← Book details Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 12 OF 100

Sashe 12

Mar'adam's Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ta samu  guri  ta  zauna  jagwab  akan d'aya  daga cikin kujerun Parlour'n   tana sauke ajiyar zuciya har lokacin wani iri take ji ajikinta , shiru parlour'n   baka Jin motsin komai sai na AC  dake aiki a falon  .
ko cikakken    minti   biyar batayi ba ta fara Jin motsin mutane , ta d'ago a hankali  masu aiki ta gani cikin shigarsu ta kullum  dukkaninsu rike da farantin silver suka rusuna tare da had'a baki "barka da zuwa hajiya "barka sannuku  ya aiki ?"
"alhamdulillah !   suka amsa tare da ajiye tire suna tambayar abinda za'a kawo mata  " me za'a  kawo miki hjy  akwai rice and stew akwai tuwon shekafa akwai dabmu  shimkafa akwai ......? "duk  babu wanda zanci aciki ta fada tana runtse idanunta dan kanta wani irin sarawa yake kmr ana buga mata guduma  ,tana nan zaune hajiya zulaiheart ta shigo cikin shigar alfarma doguwar rigar lace  har kasa wanda kimanin kudinsa ya Kai 500k ta zauna akan kujera mai zaman mutun d'aya  tayi shiru  tana duban fuskar babbar diyarta "lafiya  shahida duk na ganki haka ?a hankali ta bud'e idanunta ta saukesu  akan  hajiya zulaiheart   "wallahi  mami wata mutuwa akayi mana agurin aiki mai shiga jiki ko ince an kashe yarinyar  ......"

"Inna lillahi wa inna ilaihi rajiun oh ni zulai me mutane suka d'auki rayukan mutane ne yanzu
kashe mutun bai musu wahala ?"wallahi mami sai ma Kinga yayan yarinyar abun tausayi marayu ne babu uwa babu uba sai Allah abun daya fi d'aga min hankali yankar rago akawa yarinyar abun tausayi sam babu Imani a zukatan  wasu  mutane taya zan iya kashe mutun da hannuna ?ta karasa maganar hawaye na zubo mata."uhm  duniya  kenan  Allah dai ya tona asiri ko suwaye  suke bin ya'yan mutane  har gida suna kashesu to Kalli mutuwar mubina kigani abu kamar wasa har an kusan shekara biyu amman har yanzu babu labarin wanda yayi kisan."
Allah dai ya kyauta sam kasar nan babu tsaro shiyasa  nasa aka qara  tsaro mai karfi a gidan nan."

"hajiya ai ita sadear ana zargin makwafciyarsu ce tabi dare ta  kasheta yanzu haka maganar da nake miki tana hannu jami'an tsaro zasu fara bincike akanta  "alhamdulillah ai gara kam ita kuwa me yayi zafi haka ko akan me zata kasheta  ?mutumin  duniya   hjy ai  ba'a  iya mutumin  duniya sai Allah daya haliccesa, Allah dai ya sawaka kawai zamuce ."
"Ameen inji cewar hjy "wai  Ina maryam  da  auta suka shige ne ? sunje gidan zabiba amman dai
nasan zuwa la'asar idan anci sa'a babu traffic zaki gansu sun dawo " Anya kuwa zan jira har wannan lokacin ? bari kawai nazo na wuce  gida ."

"kin kuwa fada ma maryam   batun wannan sarkin zuciya ?"wallahi a'a jiya dai  nayi kokarin had'asu  gbdy a office dina  sai Kuma hakan bai yiwu ba ga yau ma ,Ina ganin sai dai weekend  zanzo  dan gbdy  jina nake wani iri, wallahi  mutuwar nan  ta shigeni  yarinya mai kirki da biyyaya  da sanin ya kamata  sam sadear bata da matsala a rayuwarta  sannan bata da abokin fada kowa nata ne agurin aiki  ga wasa  da  dariya ga ..."kira ne ya shigo wayar aunty shahida wanda yayi sanadiyyar katse mata magana  ta d'auka tana duba screen din wayar  direbanta  ne mlm garba  dan  haka ta mike  ta d'auki jakarta tayi wa hjy zulaiheart sallama ko a gidanta  ma kasa tabuka komai tayi babbar  yarinyarta madina duk  ta damu sai  faman tambayarta take ta fada abinda ke damunta bata ,boye mata komai ba ta fada mata mutuwar , mutuwar tsaye madina tayi dafe da qirji dan tasan sadear sosai tana janta ajiki idan taje gurin mamanta ,addua tayi mata hawaye na zubawa aunty shahida lokacin da take tuna moment dinsu da yarinya babu abinda yafi daga mata hankali kamar maganar da tace zasuyi a yau din gashi ta mutu batare da san ko akan me zata mata magana ba kwarai  taso tasan ko akan meye , Allah sarki rayuwa  kenan ta dade zaune tana jimamin mutuwar sadear   kafin daga baya ta mike ta shiga dakinta ta kwanta zuciya da gangar jikinta na mata ciwo    .."

Har  yansanda  suka karasa office dinsu  kuka hadiza take , aka  nufi d'akin  bincike daita aka nuna mata gurin zama sannan  bayan kamar awa daya wasu qararrun 'yan sanda suka shigo nan suka fara Aiko mata da tambayoyi d'aya daga cikinsu tace  "ko zamu iya sanin dalilin da yasa kika kashe  makwafciyarki sadear ? hadiza taji tambayar tamkar saukar aradu
take idanun  sukayo waje  tare da dafe qirjinta "wallahi  bani na kasheta ba nima tashi nayi naji labarin mutuwarta ,"karki wahalar da hukuma zai fiyye miki sauki ki fito ki fada mana gskiya kunyi fad'a da sadear ko ba haka ? cikin tsananin firgici da tsinkewar zuciya tattare da tsoro ta  gyada Kai  alamun "Eh!"can km  ta girgiza musu  Kai alamun "a'a!   police ta gyada Kai sannan ta cigaba "kenan kina nufin babu wata matsala ko fada wacce tasa kukayi sa'insa daita ? nan ma ta gyada Kai alamun babu cikin kankanin lokaci ta fita haiyacinta saboda  tambayoyin  da suka dinga mata tana  kare  kanta   a karshe daya daga cikin police mace tace ' kinyi furucin zaki kasheta Kuma kinyi nasara ko ba haka ba ?ta girgiza kanta alamun a'a juyin duniya akayi da hadiza amman  ta tsaya akan ba itace ta kashe sadear ba  suka  barta tare da turata  wani d'aki tana shiga taji an rufeta da duka cikin kankanin lokaci kamanin   hadiza ya sauya tayi laushi  sosai tana ihu tana Komai aka shiga daita wani daki aka garkame . tayi kuka sosai idan ka ganta sai ta baka tausayi gabadaya ta tabbatarwa kanta tata takare Ina ma batayi fad'a da sadear ba ,a she da me kararen kwana tayi fada ? wayyo Allah ni hadiza kaicona me ya kaini fada da gawa  ....?yau dai ga Inda karshen wahalana ya kawoni ni hadiza nayi nadama   ,nayi danasani ban bar yara ba ,ban bar  manya ba ,ban bar matan aure ba, ban bar tsofafi  ba , ga dai karshena ban san me gobe zata haifar ba  ta karasa maganar tana matso ruwan hawaye mai zafi daga idanunta ."

Mmn sudais

💗💗💗💗💗💗
   MAR'ADAMS
   💖💖💖💖
💗💗💗💗💗💗
Book one
Free page

*AYSHA A BAGUDO*

WATTPAD @HAUESH
Arewabooks username
Ayshabagudo
bismillahirrahmanirrahim

Wannan  littafin  na kudi ne mai bukatar karantashi   byn na kammalashi zai  biya 1000 ta wannan  account number din 1438775094 Aishat abdullahi access idan an tura sai a tura 09136918331 alert domin tabbatar da an tura  domin sauraron littafaina a tuntubi chaneel dina  (Hausa bakwai ) a YouTube.

Page5

" da  misalin karfe   tara  na daren ranar Juma'a mr ATA ya fito daga bathroom jikinsa sanye da  rigar wanka iya gwiwarsa yayinda hannunsa  d'aya ke rike da white towel yana goge kanshi  zuwa  wuyansa ,ahankali ya  qarasa  gaban mirrow ya tsaya  yana kallon  kyakkyawar  fuskarsa  yana qoqarin zare  rigar jikinsa ."shiru yayi yana kallon faffad'an qirjinsa dake  kwance da  laulausan suma tamkar na jariri sabuwar  haihuwa ga Kan nipple's dinsa a tsaye makale da  qirjinsa sai sheki suke, babu lafiyayyar macen da zata gansa a haka bataji sha'awarta ta motsa ba  saboda kyawun cikar halittar da allah yayi masa ."

kusan minti goma ya dauka tsaye  yana qarewa kansa kallo kafin  daga bisani ya juya  a natse ya koma  bathroom ." ko  cikakken  second  uku bai yi ba ya fito  ya  d'auki  kwalbar bodyspry ya feshe ilahirin  jikinsa ya saka white singlet boxer's sannan ya shirya cikin wasu hadaddun kananan kaya t shirt fari sol da dogon  wando  baki , ya kai hannu inda tsadadden   Turarensa  (Reed ) yake ya d'auka ya feshe kayan jikinsa , ta  koina a sansar jikinsa kamshi yake tashi mai sanyi da tada tsumin shaawa."  ya ajiye kwalbar turaren a mazauninsa yasa  hannun ya kwashe wayoyin  business  dinsa guda biyu ya juya  ya fito daga cikin dakin tare da janyo  kofa ."

a natse  yake saukowa daga Kan matattakala bene  hannunsa daya soke  cikin aljihun wondonsa  kai  tsaye  yana  gama saukowa ya  qarasa  dining  area ya  zauna akan d'aya daga cikin kujerun  dining yana sauke numfashi kana ya ajiye wayoyinsa akan table ."ahankali sanyin ac dake aiki a parlour'n ya dinga ratsa sansar jikinsa ,lumshe lumtsatsun idanunshi yayi yana ciza gefen lip's dinsa , cikin haka mami ta fito daga kitchen ta soma hidimar  zuba  masa abinci  ,dan shi baya son masu aiki na shiga  huruminsa saboda  Allah yayi shi  mai tsananin tsabta da kyakyami , shiyasa ba koina yake cin abinci ba, ko fuskar abinci ya kalla yaga yayi wani iri to komai za'a yi  bazai ci ba shiyasa duk sanda zai ci wani abu mahaifiyarsa ce kadai ke masa hidima  abinci wannan halin kuwa ya samo ne daga gurin kankansa alhaji abdallah dan shima ba abincin kowa yake ci ba sai wanda yayi masa  ."

bayan ta zuba masa jollof din shikafa yar waje wacce taji pepper chicken  ta hada masa coffee dinsa na gado ta ajiye masa a gabansa sannan  ta koma ta zauna a kujerar dake fuskantarsa tana dubansa a tsanake tace  "kasan wani abu my love ? ta tambayesa idanunta na kanshi ya d'an girgiza mata kansa batare da yace komai ba sai ma lumshe lumtsatsun idanunshi  da yayi yana jiran yaji me zatace .Allah  Allah !!nake  kayi  aure  na huta da yi maka hidima "shiru yayi bai yi magana ba yana jiran yaji spoon din abinci bakinsa amman  yaji shiru har tsawon second goma sai ma maganar aure da yaji ta cigaba dayi masa wanda hakan Ke mugun bata masa rai tare da dagula masa lissafi dan a halin yanzu idan akwai abinda yafi tsana bai wuce maganar auren da take bukatar yayi ba gashi burinta ba abu bane dake cikin lissafinsa ."
Chapter 12 · 0% Book details