← Book details A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 26 OF 33

Sashe 26

A Makabarta Aka Haifeni Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hakan yasa naroki alfarma gurin Baba nayabar aikinshi yataho tare dasu. Adaren dazasu tafi nakira Safeeya daki nake cemata ina zargin wani abu akan mutanen nan, itama tace mun zuciyarta tafara saka mata irin abinda nake zargi, dan ita tasan Fulani sosai, amma tacemun bazata iya cewa ita bace dan alokacin ko Sarki yaganta baze iya ganeta ba, tsawon shekaru 18, gashi bacikin hankalinta take ba, kuma bagurin jin dadi ba, babu wankan kirki, babu sallah, ba lallai bane a iya ganeta.

Shiyasa nace ma Safeeya sutafi tare, ta ajesu agurinta kuma kada tabari kowa yasan dazamansu idan har tasamu nutsuwa da tsafta zata dawo cikin kamanninta, idan kuma ba ita bace shikenan nace munyi temako.

Alokacin nakira Waziri mukayi maganar, dan aduk fadin masarautar nan mutum 3 nafi yarda dasu, kuma yana daya daga cikinsu, Sarki Qaseem, da Sarki Hasheem. Babban dalilin dayasa banyi maganar da Sarki Qaseem ba, nasan yanda halinshi yake, baze taba iya hakura abi abun asannu ba, kamar yanda nashirya, shiyasa ban fada mashi ba.

Bayan Safeeya takirani tafadamun tagano wannan mahaukaciyar bakowa bace se Fulani da diyarta, alokacinma nace mata taboye abun harse angano wadanda suka aikata mata haka. Nakira Waziri nafada mashi, kuma alokacin yake fadamun yafara zargin Sarkin Fada.

Ni nace mashi yacigaba da bibiyarshi harse ansamu cikakkiyar shedar dazata bada damar kamashi sannan, kuma nafada mashi bashi kadai bane dole akwai wata ko wani makusancin Sarki. Alokacin seyake cemun shifa yana zargin Jakadiya Karima.

Nima nayarda da abinda yafada, hakan yasa nace mashi ya zuba masu ido su duka biyun. To Alhamdulillahi yau gashi damukayi hakuri Allah yanuna mana makiyanmu afili.

Sede kuma akwai abu daya danakeso intambaya Waziri. Ina wannan bafaden da Sarkin fada yajama sharrin kisa, ina fatan ba,a yanke mashi hukuncin kisa alokacin ba? Gyara zama Waziri yayi yace, alokacin kam Sarki ya yanke mashi hukuncin kisa.

Sede ni ajikina bansan meyasa banyarda da hukuncin da Sarki ya yanke ba, kuma zuciyata takasa yarda da cewar shine yayi kisan, amma alokacin kuma zuciyata bata zargin Sarkin fada, sede kawai taki yarda da wanda akace yayi kisan.

Hakan yasa naja Sarki falo tafada mashi da kada ya yanke hukuncin dazezo yadameshi daga baya, nine nabashi shawarar daya yanke mashi hukuncin daurin rai da rai. Kuma haka akayi, haryanzu yana nan akurkutun gidan nan.

Sede tun lokacin dana fara zargin Sarkin fada da rashin gaskiya acikin gidan nan, tun daga ranar nafara kaimashi ziyara, mukan zauna muyi fira,acikin zaman damukayi ne, nakara yarda dabashine yayi kisan ba, kuma akwanakin baya ne nasa aka canza mashi gurin aiki, harda gurin zama.

Kuma tunjiya nasa aka fiddoshi yanzu haka yana masauki. Malam yace kasa akirashi yazo nan. Waziri ya aiki daya daga cikin fadawan gurin. Malam yace wannan shine iyakar abinda nasani agame da rayuwar Fulani da diyarta. Wadda haryanzu babu wanda yasan sunanta.

Abinda Baba yake kiranta dashi shine Yar Baba, wanda yacemun ada yaji Fulani tana kiranta da Baby, jin sunan zeyi mashi wahala ne, yake kiranta da diyarshi. Amma ayanzu tunda gashi sundawo gida, za,a iya saka mata sun

kuma Waziri se muji daga gareku wane irin hukunci zaku yankema wadannan maciya amanar.

Sallamar bafaden da aka aika ne tasasu kallon kofa, tare suke da wanda aka likama kisan da Sarkin Fada yayi, zama yayi yana kwasar gaisuwa, daka ganshi kasan yajigata, atsawon zaman dayayi akurkutu shekaru dayawa.

Kallon Sarki Qaseem da Sarki Hasheem Waziri yayi, domin jin abinda zasu fada. Sarki Qaseem yayi gyaran murya yace, ni babu abinda zance, sede kawai inma Allah godiya daya kawomu karshen wannan matsala damuke ciki. Tabbas wadan nan mutane, kunsamu cikin tashin hankali, babu abinda zance maku se Allah ya isa.

Sede abu daya nakeso kusani, hakan da kukayi bashine ze samurika tsoron mutane ba,ko kuma mudena jawo su zuwa jikinmu ba, ai ba,a taba taruwa azama daya, idan wani yazo daniyar cutarka, Allah ze aiko maka dana gari, wanda ze zauna da kai badan komai naka ba, sedan son dayake maka domin Allah.

Idan kuka kalli Jakadiya Safeeya da Malam,da Matata da kuma matar Yaya wato Fulani, daga baya muka kara samun Baban Darazo da abokin Yarima wato Haisam. Duka wadan nan dana lissafo babu wanda muka hada jini dashi, kuma babu wanda muka tashi dashi acikin gidan nan.

Asalima bamu taba tunanin zasu shigo cikin rayuwarmu ba, sedaga baya muka sansu, kuma duk da basu kasance yan uwa agare mu ba, sun zauna damu tsakani da Allah, babu wanda yakeda niyar cutar damu.

Idan muka kalli Malam da kanwarshi, bawai dan sun rasa abinda zasuci bane yasa suka shigo jikinmu. Jakadiya Safeeya tazo gidan nan badan kowa ba sedan bin umarnin yayanta, kuma duk da haka tarika kaskantar da kanta agaremu, wanda inda dan kudine zatazo, ninasan babu abinda ze kawota, dan aduk fadin garin Bauchi, darazo, Gombe, harma da makotanmu mutane dayawa sunsan Malam, kuma kowa yasan babban mutum ne.

Idan har kudine, bayada damuwa dasu, asalima yakan dauko wasu suci akarkashin shi. Amma duk da haka suke zama tare damu abisa gaskiya da amana. Wannan kadai ya isa yanuna ma kowa cewa wanda baku hada komai dashi ba, ze iya yimaka abinda makusancinka baze maka ba.

Yanzu ku kalli irin cin amanar da akayima Yaya, Gimbiya Zakiyya kinci amanar sarauta, kuma kinci amanar iyayenki, amatsayinki na Uwar gidan yaya amma aka hada baki dake, aka cuceshi, koba komai, mahaifinki da Abbanmu abokan junane sosai, kuma dama sune suka hada aurenku, alokacin Yaya bayasonki amma nayi imani da Allah haryanzu betaba fada maki keba ra,ayinshi bace.

Haka yakarbi zabin iyayenmu kuma yazauna dake da gaskiya da amana, segashi daga karshe kinzama butulu, bayan butulci ma harseda kika hada da cin amanar aurenku. Wa iyazubillah, kina matar aure amma kika aikata wannan babban zunubi agidanki. Amma kanki kikai mawa, kuma wlh. Kowace irin alaka ketsakinmu bazata hana ayanke maki hukunci dede da laifinki ba.

Kuka tasaka tana fadin natuba, dan Allah kumun rai, wlh duk abinda kuka fada gaskiya ne, amma niban aikata abinda kukagani da son rai na ba. Nide nasan babu abinda na tsana kamar zama guri daya da talaka, kuma ni tunda nake wlh wannan aikin da Sarkin fada yamun shikadai ne, yataba hadani dashi harmukayi magana. Akwai sanda jakadiya Karima tazo tacemun wai Sarkin Fada yana gaisheni.

Wlh ku tambayeta idan har zata fadi gaskiya zata fada maku irin cin mutuncin dana mata akan abinda tazo mun dashi, wlh babu wata alaka datake tsakanina dashi, ko aranar danasan munfara aikata sabo dashi, yana shigowa da masifa narufeshi, amma bansan ya akayi daga baya harna bashi hadin kai ba.

Dan Allah Sarkin fada kafada masu ba laifina bane. Wani malalacin murmushi Sarkin Fada yayi yadauke idonshi daga kallonta. Sarki Qaseem yace wannan kuma yarage naki, kinsan masarautar nan bata yanke hukunci seta tabbatar da sheda tazahiri, kuma ba mutum daya ba, kowa gurin nan yaga abinda kuka aikata, dan haka ki adana kalamanki.

Kallon Medaki yayi, yace kenarasa ma mezance maki, kinfi kowa zama cikakkiyar butulu, kinfi kowa sanin dayanda aka aureki da irin halaccin da Yaya yayi maki, duk da nibanyarda da labarin da mamanki tabada ba, amma sbd sanin girman alkawarin da yaya yadaukar mata, haka mukayi hakuri ya aureki.

Amma kirasa da abinda zaki saka mashi se irin wannan cin amanar, kema zakiga sakamakonki. Kuma abinda nakeso dake inaso kifada mana wacece ke? Da kuma asalin garinku.

Cikin sheshshekar kuka Medaki tace wlh nima bansan inane asalin garinmu ba, nadesan ayawon damukeyi daga wannan kauyen zuwa wani iyayena suka haifeni. Kuma sanin dana yima iyayena basu bani tarbiya tagari ba, babu ilimin addini bare na boko, to sukansu ma basu damu danasu addininba.

Nikaina nafara sanin Sallah ne alokacin dana ke bin wata kawata islamiyarsu, anan nafara sanin addini na, harna fara fahimta sosai, sekawai innata tafara doramun talla, domin ita macece meson kudi.

Aduk lokacin dana saida tana siyamun duk abinda nakeso, nima tundaga ranar son kudi,yashiga raina. alokacin kuma na hadu da wani saurayi shine yakara huremun kunne, haryayi nasarar ciremun budurcina, seda muka zubar da ciki har 2, kuma Innata bata tabamun fada ba, wannan shine sanadiyar lalacewar mahaifata.

Mahaifina dan caca ne, bedamu da ya rayuwata takeba, shiyasa nakasance tamkar dabbar daji, banida wani takunkumin daze hanani aikata abinda naga dama. Sanadiyar Caca mahaifina yarasa ranshi, mutanen gari suka koremu harmuka hadu daku, Innata tafada maku karya har kuka yarda damu.

Tabbas nasan naci amanar mijina, wanda yarufamun asiri, duk da yagane banje da budurcina ba, amma be tsaneni ba, asalima cikin laluma ya tambayani, shima nafada mashi fyade akamun wanda karyane, amma haka ya yarda dani, kuma yacemun beyarda infadama kowaba.

Dan Allah kayafe mani, nasan bankasance mace tagari ba, naci amanarka dan Allah kuyafemun. Kuka tasaka wanda seda wasu daga cikin mutanen falon sukaji tausayinta,,,,, hayaniya sukaji awaje, Wazirine da fadawa suka leka.

Wani kodaddan mutumi suka gani wanda beda kyan gani, sunata rigima da masu gadi. Waziri yace ku kyaleshi yakaraso, haka yataho yanata zare ido. Yana zuwa yace wani nake nema agidan nan nayi mashi aiki be bani kudina ba. Kuma nafada mashi idan har bebani kudina ba zanzo intona mashi asiri.

Murmushi Waziri yayi yace kashigo semuji wa kake nema. Kowa mamakin ganin mutumin daya shigo yakeyi, banda Sarkin Fada wanda yaketa muzurai. Waziri yace munajinka wakake nema?.

Yace sunanshi Sarkin Fada, kuma ya kasance daya daga cikin mutanen danake yima aiki, duk wani aikinshi nine nakeyi mashi, anan yarika fadin duk irin asirin dayasashi yayi, harda wanda yayima Areef, dana Jakadiya Karima wanda tazubarma Gimbiya Suhailat ciki kuma aka daure mahaifarta, har yakawo asirin karshe dayayi mashi.

Yace aranar yazomun akan yanason inbashi maganin mallakar zuciyar Matar Sarki, Zakiyyah, yacemun yadade yana sha,awarta amma yasan bazata taba bashi kanta ba, hakan yasa yazo inbashi magani, alokacin yacemun beda kudi amma yasan idan yasamu sa,ar kusantarta yamallake zuciyarta zesamu kudi.

Tun ranar dana bashi bankara ganinshi ba, shine yanzu nazo inkarbi hakkina. Salati kowa yakeyi, sbd wani abin al,ajabin dasuka karaji yabullo. Murmushi Waziri yayi yace kaima seka samu guri kazauna kajira naka hukuncin tunda Allah yakawoka. Zaro ido boka yayi yana fadin aishikenan kuma wlh nayafe mashi kubarni intafi.
Chapter 26 · 0% Book details