← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 62 OF 100

Sashe 62

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta  riko  hannunsa  hawaye  na zuba   daga   idanunta  ta  soma tafiya   dashi  taku  d'aya  biyu  yayi ya  tsaya cak , itama  ta  tsaya  suna fuskantar  hisham naunaye  ajiyar zuciya  ta sauke  tana  goge hawayen  dake  tsiyaya  ,ahankali  ata ya zare hannunsa  dake cikin nata  ya  yarfar   sannna  ya  zura  cikin  aljihun wondonsa  yana  jan  tsaki "ya hisham! ta  kira  sunansa  a kid'eme  "banyi  niyyar  fito  da  sirrin  dake  zuciyata  ba  amamn  ya  zama  dole  na  fad'a  maka  tunda  na  fad'awa  yaya   adam babu  komai  acikin   zuciyata  sai..." karki   kuskura  kiyi  wannan ganganci  dan  kome  zaki  yi  tawa  zuciyar   bazata   amince   ba "to  kuwa  gara    ka  ksheni da hannunka  na  huta   dan  nima  bazan iya  auren  yaya  hisham ba , yana   sona  ni kuma kai nake   so.."you're  very  stupid  Kiyi  maza ki  danna  madannin  gogewa  ki gogeni  arayuwarki  da   zuciyarki  dan ni  mallakin  mafarkina   ce   " yana   gama   fad'ar  haka  ya juya  ya haye  sama  yana  taka  step   yana  magana " hisham  ka manta da shirmen   wannan  yarinyar  ka  soma  naka   shirin   domin   wannan  auren ko   zata  mutu  sai  anyisa  useless  girl  kawai  ga  inda ake  sonku  aka  damu daku   amman ku  dinga  kai  kanku  inda  bazaa  ta'ba  sonku ba nonsense "

Hisham  ya  runtse  idanuwanshi "kenan  hasashensa  ya   tabbata ,  zarginsa   ya   zama  gasky   kenan akan ata  yake  shan  wulakanci  da  tsana  da wahala a wajenta ?   ,"ya  kalleta  cike  da  tausayawa yace "daman  ata  Kike so ?jikinta  yayi mugu  mugun sanyi ta rasa  me  zata  cewa  hisham  illa ta  runtse  idanunta  gam  tana  jin  zafi  da  ciwo  mara   iyaka a zuciyarta  ,ta durkushe qasa  tana kuka tana nemawar   kanta  mafuta   dan  dole  tasan  abun  yi  kafin  a had'ata  aure  da  hisham shima  ya durkushe  gabanta  ya  dago  ha'barta  ya  sanya  kwayar  idanunshi  cikin  nata , tai  saurin  buge masa  hannu  tana  kallonsa  cike  da tsantsar  tsana "ka  kyaleni  ni wallahi  bana  sonka  tunda  burinka  kenan  na  soka  , dan  girman   allah  ka  rabu  dani  ka manta  dani,  ka  manta da maganar  ka  ta'ba  sona  arayuwarka , ka  mantani  ta qarasa  fad'ar  haka  tana  fidda huci  mai  zafi ."

"Dan  allah  kiyi  hakuri  nasan  irin ciwo da  zafin  da  Kike  ji  acikin zuciyarki  ciwo ne  kwatankwacin wanda  nake ji  acikin  zuciyata  nasan  zafin  ciwo da radadin  kana  son  wani  baya  sonka ,wallahi  na  tausaya  miki  amman  me  yasa nuzla ?"me  yasa  sai  ata  zuciyarki  zata  kamu da so byn ni  ina qaunarki  ya  kai hannunsa  yana  share   mata  hawaye"ata bashi  da  wannan  lokacin   wahalar da kanki da zuciyarki   kawai  zakiyi  babu  wannan  tausayin a zuciyarsa    a karshe  ya  rungumeta  ajikinsa   tsam  yana  shafa  bayanta   ahankali  ahankali  babu yadda ta iya dole ta  kasance  rungume  ajikinsa  domin tana  bukatar  wanda  zai  rarrasheta  kuka  take  sosai   tana  rungume   ajikinsa "ki daina  kuka  nuzla  dan  zuciyata  bazata  iya  ganin  hawayenki  da damuwarki  ina  matukar  sonki  da  zaki  bani  dama da  sannu  zaki  daina  son  ata  ki soni  ya  fad'a  yana  qara rungumeta  gam   ajikinsa   ahankali ya mike tsaye  tare  daita  ya  nufi  kofar  fita  tun kafin mutane su  shigo su  fahimci  halin da suke ciki ."

Washegarin  da  misalin  karfe tara na dare   ata ya  shiga d'akin mami  sanye  cikin  fararen kayan bacci wondo da  riga , hannunsa  rike  da black cup dinsa  dake  dauke  da ruwan coffee  ,yayinda  dayan  hannunsa Ke cikin aljihun  wondonsa  ya samu mami  tsaye a gaban wordrobe  dinta tana qoqarin  rufewa  tana ganinsa ta sakar masa murmushi tana cewa "Masha allah   adamcy nan ya karfin jikin ?alhamd sweetheart ya qoqari dani ?kwana  nawa ya saura ai Allah Allah  nike  Kayi tafiyar nan ka dawo mu sha biki  ranar bani da dama zan aurar da d'a daya tilo ya  girgiza  kai kawai yana  ajiye  cup din hannunsa  akan bedside dinta  ya tsura mata tsumammun idanunshi yana kallonta tmkr wani maraya "yaakayi adamcy nan duk sanda kayi haka akwai abinda kake son fad'a  "haka ne sweetheart kin fi kowa sanin halina alfarma nazo nema ."

"Alfarmar kuma ?mami ta maimaita abinda ya fad'a
"Eh  ina neman wata  alfamar a wajenki   sweetheart "ina sauroronka Allah yasa zan iya ,ya marairaice  murya sosai kafin ya soma mgn  "dan  darajan  Allah sweetheart ki   qara min  lokacin auren nan wallahi wallahi wallahi !!! kinji na rantse   miki zan auri yarinyar nan zabinki , wasu yan kwanakin kawai zaki qara min har naje na dawo dan  zan dauki lokaci a france daga nan ma zan wuce  hollond  yi wasu abubuwa  masu  mahimanci  a  yanzu  na samu sauyin  lokaci amman kuma idan kina ganin zaa iya yin komai ko bana nan  fine na amince a daura auren ayi komai  amman da zaa bari na dawo sai nafi farinciki kasancewar ina son a hada auren dana hisham da nuzla yadda take kallonsa ya fahimci kamar bata yarda dashi ba "na rantse fa duk   wanda  aka rantse wa bai yarda ba shi din bana allah bane nayi miki wannan alqawarin sweetheart zan aureta ".

"naji amman  har zuwa wani lokaci ni wallahi zaka sani jin kunya auren sauran kwanaki ace an daga "karki damu sweetheart idan akwai damuwa kawai ayi ko bana nan  amman na fi son ina nan ,sai kace wata tsiyar zaka kulla  ko  kana ?ya dan ciza gefen lips dinsa "bansani ba ko zan iya kulla wani abu a auren da bana só ?kaji  dashi  tunani tayi karta je a daura yaki dawowa ya bar  yar mutane da nauyi akanta  gara kawai ta qara masa lokaci idan ya dawo sai ayi"Kwanaki nawa zan  qara maka ?uhm ko  Kmr wata biyu haka yayi  "what ! kai adamcy ban yarda da kai ba ,wallahi ki yarda dani sweetheart bazan baki kunya ba,  ba kuma zan saba alkwari ba I promise you ,ka cika alqawari  adamcy ,karki damu sweetheart  na ranse fa ,shikenan  na yarda da kai ta fad'a  kafin su fad'a hirar duniya a nan yake bata labarin   nuzla  murmshi mami tayi tana cewa "adamcy  nah mai farinjini ."

Zaune  mr  ata yake  agaban hajiya zulaiheart sanye cikin suit wondo da riga bakake   jikinsa na fitar da wani  kamshi  na daga hankali   fuskar nan nashi dake kwance da kasumba tayi fresh tayi kyau tana fitar da wani haske na dabam mai daukar hankali abun ka ga fari mutun  sallama  ya shigo mata dan sauran awa daya jirgnsa ya daga zuwa kasar  france  "Allah   kiyayya ya tsare min kai , ka kular min da kanka sosai banda wasa da abinci aci abinci akan lokaci kamar yadda doctor ya fada  "in sha allahu zan kiyaye sweetheart. Allah ya qara girma,ya qara miki lafiya da nisan kwana mai amfani kema ki kular min da kanki "Ameen summa ameen nayi maka wannan alkwarin Allah yayi muku albarka gabadaya ku "inji mami ,sannan taja musu addu'a suka shafa tana shafa masa na hannunta a fuskarshi ."a tare suka mike suka fito inda tawagarsa Ke jiransa  a haraban gidan shi kadai ne zaune a bayan motarsa   limozin sai driver a mazauninshi, hawaye ya tsiyayowa mami   sanda motocinsa suke qoqarin barin gidan sai take jin kamar kar  ya tafi  amman kamar yau ne  zai dawo gareta wannan karan mami  ta kasa daurewa sai da tayi qwalla, gefe tayi da kanta tana  dauke hawayenta ."

*****

Yau  tsawon  kwana uku  kenan   mlm  yahuza yana zariyar  zuwa gidansu  maryama amman kamar  kullum    bai samu  ganinta ba  yau  ma   daga  massalaci  ya  wuto  kofar  gidansu  yana  neman yaron  da  zai  aika  cikin  gidansu  ko cikakken minti goma bai  yi da  tsayuwa ba, sai ga yaya sadam ya fito daga cikin gidan , nan  ya mika masa hannu suka gaisa "ina  fatan dai  lafiya  kwana  biyu nan  kake zuwa  gidan nan ?"Lafiya  lau wajen  maryama  nake zuwa  sai  dai duk zuwan  da  nake  yi  bana samun ganinta ,shine  dan  naci kake ta zuwa ?to ya  zanyi  sadam  tunda  zuciyata ta  kamu da matsanancin sonta  duk  da bani  da  tabbacin  ko  tana  sona amman   nasan  tana  son  fitowa inda  nake  habib  ke  hanata  fitowa  yanzu  dai  taimaka min  ka fito min  daita  dan  nasan muddin  habib na cikin gidan  bazai  barta ta fito ba ,murmushi  sadam yayi  yana cewa "kai habib  hukuma ne wannan yaron  bari ina  zuwa  !ya  juya  ya  koma   cikin  gidan  ya  shiga  side  dinsu maryama ."

a  parlour  ya  iskesu  gabadaya   suna  hirar  duniya ya  zauna  yana  fuskantar  maryama  suka  gaisa  da  aunty   sannan   maryama  ta gaishesa haka  ma  habib ya  amsa masu da "lafiya  lau cikin sakin fuska  ,ya gida da aiki sadam  ?Alhamdulillah aunty mun godewa Allah yace yana  duban  maryama "ga malamin ku  yahuza  can a kofar  gida  yana  jiranki  yau  tsawon  kwana  uku  kenan  ina ganinsa  ashe  wai saboda  ke yake zuwa  amman  bakya  fitowa."wata  irin  kunya ta  kama  maryama  ta  sunkuyar  da  kanta  kasa  tana wasa da  zara zaran yatsun hannunta".

"ai ga  d'an  albarka dake hanata  fita  nan , ko shi zai aureta bansani  ba ?yaro  qarami dashi sai aikin nuna isa da iko ita kuma shegen son dan'uwa  tana biye  masa  aunty ta  qarashe maganar tana zabgawa habib harara  ,habib  bai ce komai  ba ya tashi ya shige ciki  dan  matsawar  yana zaune  a falon bazai iya barin maryama ta fita  zuwa koina ba km hakan zai sa yaya  sadam  yaji  babu  dadi "ai  yahuza mutumin  kirki ne kuma ga dukkanin  alamun da gaske yake aunty tace "allah  yasa shi wai habib dan matsalar daake ta samu akan masu zuwa suna tafiya né yake jin haushi "nima na fahimci haka  amman in sha allahu komai yazo karshe  dan nasan yahuza bazai  mata haka ba nima gsky na yaba da hankalinsa maza  tashi  kije maryama karki dade  maryama bata ji dadi ba ganin habib ya tashi ya barsu  km tasan duk akan mgnr fita ne  ,amman babu  yadda ta  iya  yaya  sadam da aunty suna da karfin  iko   arayuwarta  ta  mike ta fita ta bar aunty da yaya sadam   suna magana bata san abinda ya cigaba da wakana  atsakaninsu ba ."
Chapter 62 · 0% Book details