← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 100

Sashe 29

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

zuciyarsa  na  dokawa  da matsanacin karfin  gaske ya  tashi ya nufi falonsa ya  bud'e  fridge  ya d'auki kwalin   stute superior cranberry   me sanyi ya d'auki  glass  cup ya d'aura  drink akan  center  table  ya  juya jiki a mace ya  koma  zuwa  d'akinsa ya  d'auko kwalin sigari  rotimax   ya  dawo    ya    koma  kan  kujera ya zauna  ya  tsiyaya ruwan lemun   ya d'aura kafafuwansa  akan table tare  da hard'esu guri d'aya  ya Kai  Karan sigari bakinsa  ya  kunna ya fara  zuka a hankali yana fitar  da  hayaki "yaushe rabonsa da sha ? sam bazai tuna yaushe rabonsa dasha ba  cike da izza itama sigarin yake zuka idan ba  an fad'a  maka ba bazaka  ta'ba  sanin  shi din mashayin    shigari  bane koda yake  baya sha  sai idan ya tsinci Kansa cikin ' bacin   rai mai tsanani  " .

yayi  shiru  yana zuka sigari  yana  tunani   mahaifinsa   yasan  da yana raye duk runtsi  da hkn  bata faru  dashi ba , shiyasa yake son mahaifinsa  Sosai wasu hawaye  masu zafi suka zubo  masa  wanda  rabonsa  daya zubar da hawaye  har  ya manta a tsawon rayuwarsa amman  yau  ya tuna qalbinsa masoyinsa  , ana  cewa mutun  yafi  son mahaifiyarsa  akan mahaifinsa  shi  dai sai dai
sonsu  yazo d'aya  a ransa , yasan soyayyarsu suyi  kanka  da juna  ,mahaifinsa ya  soshi  har  cikin  ransa  idan  yana  cikin damuwa  sai ya  fishi shiga  damuwa ,   haka idan yana cikin farinciki  ,daf  da zai  rasu  da zarar ya kyalesa sai  ya  fashe  da kuka alokacin  hjy zulaiheart  ke tmbyrsa  dalilin  kuka  sai  yace  "ba kowa nake wa kuka  ba  sai  Adam ,Ina jin  tausayin  rayuwar Adam  bashi da  dan'uwa kamar sauran mutane naso sun kasance su biyu ya samu abokin shawara  "a  she tabbas shi  din  abun  tausayi ne bai  ta'ba  sani ba sai a  tsakanin   wannan lokacin da abubuwa  suka  kwa'be masa  yan'uwansa mata sun had'e kai da mahaifiyarsa yasan da yana da dan'uwa nmj zai iya bin bayansa Koda kuwa zaa fi  karfinsa  ne hawaye ke gangaro  masa  kamar  karamin yaro  yana  cigaba da  busawa  cikinsa hayaki  ."

ranar  a zaune ya kwana cikin   tsananin   tashin  hankali  Kash da Kashi  damuwar auren dole da za'a masa da  tunanin  Nurul qalbinsa   dan   da  zarar  ya  runtse  idanuwanshi dan bacci  sai  yaga hoton princess dinsa  tana  gargadinsa  akan  auren da zai yi  tana gudu tana binsa  tana furta kar yayi aure ya  barta  .tsawon sati  guda  tunda daya amince  da  batun auren mryam  bai sake zuwa Inda  mami   take  ba yana  d'akinsa  yaki barin ya  had'u  da kowa   dan gbdy  fita  ya fita ransa gbdy  soyayyar princess ya  dawo  masa sabo fil  ganin  tunanin  bazai bar kanshi  ba yasashi  mikewa daga kwance da yake  tare  da  zura  takalmi  silifas   ya  fito ya  shiga d'akin  zanensa ya tsaya a gaban hotonta  shiru yana  kallonta kmr yayi mata  mgn  ta amsa fuskarta  d'auke da murmushin  da shine ya zanata  ."

Hannu  ya  kai  ya  ja hoton  a zuciye   ya  yaga  yana  furzar da iska mai zafi daga  bakinsa"A ina kike  tsawon shekaru  ?"a Ina  zan  ganki ?"kin hanani  ganinki,kin hanani sukuni   daga yau kin zamo tarihi  gareni  bazan sake damuwa  dake ba ,bazan sake tunaninki ba zan manta dake arayuwata ,zan cire soyayyarki a zuciyata tunda baki da imani baki da tausayi ya fad'a yana wani irin ihu tare da daga hannuwansa duka sama "haaaaaaaa!!!

  "Hauka  yake  sosai yana  wargaza  komai  dake  cikin  d'akin tare da cigaba da yaga hotunan zanenta  yana  filinging  dasu  har  da  system  dinsa da tsarkar wuyansa wanda zanen hotonta ne aciki , gbdy  ya  hargitsa d'akin  yana  watsi  da komai   har  sanda  mahaifiyarsa  ta shigo  hannunta  rike  da cup wanda  yake d'auke  da ruwan coffee,  bedroom dinsa  ta shiga bata gansa ba dan ita kanta ta kasa jurewa rashinsa na tsawon   kwanaki , ganin baya ciki ta fito har zata fita   ta jiyo sautinsa  a hargitse dan haka ta shigo d'akin ."

ta tsay a bayansa  ta cigaba da kallonsa cikin tsananin tashin hankali mara misaltuwa  bai sani ba  yayi  zurfi  cikin tsananin  damuwa  cikin haka  ya  sake d'aukar hoton  zanen princess  yay  sama dashi sai akan fuskar hjy zulaiheart ta runtse   idanunta da sauri   jikinta na  rawa kamar   ance  ya juyo  ya ganta  tsaye  tana kallonsa  cikin tsananin tashin  hankali  sanye da doguwar  rigar shadda  milk  colour mai  dogon hannu    kyam   idanunta a  kanshi  ta kasa daukewa  ."

cikin  sauri  dunkule hannunsa ya naushi iska tare da durkushewa   kasa  ya  soma tattara kayan  daya  hargitsa yana  cewa "so..sorry  sweetheart am really  sorry    cikin  in Ina, numfashi  ta sauke da ajiyar  zuciya  sannan ta zauna  a  bakin  gado batare  da  ta ajiye  cup din hannunta ba sai dai har lokacin idanunta na Kansa tana jin ciwo da zafin halin da yake ciki   ,kusan minti biyar tana zaune tana kallonsa yana faman tattara d'akin yana mata  sannu  sannan ta fara magana a tsanake  ." kayi hakuri   Adamcy  karka  damu  da  wannan"

  ya  k'arasa  kwashe  kayan  da  yayi waste dasu  zuciyarsa  na zafi  da quna  "kana jina  Adamcy   ita  rayuwa  babu  takurawa  idan baka sameta  anan ba wata  Killa  zaka sameta a aljanna  ,yakamata  ka gane   hakan , karka  shiga rud'ani  idan an  fad'a maka  gasky  illa  ka dinga  yarda   dashi , komai na duniya  babu  sauki  kmr yadda  ka d'aukeshi sai   an   jajirce  be a man Adamcy  karka lalata rayuwarka  akan yarinyar  mafarkinka ."

"kamar  yadda  na  sha fad'a  maka ba kowani mafarki  ke  zama gaskiya ba , ta mike a hankali   ta k'araso  gurinsa ta riko hannunsa  tayi  taku  biyu ta  zaunar dashi akan kujera  kwaya d'aya  dake d'akin , madadin ta bashi coffee  din hannunta sai  ta  fita  gabanta na dokawa da matsanacin karfi dan nan duniya idan akwai abinda ta tsana to bai wuce  damuwar tilon d'anta ba , sam  bata son ganinsa  cikin damuwa ko  wannan auren ma zata yi masa ne dan dole  saboda tasan  muddin batayi masa ba zai iya kare rayuwarsa haka  batare da yayi ba  ."

ko  cikakken minti  biyar  batayi ba ta  dawo  da gorar   ruwa  mai  sanyi  ta mika  masa , babu  mutsu ya kar'ba  ya  kafa a bakinsa bai  cire ba sai daya shanye  tasssss sannan ajiye  yana sauke numfashi taja hannunsa zuwa bedroom dinsa yana biye daita  yana zance  zuci .ya yarda  tabbas  mahaifiyarsa na sonshi kuma gsky take fad'a masa akan yarinyar  mafarkinsa  sai dai ya rasa dalilin da  har wannan lokacin ya kasa yarda iya mafarki  ne  kawai  soyayyarsa  zata tsaya ..."

Tana shiga d'akinsa ta  zauna akan gado  ya kwanta  ya  d'aura kanshi akan   cinyarta  yana mai Jin   damuwarsa tana raguwa ,  a hankali ta Kai hannunta  saman  sumar kanshi ta fara  shafawa   tana mai sake jin  tsananin  son  d'anta  Ina ma  zata ga wannan yarinyar a zahiri da babu abinda  zai  hana bata  mallaka masa  ita  ta kowani  hali  ba ."
ta  dade  zaune har bacci yayi  awon gaba dashi Sannan ta d'auke kanshi ta  maida kan pillow ta lullu'be  masa rabin jiki ta sauko  ta  qara  masa karfin  ac ta kashe masa wuta   ta  duka tayi  kissing  din foring head dinsa tana sake shafa  sumarsa sannan ta  nufi  kofar fita  tana  rufo  masa kofar ."

  Koda ta koma d'akinta  kasa  runtsawa tayi   tana tsaye akan ka'fafunta tana Kai wa Allah  kukanta akan lamarin  tilon d'anta  sai da  tayi  sallah asuba sannan  ta d'an  kwanta Shima  bata  wani dade ba  ta farka ta  shiga wanka ta fito  ta shirya cikin  doguwar  riga   ta sanya  awarwaro da zobin   ziniri ta feshe ilahirin jikinta da turaren humura  mai sanyi kamshi hjy zulaiheart  kenna  Allah yayita  da son kwaliyya da son kamshi  tun tana matashiyarta  har zuwa wannan lokacin da tsufa yazo mata  ta  fito zuwa  babban  parlour'nta  tare da  danna bell din bangaren   masu aiki kafin  kace me  gbdy sun  hallara   sun   zube  a gabanta  suna gaisheta cike da girmamawa. ta  dubesu  tare da amsawa cikin tsananin farinciki dan tana da sakewa da masu aikinta bata zalintarsu sannan bata son su zalinceta yadda take jin dadin zama dasu haka suma suke yabonta da yi mata fatan alkhairi a rayuwarta .

Fuskarta a sake ta bawa 'yan aikinta  umarni abinda  take bukata su dafa a ranar wanda zai zamo  na sadaka ne  kasancewarsa juma'a  "yau  za'a yi  abincin sadakan   da aka saba yi amman ina son  a qara  hannu  sannan a had'a da  wake  da shinkafa Ina son a rabawa  yara kanana  suka  amsa  da "to"  sannan kowace ta soma k'okarin  mikewa "ke tabawa ..." wacce aka kira da tabawa ta tsaya sauran  suka kama gabansu dan fara aiwatar da aiki "ki shirya breakfast  wa sauran jamar gida idan kin gama ki hanzarta sanar dani  ."

"shikenan hajiya itama ta fad'a  tare da juyawa da sauri ." Hjy zulaiheart tana zaune mrym da nana hauwa'u suka  shigo  duk suka zauna suka sanyata a tsakiya  kowacce hannunta empty   babu Komai kamar Koda yaushe  sun baro wayoyinsu    na  gado  a d'akinsu  d'aya byn daya suka  gaisheta   ta amsa cike da sakin fuska a fili  tace   "yau  dai babu danne danne waya ko Kuma an  gaji  da rike wayar ne ?
sukayi murmushi  nana hauwa'u tace " ai tun wuri nayiwa marsi kashedi muddin yaya adam zata aura ta saukakawa kanta akan shiga yanar gizo "wannan haka ne domin zai iya kawo rashin jituwa a tsakaninsu abinda bazan so  faruwarsa ba kenan  nafi bukatarta zaman lfy atsakaninsu. 

ta Kalli bangaren da  nana hauwa'u take zaune  tace " ya batun shari'a da ake da yarinyar da ake zargi ta kashe mubina ne har yanzu na kasa fahimtar gskyr magana gashi Adamcy nata k'okarin shiga cikin maganar  uncle jay ya hana ?"ai gsky gara da  uncle jay ya hana  wani shari'a za'a yi mami  Abar ko waye da Allah kawai mubina dai ta rigada ta mutu bazata dawo ba komai za'ayi ,haka Allah ya qaddaro mata nata mutuwar zata  rataya a wuyan wani inshallahu ruhinta na aljanna suka had'a baki gurin cewa" Ameen "
Chapter 29 · 0% Book details