Sashe 97
Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallonsa maryam ta cigaba da yi ko kifta idanunta bata són yi akanshi "kallonsa kad'ai ya isa ya harzikawa mutun brain dinsa ,namijin duniya ne ko daga yanayinsa ,wani murmushin farinciki na samun nasara ya subuce mata "duk Kinsa da aureta gashi dai allah ya bata sa'a a karshe ta zama mallakinsa na har abada, domin tasan muddin mami na numfashi a doron duniya bazata barshi ya wulakantata ba bare akai ga maganar saki atsakaninsu zasu rayu tare har karshen numfashinsu dan haka zata iyawarta da komai ta makallakesa har ma ta zama wani sashin na rayuwarsa ."
Duk da ba kulata yake ba bare kallota amman da kyar take iya control din kanta akanshi don kallonsa yana cikin abinda ke sata fita haiyacinta tama rasa a duniyar da take ,a duk lokacin da tayi saa ya kalleta kuwa hakan na matukar sata natsuwa ,ta lumshe idanunta acikin ranta tace "adamcy nah ni kad'ai ,komai naka yayi min ilarka dai baka son rainin da zafin zuciya uwa uba tsanar mutane na babu gaira babu dalili ."
Kamar ance ya d'ago kanshi dake risine yaga idanunta akanshi ,a zaunen da yake ransa ya fara 'baci ,zuciyarsa ta dinga tafarfasa sakamakon kallon da take masa na kurrulla irin kallon daya fi tsana arayuwarsa ,numfashi ya sauke ahankali tare da sake kau da kanshi muryarsa a tsarke ya kiran sunan da yake kiran mahaifiyarsa dashi "sweetheart !"ya'akayi adamcy nan? "ta amsa cike da tsananin kulawa "Kece wa yarinyar nan ta bar d'akin nan" a d'an firgice mami tace "wace yarinyar kuma ?"
Shiru yayi yana sake 'bata rai mami ta kalli gabadaya parlour'n babu kowa daga ita sai shi da maryam ne acikinsa "kenan dai maryam yake nufi ?"adamcy matarka ce fa ?"oh my god sweetheart ki kalli kiga irin kallon rainin hankalin da take min ." yayi mgnr a d'an tsawa ce mami ta waiga ta kalli maryam wacce tun soma maganarsa tayi saurin d'auke idanunta akanshi ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta ."
"Ba nasara akayi akaina ba ni naga damar amincewa aurenta dan naga sai wani kallon gani gani take min ,wallahi tun da wuri ki ja mata kunne kar taga an d'aura min ita ta nemi ta dinga min kallon iskanci idan ma tana tunanin wani abu acikin ranta wallahi tayi maza ta cire dan hakan ba abu ne mai sauki ba ."
"Da me zan ji ?aurenta da aka min dole ,ko da kallon iskanci da take min ? amman barni da zazzafar qaddarar data rufta min shekaru goma sha .." yayi shiru yana sauke zazzafan numfashi ,ya gyara zamansa tare da kai hannuwansa duka ya rufe fuskarsa dashi yana jin kamar yayi kuka kafin daga bisani ya cigaba da sakin bakaken maganganu masu zafi da ta'ba zuciya duk magiyar da mami take masa akan yyi shiru bai yi ba har sai daya samu natsuwa sannan ya saurara inda ya kwanta akan kujera ya juyar da kanshi gefe yana sauke numfashi ."
mami ta kallesa na second biyar sannan ta juya ta kalli maryam dake tsaye gabadaya ta rasa me zata ce ."yayinda maryam Jiki a matukar sanyaye ta matsa daga kusa dasu tare da juya masu baya tana jin faduwar gaba mai tsananin , tsanarsa gareta yana matukar d'aga mata hankali sosai taji bacin rai ,taji kamar ta fice daga d'akin mummansa ganin yadda ya juya baya ko mami yaki kallo ."
mami ta qara matsowa kusa dashi tace "Adamcy ka daina zafafa kiyayyar matarka a gaban idanunta saboda ban fidda rai wata rana shakuwa mai qarfi na iya shiga tsakaninku ba dan haka ka dinga qoqarin dannewa ka barwa zuciyarka please " tana gama fadar haka ta mike tsaye ta qarasa inda maryam take tsaye tare da riko hannunta suka fito daga d'akin."
Suna fita mami ta soma qoqarin rarrashin maryam ,tayi saurin cewa mami "karki wani damu mami banji komai araina ba," idan da sabo na rigada na saba da halinsa fatana allah yasa aurenmu ya zame mana alkhairi arayuwarmu gabadaya."shiru tayi kafin ta cigaba da magana "mami ni dai ki qara tayamu da addua akan wacce kike mana duk da har yanzu yaya adam bai amince dani ba amman yau kawai naji wani sanyi da samun 'yanci a zuciyata ."
Murmushi mami tayi dan tun tuni ta fahimci wani abu akan maryam din hakan kuma yayi mata dadi domin ko babu komai zatayi hakuri da duk wani wulakanci d'anta cike da farinciki tace"na gode sosai maryam in sha allahu zan cigaba da yi maku addua allah yayiwa rayuwar aurenku albarka allah ya azurtaku da samun zuria masu albarka ko ni yau zuciyata ta rage nauyi duk da rayuwar da adamcy ya d'auko ya rage kashi sabain na farincikina amman duk da haka naji zuciyata ta rage nauyi saboda nayi imani ko bayan raina zaki kula da rayuwar dan'uwanki ."
"Maryam adamcy rayuwata ne Kiyi hakuri dashi , Kiyi hakuri da halinsa ki kular min dashi "in sha allahu mami zanyi iyakar qoqarina " na gode maryam allah yayi miki albarka "ameen na gode mami allah ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani "Ameen Ameen mryam shiyasa nake qara sonki akwai ki da hakuri dasanin yakamata ."suka cigaba da takawa ahankali suna magana har suka sauko qasa fuskarsu d'auke da murmushin farinciki ."
Bayan saukowar mami ta aika akira mata hisham dan tun safe yana bangaren baba babba tare dasu salim tana zaune a d'akinta yayi sallama sai data bashi izinin shigowa sannan ya turo kofar d'akin ya shiga kanshi a risine a kasa kallo d'aya zaka masa ka fahimci jikinsa a mace yake , hisham ya rusuna ya gaishe da mami cike da girmamawa ,ta amsa masa cike da kulawa tana nuna masa kan kujera amman yaki zama ya zauna akan daddumar daya gani a shimfide akan kafet."
"Hisham ya akaji da taro ?kamar bazai amsa ba amman ya kasa ko babu komai mami tana da kima gareshi bazai ta'ba yi mata banza ba,dan haka ya bude bakinsa da kyar yace "alhamdulillah mami ya naku ?to Alhamdulillah hisham allah yayi maku albarka gabadayanku, allah kuma ya baku ikon cinye jarabawa rayuwar, kowani bawa rayuwarsa tattare take tafiya da jarabawa iri iri ."
"Kayi hakuri akan sauyin daka samu ka dauki hakan a matsayin jarabawa da kuma qaddara, auren auta yana daga cikin qaddararka wanda baka isa ka goge faruwar hakan ba ,abinda nake son ka fahimta Idan allah bai nufeka da samun wani abu arayuwarka ba sai ka gode masa domin allah sonka yake kuma duk abinda allah ya qaddara shi zaka samu, abinda allah bai qaddara zaka sameshi ba duk yadda abun ya kusantoka at end of the day bazaka sameshi ba duk kuwa son da kake yiwa abun ."
"Wannan kuma duk hukuncin ubangaji ne , idan da yau mun sanya hakan acikin zukantamu da zamuyi rayuwa cikin jin dadi cikin annashuwa batare da wata damuwa ba ,idan mun samu allah ne ,idan mun rasa allah ne" wama tasha una illa anyasha allahu rabbul alameen duk yadda kaso idan allah bai so ba bazai ta'ba yuwa ba ."
"wannan hukunci ne na allah ,allah yasa hakan shine mafi alkairi wata killan ma idan ka samu auren nuzla arayuwarka ta zame maka maseefa da tashin hankalin da sai kayi nadama ,ta zama bala'i arayuwarka yanzu rashinta sai ya zame maka alkhairi arayuwarka kayi hakuri da sauyin da allah yayi maka da sannu zaka ga irin sakayya da allah zai maka domin duk wanda ya yarda da allah allah zai isar masa ."
"idan kuma akwai alkhairi a tsakaninka da nuzla sai kaga anan gaba ka qara daita wannan duk kadan ne daga hukuncin ubangiji fatanmu allah ya zaba mana abinda yafi zama alkhairi arayuwarmu kar allah ya barmu da zabinmu "duk wannan maganar da mami take kanshi na kasa ya kasa d'ago kanshi har sai data dasa aya ta hanyar saka masa albarka sannan ya d'ago yayi mata godiya ya mike a natse ya fice daga gidan gabadaya."
Karfe biyar daidai motoci guda goma na alfarma sukai parking a kofar gidan mami domin d'aukar nana hauwa ,mutanen da suka zo gabadaya sun kasance kawaye ne ga hajiya zulfa'u ,kowacce cikin shiga ta alfarma domin kallo daya zaka masu ka fahimci kudi ya zauna ajikinsu shigar kowace tana wane na wane , sai dai mami tace hisham take son yazo ya d'auke amaryarsa da kanshi lokacin da sakon ya samesa yaji abun wani iri ranshi ya 'baci matuqa ."
"duk kawayen mumynsa da abokansa da suka tafi d'aukota basuyi ba sai shi da kanshi yaje kamar wata zinariya ?yayi wa kanshi tmbyr yana jan tsaki bana jin zan iya zuwa dan nasan nauyi kawai mami take són d'aura min ya lalubo wayarsa yana qoqarin kashewa kiran mami ya shigo "ya salam !"ya furta a fili yana mai dafe kanshi kiranta né yayita shigowa har sai daya d'auka ,yana d'auka tace "hisham d'ana kazo ka d'auki matarka " babu yadda ya iya dole ya amsa da "tô mami ganinan zuwa"ransa a matukar 'bace ya tashi ya shirya cikin wani d'anyen voyal fari sol ya shiga d'akin hjy zulfa'u ya fad'a mata inda zashi sannan ya fito ya kamo hanyar zuwa abdullahi estate."
zaune nana hauwa'u take agaban mahaifiyarta sanye da fararen kaya tun daga kan takalmi mayafi pos din dake rike a hannunta agogo komai na jikinta fari ne sol jikinta lullube cikin mayafi , shape din fuskarta kawai ake iya gani ,wani irin qamshin jikinta Ke fitarwa mai sanyin dadi da sanya natsuwa tare da kwantar da hanakali yayinda yan'uwata mata ke zaune akan kujera kowace cikin shiga iri d'aya ."
nasiha mai matukar ratsa jiki mami take mata tana tunatar daita hakin daya rataya a wuyanta cike da gamsuwa nana hauwa take gyada mata kai tana zubar da hawaye adaidai lokacin ATA ya shigo d'akin sakamakon kiransa da mami tayi bai qarasa inda suke ba ya samu waje ya tsaya ya jingina bayansa da bango d'akin ya rungume hannuwansa duka a qirjinsa yana kallon nana hauwa'u dake zubar da hawaye yayinda aunty shahida ta mike daga mazauninta tana faman rarrashinta tana goge mata hawaye ."
Duk da ba kulata yake ba bare kallota amman da kyar take iya control din kanta akanshi don kallonsa yana cikin abinda ke sata fita haiyacinta tama rasa a duniyar da take ,a duk lokacin da tayi saa ya kalleta kuwa hakan na matukar sata natsuwa ,ta lumshe idanunta acikin ranta tace "adamcy nah ni kad'ai ,komai naka yayi min ilarka dai baka son rainin da zafin zuciya uwa uba tsanar mutane na babu gaira babu dalili ."
Kamar ance ya d'ago kanshi dake risine yaga idanunta akanshi ,a zaunen da yake ransa ya fara 'baci ,zuciyarsa ta dinga tafarfasa sakamakon kallon da take masa na kurrulla irin kallon daya fi tsana arayuwarsa ,numfashi ya sauke ahankali tare da sake kau da kanshi muryarsa a tsarke ya kiran sunan da yake kiran mahaifiyarsa dashi "sweetheart !"ya'akayi adamcy nan? "ta amsa cike da tsananin kulawa "Kece wa yarinyar nan ta bar d'akin nan" a d'an firgice mami tace "wace yarinyar kuma ?"
Shiru yayi yana sake 'bata rai mami ta kalli gabadaya parlour'n babu kowa daga ita sai shi da maryam ne acikinsa "kenan dai maryam yake nufi ?"adamcy matarka ce fa ?"oh my god sweetheart ki kalli kiga irin kallon rainin hankalin da take min ." yayi mgnr a d'an tsawa ce mami ta waiga ta kalli maryam wacce tun soma maganarsa tayi saurin d'auke idanunta akanshi ta sunkuyar da kanta kasa tana wasa da yatsun hannunta ."
"Ba nasara akayi akaina ba ni naga damar amincewa aurenta dan naga sai wani kallon gani gani take min ,wallahi tun da wuri ki ja mata kunne kar taga an d'aura min ita ta nemi ta dinga min kallon iskanci idan ma tana tunanin wani abu acikin ranta wallahi tayi maza ta cire dan hakan ba abu ne mai sauki ba ."
"Da me zan ji ?aurenta da aka min dole ,ko da kallon iskanci da take min ? amman barni da zazzafar qaddarar data rufta min shekaru goma sha .." yayi shiru yana sauke zazzafan numfashi ,ya gyara zamansa tare da kai hannuwansa duka ya rufe fuskarsa dashi yana jin kamar yayi kuka kafin daga bisani ya cigaba da sakin bakaken maganganu masu zafi da ta'ba zuciya duk magiyar da mami take masa akan yyi shiru bai yi ba har sai daya samu natsuwa sannan ya saurara inda ya kwanta akan kujera ya juyar da kanshi gefe yana sauke numfashi ."
mami ta kallesa na second biyar sannan ta juya ta kalli maryam dake tsaye gabadaya ta rasa me zata ce ."yayinda maryam Jiki a matukar sanyaye ta matsa daga kusa dasu tare da juya masu baya tana jin faduwar gaba mai tsananin , tsanarsa gareta yana matukar d'aga mata hankali sosai taji bacin rai ,taji kamar ta fice daga d'akin mummansa ganin yadda ya juya baya ko mami yaki kallo ."
mami ta qara matsowa kusa dashi tace "Adamcy ka daina zafafa kiyayyar matarka a gaban idanunta saboda ban fidda rai wata rana shakuwa mai qarfi na iya shiga tsakaninku ba dan haka ka dinga qoqarin dannewa ka barwa zuciyarka please " tana gama fadar haka ta mike tsaye ta qarasa inda maryam take tsaye tare da riko hannunta suka fito daga d'akin."
Suna fita mami ta soma qoqarin rarrashin maryam ,tayi saurin cewa mami "karki wani damu mami banji komai araina ba," idan da sabo na rigada na saba da halinsa fatana allah yasa aurenmu ya zame mana alkhairi arayuwarmu gabadaya."shiru tayi kafin ta cigaba da magana "mami ni dai ki qara tayamu da addua akan wacce kike mana duk da har yanzu yaya adam bai amince dani ba amman yau kawai naji wani sanyi da samun 'yanci a zuciyata ."
Murmushi mami tayi dan tun tuni ta fahimci wani abu akan maryam din hakan kuma yayi mata dadi domin ko babu komai zatayi hakuri da duk wani wulakanci d'anta cike da farinciki tace"na gode sosai maryam in sha allahu zan cigaba da yi maku addua allah yayiwa rayuwar aurenku albarka allah ya azurtaku da samun zuria masu albarka ko ni yau zuciyata ta rage nauyi duk da rayuwar da adamcy ya d'auko ya rage kashi sabain na farincikina amman duk da haka naji zuciyata ta rage nauyi saboda nayi imani ko bayan raina zaki kula da rayuwar dan'uwanki ."
"Maryam adamcy rayuwata ne Kiyi hakuri dashi , Kiyi hakuri da halinsa ki kular min dashi "in sha allahu mami zanyi iyakar qoqarina " na gode maryam allah yayi miki albarka "ameen na gode mami allah ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani "Ameen Ameen mryam shiyasa nake qara sonki akwai ki da hakuri dasanin yakamata ."suka cigaba da takawa ahankali suna magana har suka sauko qasa fuskarsu d'auke da murmushin farinciki ."
Bayan saukowar mami ta aika akira mata hisham dan tun safe yana bangaren baba babba tare dasu salim tana zaune a d'akinta yayi sallama sai data bashi izinin shigowa sannan ya turo kofar d'akin ya shiga kanshi a risine a kasa kallo d'aya zaka masa ka fahimci jikinsa a mace yake , hisham ya rusuna ya gaishe da mami cike da girmamawa ,ta amsa masa cike da kulawa tana nuna masa kan kujera amman yaki zama ya zauna akan daddumar daya gani a shimfide akan kafet."
"Hisham ya akaji da taro ?kamar bazai amsa ba amman ya kasa ko babu komai mami tana da kima gareshi bazai ta'ba yi mata banza ba,dan haka ya bude bakinsa da kyar yace "alhamdulillah mami ya naku ?to Alhamdulillah hisham allah yayi maku albarka gabadayanku, allah kuma ya baku ikon cinye jarabawa rayuwar, kowani bawa rayuwarsa tattare take tafiya da jarabawa iri iri ."
"Kayi hakuri akan sauyin daka samu ka dauki hakan a matsayin jarabawa da kuma qaddara, auren auta yana daga cikin qaddararka wanda baka isa ka goge faruwar hakan ba ,abinda nake son ka fahimta Idan allah bai nufeka da samun wani abu arayuwarka ba sai ka gode masa domin allah sonka yake kuma duk abinda allah ya qaddara shi zaka samu, abinda allah bai qaddara zaka sameshi ba duk yadda abun ya kusantoka at end of the day bazaka sameshi ba duk kuwa son da kake yiwa abun ."
"Wannan kuma duk hukuncin ubangaji ne , idan da yau mun sanya hakan acikin zukantamu da zamuyi rayuwa cikin jin dadi cikin annashuwa batare da wata damuwa ba ,idan mun samu allah ne ,idan mun rasa allah ne" wama tasha una illa anyasha allahu rabbul alameen duk yadda kaso idan allah bai so ba bazai ta'ba yuwa ba ."
"wannan hukunci ne na allah ,allah yasa hakan shine mafi alkairi wata killan ma idan ka samu auren nuzla arayuwarka ta zame maka maseefa da tashin hankalin da sai kayi nadama ,ta zama bala'i arayuwarka yanzu rashinta sai ya zame maka alkhairi arayuwarka kayi hakuri da sauyin da allah yayi maka da sannu zaka ga irin sakayya da allah zai maka domin duk wanda ya yarda da allah allah zai isar masa ."
"idan kuma akwai alkhairi a tsakaninka da nuzla sai kaga anan gaba ka qara daita wannan duk kadan ne daga hukuncin ubangiji fatanmu allah ya zaba mana abinda yafi zama alkhairi arayuwarmu kar allah ya barmu da zabinmu "duk wannan maganar da mami take kanshi na kasa ya kasa d'ago kanshi har sai data dasa aya ta hanyar saka masa albarka sannan ya d'ago yayi mata godiya ya mike a natse ya fice daga gidan gabadaya."
Karfe biyar daidai motoci guda goma na alfarma sukai parking a kofar gidan mami domin d'aukar nana hauwa ,mutanen da suka zo gabadaya sun kasance kawaye ne ga hajiya zulfa'u ,kowacce cikin shiga ta alfarma domin kallo daya zaka masu ka fahimci kudi ya zauna ajikinsu shigar kowace tana wane na wane , sai dai mami tace hisham take son yazo ya d'auke amaryarsa da kanshi lokacin da sakon ya samesa yaji abun wani iri ranshi ya 'baci matuqa ."
"duk kawayen mumynsa da abokansa da suka tafi d'aukota basuyi ba sai shi da kanshi yaje kamar wata zinariya ?yayi wa kanshi tmbyr yana jan tsaki bana jin zan iya zuwa dan nasan nauyi kawai mami take són d'aura min ya lalubo wayarsa yana qoqarin kashewa kiran mami ya shigo "ya salam !"ya furta a fili yana mai dafe kanshi kiranta né yayita shigowa har sai daya d'auka ,yana d'auka tace "hisham d'ana kazo ka d'auki matarka " babu yadda ya iya dole ya amsa da "tô mami ganinan zuwa"ransa a matukar 'bace ya tashi ya shirya cikin wani d'anyen voyal fari sol ya shiga d'akin hjy zulfa'u ya fad'a mata inda zashi sannan ya fito ya kamo hanyar zuwa abdullahi estate."
zaune nana hauwa'u take agaban mahaifiyarta sanye da fararen kaya tun daga kan takalmi mayafi pos din dake rike a hannunta agogo komai na jikinta fari ne sol jikinta lullube cikin mayafi , shape din fuskarta kawai ake iya gani ,wani irin qamshin jikinta Ke fitarwa mai sanyin dadi da sanya natsuwa tare da kwantar da hanakali yayinda yan'uwata mata ke zaune akan kujera kowace cikin shiga iri d'aya ."
nasiha mai matukar ratsa jiki mami take mata tana tunatar daita hakin daya rataya a wuyanta cike da gamsuwa nana hauwa take gyada mata kai tana zubar da hawaye adaidai lokacin ATA ya shigo d'akin sakamakon kiransa da mami tayi bai qarasa inda suke ba ya samu waje ya tsaya ya jingina bayansa da bango d'akin ya rungume hannuwansa duka a qirjinsa yana kallon nana hauwa'u dake zubar da hawaye yayinda aunty shahida ta mike daga mazauninta tana faman rarrashinta tana goge mata hawaye ."