Sashe 28
Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rai a matukar bace hjy zulaiheart ta shiga bangaren ATA tana gama shiga ta fara zuba masa fad'a " tur da haihuwarka Adam " ya waigo a matukar firgice yana zaro Idanu lokaci guda yay fillinging da wayar dake rike a hannunsa ya zube kan gwiwowinsa kasan a gabanta cikin tsananin tashin hankali muryarsa a shake yace "sweetheart me nayi ?"dan Allah ki yafe min ,kiyi min afuwa bazan sake ba."
hjy zulaiheart ta nuna sa da yatsa "Kai Adamcy ban ta'ba sanin baka da hankali da tunani ba sai yau , yau tsawon shekaru Ina binka akan magana daya amman babu komai na rantse da girman Allah bazan sake maka magana akan batun aurenka ba ka cigaba da rayuwarka haka har mutuwa ta riskeka tunda baka san mutuncin kanka ba, ga yarinya yar mutunci yar'uwarka amman dai..."sai tayi shiru tana huci ta kasa cigaba da mgn sai lokacin ya fahimci laifinsa ."
ya sunkuyar da kansa kasa yayinda mami ta cigaba da magana cikin zafin rai "idan baka so maryam ba wa yakamata kaso?" ba dan maryam na diyar dan'uwana ba tana da nagarta da kamun kan da kowani nmj zai sota Kuma mahaifinta nada nagarta da zai zama surukinka "ai ka nuna min ban Isa da Kai ba ko ? to na gode Allah ya saka da alkhairi Allah ya biya ."
"a'a sweetheart wallahi kin Isa dani sai dai zuciyata ta kasa ..."mami tayi saurin tareshi da cewa ",aikin banza daga yau in nice na haifeka to ka fara shirin aurenka da maryam Koda yin hakan yana nufin rasa komai naka ATA ya kalleta da sauri sannan yace "to sweetheart zanyi duk yadda kike so sai dai naso ki dan saueareni kiji ita kanta yarinyar bata ..."
Mami ta juya a matukar fusace tana cewa "bazan saurari komai daga bakinka ba ni dai na fad'a maka muddin nice uwarka ka shirya rayuwar aure da mrym idan baka zo ka sameni da maganar aurenta a daren yau ba na rantse maka da girman Allah sai dai ka nemi wata uwar bani zulaiheart ba kayi abinda nake so shine zaman lafiyarka dani ta karasa fita tana magana cikin tsananin fushi da bata ta'ba yin irinsa ba ."
ATA ya rike kanshi tare da furta "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun"shikenan zuciyarsa ta sake shiga rud'ani kasa ya zame ya zauna akan capet tare da zabga tagumi tunani yake yi yanxu ya zai yi kenan?"shin ya cigaba da kafewa akan ra'ayinsa ne ko Kuma ya hakura ya aureta a wuce gurin ?cike da sanyin jikin ya mike ya nufi bangarenta Yana kokarin shiga part dinta sukayi karo da maryam itama d'akin hjy zulaiheart zata sakmakon kiranta datayi ."
wani irin gigitacen mari ya ɗauketa dashi Sanna ya rufeta da duka "kina hauka ne da zaki hada jikinki danawa ? kasa tayi dafe da kuncinta tana kallon zara zaran yatsun ka'fafunsa dake jere kowannensu dauke da kwantaccen gashi ,koina ajikinta rawa yake "mahaukaciya kawai ko ni sa'anki ne ?ta d'ago tana dubansa sai faman huci yake "Maza ki d'auke wad'an nan banzayen idanun naki akaina wallahi ban taba jin na tsani wani halitta ba kamarki har kece zaki bude baki ki fuskanci 'yan'uwana da Kalmar baki sona saboda ke din dakikya ce da bata san hallici ba yasa kafarsa d'aya ya take mata kafa yana watsa mata kallon banza ."
"ki sani bana sonki kuma har abada bazan soki ba wani abu taji ya caki zuciyarta tare da kafeshi da idanunta da suka canza kala zuwa na bacin rai yayinda wani bakinciki ya tokare mata kahon zuciya wanda yasa hawayen ya cika idanunta amman ta danne taki barin su zuba tunda take baa ta'ba mata wulakanci irin na yau ba wannan shine karo na biyu da ya daura hannunsa ajikinta ranta yayi matukar baci tana son ta bar wajen amman bazata iya ba bazata iya ba dan batasan me zai sake biyowa baya ba ,dan haka ta kife kanta akasa kuka take son tayi amman bata son tayi akan wani banza da bai san darajarta ba ..."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS
AYSHABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 11
" har tsawon wannan lokacin yana tsaye yana mata kallon kaskanci kafin daga bisani ya d'an motsa labbansa " biyayya Kawai zan yiwa mahaifiyata na aureki sai dai zakiji jiki sai kinyi da kin sanin kalmarki gareni, zakin san kin ta'boni yana gama fad'ar haka ya d'auke kafarsa tare da shure mata kafa ya nufi cikin part din mahaifiyarsa ransa a dagule .
girgiza kai mryam ta shiga yi kafin daga baya ta rarrafa ta shige parlour'nsu ta ra'be a bakin kofar d'akin tana kukan zuci , cikin yanayi na tashin hankali take furta "me na tsare maka ya adam ? "me yasa baka sona ? "me yasa ka tsaneni hk ? haka tayita jerowa kanta tambayoyin da bata da mai bata amsa sai shi shi din kuma bata isa ta tuknkaresa ba gbdy Idanunta sun canza qala tsabar tashin hankalin data tsinci kanta ."
kuka take son yi sai dai zafin da zuciyarta ke yi yasa hawayenta yaki diga sai idanuwanta gbdy sun burkice " baka sona amman ya zama dole na jurewa komai muddin ina son rabuwa da iyayena lafiya , bazata manta kalman mahaifinta ba alokacin da zata dawo daga abuja domin sun samu kyakkyawan mazauni acikin kwalkwaluwarta "maryam muddin ni ne wanda nayi sanadiyyar zuwanki duniya Kuma kina son gamawa da duniya lafiya ki auri adam bisa umarnina Kuma ki zauna dashi zama na amana bisa umarnina , yau ace ba yar'uwata ce ta nemi wannan hadin ba sam bazan takura miki ba zan barki har sanda zaki kawo min irin mijin da kike so .."
A bakin gado ya iske hjy zulaiheart ta cika tayi bam ,cikin sanyi jikin nan nashi ya k'araso ya zauna a gabanta yana neman gafararta , ko kallon Inda yake bata yi ba daga karshe ma ta kawar da fuskarta gefe al'amun bata son ganinsa ya runtse idanuwanshi sosai yana sauke numfashi ,byn kmr second biyar ya bud'e idanunshi ya fara Kame kame "uhm ammm kiyi hakuri sweetheart , afuwa sweetheart I will not do it again , inshallahu I promise you zan aureta ."
"hjy zulaiheart taji dadin jin furucinsa har cikin ranta sai dai ta share tana jan tsaki a fili. "ki yarda sweetheart duk duniya babu wanda zai soki da son farincikinki kmr ni ,kiyi hakuri bazan juri ganin 'bacin ranki ba ya fad'a yana riko hannunta , naunayen ajiyar zuciya ta sauke batare data fuskancesa ba ,duk da zuciyarta ta d'an yi sanyi dan daman fushin na dole ne yanxu kuwa ta hakura .
damuwarta daman yayi aure tana son taga aurensa taga ya'yansa kamar yadda taga na sauran yaranta amman duk da haka bazata sakar masa fuska ba dan tasan halinsa kamar yunwar cikinta canzawarsa bai da wuya ya d'auki mintuna masu tsawo agabanta bata daga Kai ta kallesa ba sai ma ta mike zata bar masa d'akin , ya mike da sauri jikinsa na kyarma ya tareta dan sosai ya hango damuwa qarara akan fuskarta ya sake kamo hannuwanta duka cikin nashi , ta fizge a fusace tana watsa masa harara "sweetheart kiyi hakuri dan girman Allah wallahi zan aureta trust Adamcy zai aureta tunda yace zaiyi wallahi wallahi zan aureta Koda kuwa zan rasa rayuwata....."
hannunta d'aya tasa ta zare hannunta daga cikin nashi ta tsura masa idanunta "wallahi ban san Inda ka d'auko halinka ba , sam mahaifinka ba haka yake ba mutumin kirki ne, mahaifinka baya uhm baya uhm bare miskilanci , kullum cikin neman yadda zai kyautata mana daku ya'yansa da 'yan'uwansa yake , a kullum mahaifinku so yake ku zama na gari a rayuwa sannan masu jin kan iyaye da tausayi Allah ya duba bayan mahaifinku cikin kaf ya'yan mahaifinka Kai ne kawai ka fita dabam acikinsu da wasu halaiya Kai ma Kuma wannan halin miskilancin da zafin zuciyar ne illarka tun kafin ya rasu ya fad'a yace bashi ka d'auko ba .bari na fad'a maka gsky wannan halin naka sam ba nashi bane Kai ka san Inda ka samo abunka dan shi ba haka yake yi ba, dan ta mahaifinka duniya bazai tashi ba ,ga rikon addinin ga tsananin zumunci da sanyi hali ."
ga lokaci yazo daya kamata ka tattara biyayyar Uba da uwa ka had'a kayi min amman kullum cikin musguna min kake akan zance aure auren da kai ne kaji dadinsa , wallahi duk macen data samu miji irin mai halin mahaifinka ta gama dace a duniya da lahira ni kaina kullum kukan da nake yi kenan mahaifinka ya bauta mana ya sangartani sannan ya bautawa zumunci Allah ya jikansa yasa aljanna ce makomarsa ka canja idan zaka canza tana gama fad'ar haka ta fita ta barshi cike da zafin zuciya."
Jiki a sanyaye ya bar d'akin zuwa nashi yana shiga d'akinsa ya shiga zariya kwalkwaluwarsa ta shiga tunani , sai dai Kansa ya toshe ya cunkushe guri d'aya ya kasa tunanin komai ya zauna a bakin gado ya had'e hannunwansa duka a ha'barsa yana tunanin can byn wasu mintuna ya mike ya koma kan bedside ya zauna yayi shiru yana kallon d'akin ,sake mikewa yayi ya d'aura Kashi akan katifa yana Jin quna a ransa.
hjy zulaiheart ta nuna sa da yatsa "Kai Adamcy ban ta'ba sanin baka da hankali da tunani ba sai yau , yau tsawon shekaru Ina binka akan magana daya amman babu komai na rantse da girman Allah bazan sake maka magana akan batun aurenka ba ka cigaba da rayuwarka haka har mutuwa ta riskeka tunda baka san mutuncin kanka ba, ga yarinya yar mutunci yar'uwarka amman dai..."sai tayi shiru tana huci ta kasa cigaba da mgn sai lokacin ya fahimci laifinsa ."
ya sunkuyar da kansa kasa yayinda mami ta cigaba da magana cikin zafin rai "idan baka so maryam ba wa yakamata kaso?" ba dan maryam na diyar dan'uwana ba tana da nagarta da kamun kan da kowani nmj zai sota Kuma mahaifinta nada nagarta da zai zama surukinka "ai ka nuna min ban Isa da Kai ba ko ? to na gode Allah ya saka da alkhairi Allah ya biya ."
"a'a sweetheart wallahi kin Isa dani sai dai zuciyata ta kasa ..."mami tayi saurin tareshi da cewa ",aikin banza daga yau in nice na haifeka to ka fara shirin aurenka da maryam Koda yin hakan yana nufin rasa komai naka ATA ya kalleta da sauri sannan yace "to sweetheart zanyi duk yadda kike so sai dai naso ki dan saueareni kiji ita kanta yarinyar bata ..."
Mami ta juya a matukar fusace tana cewa "bazan saurari komai daga bakinka ba ni dai na fad'a maka muddin nice uwarka ka shirya rayuwar aure da mrym idan baka zo ka sameni da maganar aurenta a daren yau ba na rantse maka da girman Allah sai dai ka nemi wata uwar bani zulaiheart ba kayi abinda nake so shine zaman lafiyarka dani ta karasa fita tana magana cikin tsananin fushi da bata ta'ba yin irinsa ba ."
ATA ya rike kanshi tare da furta "inna lillahi wa inna ilaihi rajiun"shikenan zuciyarsa ta sake shiga rud'ani kasa ya zame ya zauna akan capet tare da zabga tagumi tunani yake yi yanxu ya zai yi kenan?"shin ya cigaba da kafewa akan ra'ayinsa ne ko Kuma ya hakura ya aureta a wuce gurin ?cike da sanyin jikin ya mike ya nufi bangarenta Yana kokarin shiga part dinta sukayi karo da maryam itama d'akin hjy zulaiheart zata sakmakon kiranta datayi ."
wani irin gigitacen mari ya ɗauketa dashi Sanna ya rufeta da duka "kina hauka ne da zaki hada jikinki danawa ? kasa tayi dafe da kuncinta tana kallon zara zaran yatsun ka'fafunsa dake jere kowannensu dauke da kwantaccen gashi ,koina ajikinta rawa yake "mahaukaciya kawai ko ni sa'anki ne ?ta d'ago tana dubansa sai faman huci yake "Maza ki d'auke wad'an nan banzayen idanun naki akaina wallahi ban taba jin na tsani wani halitta ba kamarki har kece zaki bude baki ki fuskanci 'yan'uwana da Kalmar baki sona saboda ke din dakikya ce da bata san hallici ba yasa kafarsa d'aya ya take mata kafa yana watsa mata kallon banza ."
"ki sani bana sonki kuma har abada bazan soki ba wani abu taji ya caki zuciyarta tare da kafeshi da idanunta da suka canza kala zuwa na bacin rai yayinda wani bakinciki ya tokare mata kahon zuciya wanda yasa hawayen ya cika idanunta amman ta danne taki barin su zuba tunda take baa ta'ba mata wulakanci irin na yau ba wannan shine karo na biyu da ya daura hannunsa ajikinta ranta yayi matukar baci tana son ta bar wajen amman bazata iya ba bazata iya ba dan batasan me zai sake biyowa baya ba ,dan haka ta kife kanta akasa kuka take son tayi amman bata son tayi akan wani banza da bai san darajarta ba ..."
Mmn sudais
💗💗💗💗💗💗
MAR'ADAMS
💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
*AYSHA A BAGUDO*
WATTPAD @HAUESH
AREWABOOKS
AYSHABAGUDO
bismillahirrahmanirrahim
Wannan littafin na kudi ne mai bukatar karantashi byn na kammalashi zai biya 1000 ta wannan account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina (Hausa bakwai ) a YouTube.
Page 11
" har tsawon wannan lokacin yana tsaye yana mata kallon kaskanci kafin daga bisani ya d'an motsa labbansa " biyayya Kawai zan yiwa mahaifiyata na aureki sai dai zakiji jiki sai kinyi da kin sanin kalmarki gareni, zakin san kin ta'boni yana gama fad'ar haka ya d'auke kafarsa tare da shure mata kafa ya nufi cikin part din mahaifiyarsa ransa a dagule .
girgiza kai mryam ta shiga yi kafin daga baya ta rarrafa ta shige parlour'nsu ta ra'be a bakin kofar d'akin tana kukan zuci , cikin yanayi na tashin hankali take furta "me na tsare maka ya adam ? "me yasa baka sona ? "me yasa ka tsaneni hk ? haka tayita jerowa kanta tambayoyin da bata da mai bata amsa sai shi shi din kuma bata isa ta tuknkaresa ba gbdy Idanunta sun canza qala tsabar tashin hankalin data tsinci kanta ."
kuka take son yi sai dai zafin da zuciyarta ke yi yasa hawayenta yaki diga sai idanuwanta gbdy sun burkice " baka sona amman ya zama dole na jurewa komai muddin ina son rabuwa da iyayena lafiya , bazata manta kalman mahaifinta ba alokacin da zata dawo daga abuja domin sun samu kyakkyawan mazauni acikin kwalkwaluwarta "maryam muddin ni ne wanda nayi sanadiyyar zuwanki duniya Kuma kina son gamawa da duniya lafiya ki auri adam bisa umarnina Kuma ki zauna dashi zama na amana bisa umarnina , yau ace ba yar'uwata ce ta nemi wannan hadin ba sam bazan takura miki ba zan barki har sanda zaki kawo min irin mijin da kike so .."
A bakin gado ya iske hjy zulaiheart ta cika tayi bam ,cikin sanyi jikin nan nashi ya k'araso ya zauna a gabanta yana neman gafararta , ko kallon Inda yake bata yi ba daga karshe ma ta kawar da fuskarta gefe al'amun bata son ganinsa ya runtse idanuwanshi sosai yana sauke numfashi ,byn kmr second biyar ya bud'e idanunshi ya fara Kame kame "uhm ammm kiyi hakuri sweetheart , afuwa sweetheart I will not do it again , inshallahu I promise you zan aureta ."
"hjy zulaiheart taji dadin jin furucinsa har cikin ranta sai dai ta share tana jan tsaki a fili. "ki yarda sweetheart duk duniya babu wanda zai soki da son farincikinki kmr ni ,kiyi hakuri bazan juri ganin 'bacin ranki ba ya fad'a yana riko hannunta , naunayen ajiyar zuciya ta sauke batare data fuskancesa ba ,duk da zuciyarta ta d'an yi sanyi dan daman fushin na dole ne yanxu kuwa ta hakura .
damuwarta daman yayi aure tana son taga aurensa taga ya'yansa kamar yadda taga na sauran yaranta amman duk da haka bazata sakar masa fuska ba dan tasan halinsa kamar yunwar cikinta canzawarsa bai da wuya ya d'auki mintuna masu tsawo agabanta bata daga Kai ta kallesa ba sai ma ta mike zata bar masa d'akin , ya mike da sauri jikinsa na kyarma ya tareta dan sosai ya hango damuwa qarara akan fuskarta ya sake kamo hannuwanta duka cikin nashi , ta fizge a fusace tana watsa masa harara "sweetheart kiyi hakuri dan girman Allah wallahi zan aureta trust Adamcy zai aureta tunda yace zaiyi wallahi wallahi zan aureta Koda kuwa zan rasa rayuwata....."
hannunta d'aya tasa ta zare hannunta daga cikin nashi ta tsura masa idanunta "wallahi ban san Inda ka d'auko halinka ba , sam mahaifinka ba haka yake ba mutumin kirki ne, mahaifinka baya uhm baya uhm bare miskilanci , kullum cikin neman yadda zai kyautata mana daku ya'yansa da 'yan'uwansa yake , a kullum mahaifinku so yake ku zama na gari a rayuwa sannan masu jin kan iyaye da tausayi Allah ya duba bayan mahaifinku cikin kaf ya'yan mahaifinka Kai ne kawai ka fita dabam acikinsu da wasu halaiya Kai ma Kuma wannan halin miskilancin da zafin zuciyar ne illarka tun kafin ya rasu ya fad'a yace bashi ka d'auko ba .bari na fad'a maka gsky wannan halin naka sam ba nashi bane Kai ka san Inda ka samo abunka dan shi ba haka yake yi ba, dan ta mahaifinka duniya bazai tashi ba ,ga rikon addinin ga tsananin zumunci da sanyi hali ."
ga lokaci yazo daya kamata ka tattara biyayyar Uba da uwa ka had'a kayi min amman kullum cikin musguna min kake akan zance aure auren da kai ne kaji dadinsa , wallahi duk macen data samu miji irin mai halin mahaifinka ta gama dace a duniya da lahira ni kaina kullum kukan da nake yi kenan mahaifinka ya bauta mana ya sangartani sannan ya bautawa zumunci Allah ya jikansa yasa aljanna ce makomarsa ka canja idan zaka canza tana gama fad'ar haka ta fita ta barshi cike da zafin zuciya."
Jiki a sanyaye ya bar d'akin zuwa nashi yana shiga d'akinsa ya shiga zariya kwalkwaluwarsa ta shiga tunani , sai dai Kansa ya toshe ya cunkushe guri d'aya ya kasa tunanin komai ya zauna a bakin gado ya had'e hannunwansa duka a ha'barsa yana tunanin can byn wasu mintuna ya mike ya koma kan bedside ya zauna yayi shiru yana kallon d'akin ,sake mikewa yayi ya d'aura Kashi akan katifa yana Jin quna a ransa.