← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 88 OF 100

Sashe 88

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Shiru yayi ya kasa cigaba da magana "mami dan darajan allah kiyi hakuri tunda yayi nadama har ya baki hakuri sannan babu abinda zai samu maryam zata cigaba da rayuwa kamar kowacce yar adam Kiyi hakuri ki yafe masa kin rigada Kinsan halin adam bai iya magana ba duk maganar data fito bakinsa haka yake cabawa inji cewar aunty khadija wani mugun kallo ya wurga ma mai hade da harara ."

"Me yasa bazai zama mutun na farko da zai ji ciwon abinda akayi mata ba? maryam fa matar da zai aura ce, matar da zai raba duk wani farinciki da akasin haka ce daita ,kuma yaruwa mafi kusanci da rayuwarsa amman ya dinga nunawa duniya baya sonta , wallahi ina matukar qaunar zamansu tare amamn tunda abun ya kai ga haka nima na hakura sannan bana fushi dashi na yafe masa duniya da lahira ya kawo wacce yake so ta qarasa mgnr kuka na kwance mata .."cikin muryar kuka aunty shahida da khadija suka durkushe agaban mami suna kuka suna bata hakuri "dan allah mami Kiyi hakuri karki bari a fasa auren nan bayn an gama komai ."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
     MAR'ADAMS
     💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS USERNAME
AYSHAABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim

Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a turawa wannan  09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.

             Page 27

  Cikin muryar kuka mami tace  "har yau na kasa fahimtar me yasa adamcy baya son maryam ?me maryam ta rasa ? me yasa yake jin idan ta mutu zai ji dadi zai  huta?" ta qarasa mgnr tana goge hawayenta "Kiyi hakuri mami  zai sota in sha allahu nan suka dinga  rarrashin mami shi kuwa ATA ya qasa cewa komai sai ma ya mike   cikin yanayi na tashin hankalin ganin mahaifiyarsa na zubar da hawaye akanshi  ya bar  d'akin  zuwa nashi yana furzar da  numfashi  mai zafi ."

ko bayan fitarsa hakuri sosai  aunty shahida da aunty khadija sukai  ta bawa mami da kyar suka samu ta sauko ta hakura "kiyi hakuri mami ki yafe masa sannan ki kwantar da hankalinki muddin muna raye adam bashi da wata mata sai maryam kuma bazamu ta'ba barin tasha wahala a gidansa ba sai inda karfinmu ya qare ."sanyayyen numfashi mami ta sauke tana mai sake gyara zamanta  tare da riko hannuwansu cikin nata "na yafe masa dan ko baku nemar masa  yafiya  ba  zan yafe masa domin iyaye ne kadai suke iya yafewa ya'yansu batare da ya'yan  sun nemi yafiya daga garesu ba  ,gaba dayanku allah yayi maku albarka allah kuma ya albarkaci rayuwar ya'yanku kuje ku cigaba da shirye shiryen  biki ina alfahari daku ta qarasa  mgnr tana murmushi ".

wani farinciki ne ya mamaye zukansu suka mike  suka  fito daga dakin mami  zuwa  d'akin ATA
alokacin yana kwance flat akan  kujera  yana fidda numfashi sama sama ."Jin motsin shigowarsu ya sashi bude idanunshi da kyar sai dai  bai mike  ba har sanda suka samu waje suka zauna  suka tsura masa idanuwansu suna kallonsa, kusan mintuna goma suka d'auka suna kallonsa da nazarinsa sannan   aunty shahida ta kira sunansa "adam !"
yana jinta amman yaki  amsawa  sai ma sauke ajiyar zuciya yayi tare da furzar da zazzafar iska daga bakinsa "

"kana jina fa  adam ?"eh ina jinki ki fad'a abinda zaki fad'a  ya fad'a a takaice tare da mikewa ya zauna  yana kallon wani bangaren dabam  yana ciza gefen lip's dinsa  yayinda idanuwanshi suka canza kala dan bai ta'ba shiga tashin hankali  irin na yau ba ganin mahaifiyarsa na zubar da hawaye ,"shi kuwa me zaiyi da maryam arayuwarsa ?ai har abada bazai ta'ba sota ba zai dai yi biyayya wa mahaifiyarsa  ."

Aunty shahida ta danne abinda taji na haushin abinda yayi mata yanzu ta  soma magana cikin fushi "wallahi adam kabi duniya ahankali da girmanka da komai amamn ka dinga  sa mahaifiyarka kuka a zatonka yadda kake yiwa mami zaka ci bulus ne ?cikin yanayi na tashin hankali ya waigo ya tsura mata tsumammun idanunshi dake cike da matsanamcin tashin hankali duk da magana yake son yi amman ya kasa bude bakinsa dan haka ya runtse idanuwanshi kawai  yana janyo wani irin numfashi mai zafi yana fesarwa ya maida kanshi jikin kujera ya kwantar ."

"tsawon shekaru fa take binka akan aure ,ka mance kaine kaki fito da mata har yasa ta yanke wannan hukuncin akanta  ?"iyaye ne kadai suke son  ganin cigaban ya'yansu mami na son ganin gobenka tayi kyau ne yasa  ta hadaka da mrym sannan  karka manta kai ma aure zakayi  yanzu kuma zaka haihu yaya zakaji duk ranar da kacewa d'anka  ko 'yarka ga abinda kake so suka  ce aa ba zasu maka  biyayya ba abinda suke  só shi zasuyi   ?

"to ni yanzu me nayi kuma ?ya fad'a a matukar hassale tare da gyara zamansa ya  bude idanuwanshi a hankali ya zuba masu ya cigaba da motsa labbansa "yarinyar nan ce  bana só kuma bana jin zan sota ,sai kuma na kasa fad'ar albarkacin bakina ko ana so dole ne  ? yayi  tambayar  a dan fusace yana kallonsu ,ku tsaya na tmbyeku daga Ke har khadija auren dole mahaifinmu yayi maku ?"sukayi shiru suna kallonsa dan basu da amsar da zasu bashi "gbdynku kuna son mazajenku kuka  auresu  to me yasa sai ni dana kasance nmj  zaa wa auren dole kuma a hanani mgn ?".

"amman ai ba dole sai ka fad'a a gaban mami ba ,wannan kalmar da kake fad'a ita Ke sa mami jin wani abu aranta , dannewa ya kamata kayi ka rungume maryam ."har yanzu baku bani amsar tmbyta ba tukun kafin ku shigo da wata ,auren dole akayi maku ?"zuba masa idanu sukayi kowannensu da abinda yake sakawa aransa ,ahankali ya lumshe tsumammun  idanunshi tare da sanya hannunsa daya a saitin qirjinsa yana murza daidai inda zuciyarsa take beating very fast "gbdynku bazaku iya fahimtar quna da radadin da nake ji acikin zuciyata ba  ,so ne dai na fad'a bana sonta kuma wallahi ko yanzu aka fasa auren nan murna zanyi  mutun daya ce kawai ta samu kyakkyawan mazauni anan  itace mafarkina ,me zaayi da wannan guntuwar yarinya yarinyar Kmr agwagwa  kawai fari ne ya taimaketa ya qarasa mgnr yana cigaba da shafa zuciyarsa yana lumshe ido ."

"Wani haushinsa ya kama aunty khadija  ranta a matukar bace tace "Idan zaka  manta mafarkinka ka manta ka sanya mrym  a zuciyarka dan wannan auren mutuwa ce kawai zata ra.."Kafin ta qarashe  maganar ya jefa mata wani mugun kallo wanda yasa tayi gaugauwar yanke maganarta babu shiri ,dan girman allah adam kayi qoqari kasanya maryam ko kad'an a zuciyarka "bazan iya ba"ya fad'a atakaice "zaka iya adam kayi qoqarin kwatantawa please."
  "bama da ikon waye zamu so waye zamu fad'a soyayya dashi   bazan iya yi maku karya cewar zan sanyata a zuciyata ba   daga baya kuga akasin haka dan bazan iya karya maku zuciya daga baya kuji haushina ba ,kuyi hakuri  kawai  bazan iya ba ,sannan kusan wani abu  a kullum ina fad'a  maku amman kun kasa fahimtata kuskure zaayi a auren  nan yakamata abar maganar auren nan haka mu cigaba da rayuwarmu daita  irin ta yan'uwantaka."

"zamuyi rayuwa daita ta har abada shine maanar aure,  akwai abubuwa acikin rayuwar aure,aure   ba abu bane na takaitaccen lokaci idan anyisa anyisa kenan sai fatan mutuwa ce zata raba zata bukaci farinciki ni  km bazan ta'ba bata farinciki ba saboda ni kaina zuciyata bata tare da farinciki komai zuciyata a rufe take da soyayyar wata wato mafarkina kenan ,itama ina neman adduarku allah ya yaye min tunaninta na huta yayi maganr Kmr zai zubda hawaye . yayi shiru tare da rungume hannuwansa duka a qirjinsa yana jin wani irin tuttukin bakinciki."

"to Allah  yaye maka tunaninta kai bama tunaninta ba ni zanyi addua allah ya mantar da kai ita gbdy  kaji ka tsaneta  fiyye da komai a duniya inji cewar aunty khadija ,numfashi kawai ya sauke yana kallonta a dage batare da yace komai ba dan shi yasan ba abune mai sauki ba ya mantata.yanzu ga shirye shiryen biki  zaa shiga daga jibi ya kenan ?"
"babu ruwana da duk wani abinda zaayi na shirin biki ,ni dai abinda nasani aure ne na amince zan aureta amman batun wani shirye shirye babu ruwana" har maganar rabon iv ?"ya ina fad'a maku bani da wata damuwa da komai  da zaa gudanar kuna qara shigo min  da wani maganar rabon Iv ."yayi mgnr da fushin zuciya .

"rabu dashi aunty  shahida duk abinda ya dace salim da hisham  sunyi  ,kai kuma kaje can  ka karata da mugun halinka allah ya ganar da kai mu zamuyi komai kuma aure babu fashi sai an cikawa mami burinta  sai dai idan mutuwa zakayi ka mutu nonsense kawai  "bai sake cewa komai ba har suka mike suka bar d'akin ya koma ya kwanta lamo yana kallon saman d'akin ,ranar yini yayi kwance a d'aki cikin tsananin damuwa ."

da misalin karfe takwas na dare ya sauko kamr yadda aka saba an shirya masa dining da kalolin abinci dabam dabam ya zauan akan kujera shiru babu mami haka nan ya kasa ci ya kai hannu ya shafa kanshi zuwa fuskarsa duk tsananin yunwar da yake ji ya kasa sakawa cikinsa komai ya cigaba da zama shiru sai kusan karfe tara mami ta fito daga dakinta sanye ciki riga da zani na atamfa super tana kwallawa auta da maryam kira atare suka fito daga dakinsu suna amsawa mami ta dan yi taku zuwa dining area taja kujera ta  zauna tana cewa "maryam zuba mana abinci jikinta a sanyaye ta bude kular farko tana tmbayarta "mami me zan zuba miki  ?"
Chapter 88 · 0% Book details