisawa, Areef yace Aunty ashe beauty agidanki take? Kawai muna zaune nida Haisam agurin lambu semukaji karar wani abu acikin ruwa, muna dubawa ashe ita ce tafada, koda nacirota, ta suma, da kyar ta farfado. Shine tabamu tsoro, dan bamutaba ganinta agidan nan ba, gashi kuma kyanta ya kai akirata da aljana.